← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 211 OF 211

Sashe 211

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"An yