Sashe 198
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin yamutsa fuska Esha ɗin tace "Momy, am i not a Good Girl?" da sauri Fanan ɗin ta kai hannu tana shafa kumatunta tace "Oh no, Sweetheart you are a Good Girl, kawai dai in kina haƙuri da abubuwa shine zaki ƙara zama yarinyan kirki ki rinƙa jan Friends ɗin ki a jiki da yan'uwanki kuyi wasa ba tare da kunyi faɗa ba amman yanzu kowa bai jin daɗin yin wasa dake saboda yawan faɗan ki, We are not happy yadda kowa ke maganan baki ji pls ki bari yadda za'a rinƙa cewa Esha Good Girl ce tana da haƙuri da kirki" kai Esha ɗin ta ɗaga mata tace to zata rinƙa yin haƙurin, Fanan ta tambayi ta yi promise ta bari da sauri ta ɗaga mata kai alamar eh tace yauwa haka take so amman in ta ƙara ji ta bugi wani har tayi mashi rauni itama zata 6ata da ita, da sauri Esha ɗin ta girgiza mata kai tace Allah bazata ƙara ba, kallon Haisam Fanan tayi da duk abun nan bai kallesu ba tayi ɗan murmushi kafin ta maido idonta kan Esha ta kai hannu ta matso da kanta ta raɗa mata ta sauka ta duƙa gabanshi ta bashi haƙuri da sauri ta ɗaga mata kai don sosae ta damu da fushin da yayi da ita, saukkowa tayi a ɗarare ta matsa saitin shi tayi kneel down cikin karyayyar murya ta furta "i'm Sorry Daddy, i won't do it again i promise you" shiru bai ce komai ba bai kuma kalleta ba har lokacin fuskar shi a ɗaure take, cikin mutuwar jiki Esha ɗin ta juya ta kalli Fanan tana ta6e baki da kai tayi mata alamun ta ƙara matsawa kusa dashi ta bashi haƙurin, sanin tunda suke dashi bai ta6a bugunsu ba yasa bata ji tsoron matsawa dab dashi ba ta ƙara maimaita haƙurin data bashi sai lokacin ya maido idanun shi kanta ganin haka yasa ta marairaice mashi fuska tana dan motsa baki, ganin baice komai ba yasa ta kalli Fanan ta ƙara yi mata alamun ta kama hannun shi ta bashi haƙurin, hannunta har ɗan rawa yake ta kai ta ɗan kama hannun Haisam guda ganin bai janye ba yasa ta kai ɗayan ta kama duka hannuwan shi tace "pls My Daddy, am Sorry..." tana faɗin haka su Twins suka haɗa baki suka ce please Dad Sorry, hannu Fanan ta kai ta dafa kafaɗarshi tace "Sorry Babe, please forgive her, tayi alƙawarin bazata ƙara ba" Sigh yay cikin muryarshi mai cike da natsuwa idanun shi akan Esha ɗin yace mata kada ta ƙara aikata abu irin haka in ba haka ba zai ɗauki mataki akan ta kuma ba ruwanshi da ita, da sauri ta jinjina mashi kai ya saki fuska tare da ɗago da ita aikuwa da sauri ta faɗa jikin shi tana murmushin farinciki haka su Twins ma murmushin suke harda yi masu gwalo Fanan ma dariyar take ta furta "Esha, Daddy's pet", harda Fanan aka zauna yin Assignment ɗin abun gwanin burgewa, Washe gari Haisam ɗinne ya kai su Makarantar yayi shigar zuwa aiki yana sanye cikin suit, har class ɗinsu yaje yasa aka kira mashi yarinyar data buga ya bata haƙuri itama Esha yasa ta bata haƙurin yace ma Esha daga yanzu su abokai ne su rinƙa yin wasa tare kada ya ƙara jin tayi faɗa da wani tace mashi to, harda kyautar kuɗi masu yawa yaba class Aunty ɗinsu kafin ya tafi, ba laifi a lokacin ta rage rashin jin saidai ance wai mai hali baya barin halin shi koda ya barin wani lokacin bata cikin sauƙi ba.
Cikin sa'a Mino ta kammala karatunta na nursing saida Fatuu taji ba daɗi zata koma Abuja ta barta sauƙinta ma Aysha na nan lokacin itama Aysha ajinta shidda suna gabda yin jarabawar gama Makaranta, bayan result ɗin Mino ya fito wanda yayi kyau sosae ta fara shirin fara yin bautar ƙasa, a wani Weekend da Haisam zaije Zaria ne ya tafi tare da abokinshi Na'eem yayi mashi rakiya daga nan shima zai gaido danginshi don ɗan Zaria ɗinne amman iyayenshi a Abuja suke zaune, bayan sallar Juma'a suka iso Zaria lokacin da suka isa gidan Fatuu bata dawo daga makaranta ba sai Aysha kawai da mai aikinsu, tana sanye cikin riga da skirt na atampa ta zama budurwa sak irin jikin Mino gareta itama doguwa ce kuma bata da jiki gashi tana da kyawun Fuska saidai bata kama dasu Fatuu sosae kamar yadda Mino ke kama da ita, ita ta tarbesu cikin fara'a tana masu sannu da zuwa gaba ɗayansu fuskokinsu a sake suna mata murmushi suka amsa mata, a parlor suka zauna ta kawo masu ruwa da lemu tace bari ta shirya masu table Haisam yace ta bari ba yanzu zasu ci abincin ba sun ci a Kaduna sai ko zuwa ɗan anjima tace to, har zata tafi taji ya tambayi ya karatunta ta tsaya tana murmushi ta amsa mashi da Alhamdulillah suna ta shirin yin jarabawa yay mata fatan sa'a haka ma Na'eem daketa kallonta yana murmushi shima yay mata fatan sa'a ta kalleshi tay mashi godiya kafin ta juya ta tafi, bayan tafiyarta ne Na'eem ya maida idonshi kan Haisam yace mashi amma daga ganin wannan sister ɗin Madam ce ko ya ɗaga mashi kai, tambayar shi yay zuwa tayi Haisam din ya bashi amsa da anan take wurinta tana tayata zama itama tana karatu, jinjina kai Na'eem ya ɗan yi yay shiru can kuma sai yace mashi zasu bashi ita don ya ganta kuma tayi mashi,
"Ita kuma wife en naka fa?" Haisam ya tambaya yana murmushi shima Na'eem din murmushin yake yace zai ƙara ne kamar yadda shima yake da biyu, murmushi kawai Haisam yay bai ce komai ba ganin haka yasa Na'eem yace shi yake saurare Haisam ya tambayi wai is he serious ya ɗaga mashi kai yace Allah tayi mashi da gaske yaji yana sonta da aure, murmushin gefe Haisam yay yace mashi ai ƙarama ce yanzu zata gama Secondary Na'eem din yace ai abun ba'a nan yake ba tunda dai ta balaga lafiya lou za'a iya yi mata aure tunda ta isa, shiru ya ɗan yi kafin ya gyaɗa kai yace in da gaske yake sai ya nemi soyayyar yarinyar Na'eem ɗin ya gyaɗa kai ya tambayi sunanta ya faɗi mashi, anan falo suka zauna suna kallo har akayi sallar La'asar suka tafi Masallaci, bayan dawowarsu Haisam yace suje ciki ya huta yace a'a yana son zai yi magana da Aysha Haisam yace Ok shi zai shiga ciki Na'eem ɗin yace Ok pls ya turo mashi ita, a saman doguwar kujera ya zauna bada daɗewa ba sai ga Ayshar ta fito ta nufo cikin falon, daga gabanshi ta tsaya tana murmushi shima shi yake mata tace gata Yaya Haisam yace yana kiranta yace mata eh tare da nuna mata gefen shi yace tazo ta zauna, saida tayi ɗan jim kafin ta nufi inda ya nuna matan ta zauna daga can ƙarshe ya gyara zaman shi ya dawo yana kallonta,
"Aysha ya School?" ya tambaya da muryarshi ta yan gayu, tanata murmushi tace mashi lafiya lou ya sake tambayar tana dai maida hankali ko tace mashi eh ya tambayi wane department take tace mashi Science,
"Ko kema kina son zama Doctor ne?" kai ta ɗaga mashi alamar eh yace ashe da future Doctor yake zaune tayi yar dariya,
"To za'a rinƙa duba ni in an zama Doctor en?" kai ta ɗaga mashi kafin cikin yar muryarta tace in yana so yay yar dariya yace in mutum bashi da lafiya har sai yana so likita zai duba shi murmushi tayi bata ce komai ba, ta lura da irin kallon da yake mata hakan yasa ta fara yin wasa da yatsunta tana yi tana ɗan kallonshi tana murmushi,
"Yanzu in kiga gama karatun zaki aure ne sai kici gaba da karatun ko?" da sauri ta kalleshi tare da ɗan waro ido tace "Aure kuma!" kai ya ɗaga mata ta ɗan girgiza mashi nata tace ba aure zata yi ba Karatun zata cigaba,
"Why bazaki aure ba, ai ana karatu koda aure ba kiga sister en ki ba itama tana da aure harda yara ma kuma tana karatunta",
"To ai ni ko Saurayi ban dashi" ta faɗa tana ta murmushi, wani kallo yayi mata yace wasa dai take mashi amman kamar ita ya za'ai tace bata da saurayi, da sauri tace "Allah da gaske nake maka ni ko ance ana sona ban yarda saboda Karatu nike son yi" yadda take mashi magana sosae yake burgeshi gashi daga yanayin Maganarta zaka gane yarintar ta,
"Yanzu ace ki samu wanda yake son ki kuma kema kina son shi bazaki yarda kuyi auren ba sai kici gaba da karatun?" da alamun rashin fahimta tace "wa?" yace mata misali ne ya bata tay ɗan shiru alamar tunani yana ta kallonta can tana murmushi tace to in su Adda Fatuu sun amince sai tayi,
"Ai ba su zasu zauna maki ba ko Aysha, in kina so nasan bazasu hana kiyi auren ba" kai ta ɗaga mashi alamar eh yace in ta samu wanda take son kenan zata yi auren ta sake ɗaga mashi kai kafin ta sunnar da kanta alamar kunya,
"Ok, dama wani ne ya ganki kin yi mashi yaji yana son auren ki da Kin gama School, to har nayi ma Yayan ki Haisam Maganar yace ya nemi amincewar ki shiyasa nace to bari in maki magana" ba shiri ta ɗago tana kallon shi da alamun mamaki har ya gama ta waro idanunta tubarkalla tace mashi "ni kuma!" kai ya ɗaga mata ta sake cewa "a ina ya sanni"? Yadda tayi ne ya sashi yin yar dariya kafin yace yaga hoton ta ne tay shiru tana kallon shi,
"Aysha baki ce komai ba game da wanda na faɗa maki yana son ki" dan yamutsa fuska tay ta ɗan yarfa hannu alamar bata san mi zata ce ba, ganin ya kafeta da ido yasa tace to ai ita bata san shi ba,
Cikin sa'a Mino ta kammala karatunta na nursing saida Fatuu taji ba daɗi zata koma Abuja ta barta sauƙinta ma Aysha na nan lokacin itama Aysha ajinta shidda suna gabda yin jarabawar gama Makaranta, bayan result ɗin Mino ya fito wanda yayi kyau sosae ta fara shirin fara yin bautar ƙasa, a wani Weekend da Haisam zaije Zaria ne ya tafi tare da abokinshi Na'eem yayi mashi rakiya daga nan shima zai gaido danginshi don ɗan Zaria ɗinne amman iyayenshi a Abuja suke zaune, bayan sallar Juma'a suka iso Zaria lokacin da suka isa gidan Fatuu bata dawo daga makaranta ba sai Aysha kawai da mai aikinsu, tana sanye cikin riga da skirt na atampa ta zama budurwa sak irin jikin Mino gareta itama doguwa ce kuma bata da jiki gashi tana da kyawun Fuska saidai bata kama dasu Fatuu sosae kamar yadda Mino ke kama da ita, ita ta tarbesu cikin fara'a tana masu sannu da zuwa gaba ɗayansu fuskokinsu a sake suna mata murmushi suka amsa mata, a parlor suka zauna ta kawo masu ruwa da lemu tace bari ta shirya masu table Haisam yace ta bari ba yanzu zasu ci abincin ba sun ci a Kaduna sai ko zuwa ɗan anjima tace to, har zata tafi taji ya tambayi ya karatunta ta tsaya tana murmushi ta amsa mashi da Alhamdulillah suna ta shirin yin jarabawa yay mata fatan sa'a haka ma Na'eem daketa kallonta yana murmushi shima yay mata fatan sa'a ta kalleshi tay mashi godiya kafin ta juya ta tafi, bayan tafiyarta ne Na'eem ya maida idonshi kan Haisam yace mashi amma daga ganin wannan sister ɗin Madam ce ko ya ɗaga mashi kai, tambayar shi yay zuwa tayi Haisam din ya bashi amsa da anan take wurinta tana tayata zama itama tana karatu, jinjina kai Na'eem ya ɗan yi yay shiru can kuma sai yace mashi zasu bashi ita don ya ganta kuma tayi mashi,
"Ita kuma wife en naka fa?" Haisam ya tambaya yana murmushi shima Na'eem din murmushin yake yace zai ƙara ne kamar yadda shima yake da biyu, murmushi kawai Haisam yay bai ce komai ba ganin haka yasa Na'eem yace shi yake saurare Haisam ya tambayi wai is he serious ya ɗaga mashi kai yace Allah tayi mashi da gaske yaji yana sonta da aure, murmushin gefe Haisam yay yace mashi ai ƙarama ce yanzu zata gama Secondary Na'eem din yace ai abun ba'a nan yake ba tunda dai ta balaga lafiya lou za'a iya yi mata aure tunda ta isa, shiru ya ɗan yi kafin ya gyaɗa kai yace in da gaske yake sai ya nemi soyayyar yarinyar Na'eem ɗin ya gyaɗa kai ya tambayi sunanta ya faɗi mashi, anan falo suka zauna suna kallo har akayi sallar La'asar suka tafi Masallaci, bayan dawowarsu Haisam yace suje ciki ya huta yace a'a yana son zai yi magana da Aysha Haisam yace Ok shi zai shiga ciki Na'eem ɗin yace Ok pls ya turo mashi ita, a saman doguwar kujera ya zauna bada daɗewa ba sai ga Ayshar ta fito ta nufo cikin falon, daga gabanshi ta tsaya tana murmushi shima shi yake mata tace gata Yaya Haisam yace yana kiranta yace mata eh tare da nuna mata gefen shi yace tazo ta zauna, saida tayi ɗan jim kafin ta nufi inda ya nuna matan ta zauna daga can ƙarshe ya gyara zaman shi ya dawo yana kallonta,
"Aysha ya School?" ya tambaya da muryarshi ta yan gayu, tanata murmushi tace mashi lafiya lou ya sake tambayar tana dai maida hankali ko tace mashi eh ya tambayi wane department take tace mashi Science,
"Ko kema kina son zama Doctor ne?" kai ta ɗaga mashi alamar eh yace ashe da future Doctor yake zaune tayi yar dariya,
"To za'a rinƙa duba ni in an zama Doctor en?" kai ta ɗaga mashi kafin cikin yar muryarta tace in yana so yay yar dariya yace in mutum bashi da lafiya har sai yana so likita zai duba shi murmushi tayi bata ce komai ba, ta lura da irin kallon da yake mata hakan yasa ta fara yin wasa da yatsunta tana yi tana ɗan kallonshi tana murmushi,
"Yanzu in kiga gama karatun zaki aure ne sai kici gaba da karatun ko?" da sauri ta kalleshi tare da ɗan waro ido tace "Aure kuma!" kai ya ɗaga mata ta ɗan girgiza mashi nata tace ba aure zata yi ba Karatun zata cigaba,
"Why bazaki aure ba, ai ana karatu koda aure ba kiga sister en ki ba itama tana da aure harda yara ma kuma tana karatunta",
"To ai ni ko Saurayi ban dashi" ta faɗa tana ta murmushi, wani kallo yayi mata yace wasa dai take mashi amman kamar ita ya za'ai tace bata da saurayi, da sauri tace "Allah da gaske nake maka ni ko ance ana sona ban yarda saboda Karatu nike son yi" yadda take mashi magana sosae yake burgeshi gashi daga yanayin Maganarta zaka gane yarintar ta,
"Yanzu ace ki samu wanda yake son ki kuma kema kina son shi bazaki yarda kuyi auren ba sai kici gaba da karatun?" da alamun rashin fahimta tace "wa?" yace mata misali ne ya bata tay ɗan shiru alamar tunani yana ta kallonta can tana murmushi tace to in su Adda Fatuu sun amince sai tayi,
"Ai ba su zasu zauna maki ba ko Aysha, in kina so nasan bazasu hana kiyi auren ba" kai ta ɗaga mashi alamar eh yace in ta samu wanda take son kenan zata yi auren ta sake ɗaga mashi kai kafin ta sunnar da kanta alamar kunya,
"Ok, dama wani ne ya ganki kin yi mashi yaji yana son auren ki da Kin gama School, to har nayi ma Yayan ki Haisam Maganar yace ya nemi amincewar ki shiyasa nace to bari in maki magana" ba shiri ta ɗago tana kallon shi da alamun mamaki har ya gama ta waro idanunta tubarkalla tace mashi "ni kuma!" kai ya ɗaga mata ta sake cewa "a ina ya sanni"? Yadda tayi ne ya sashi yin yar dariya kafin yace yaga hoton ta ne tay shiru tana kallon shi,
"Aysha baki ce komai ba game da wanda na faɗa maki yana son ki" dan yamutsa fuska tay ta ɗan yarfa hannu alamar bata san mi zata ce ba, ganin ya kafeta da ido yasa tace to ai ita bata san shi ba,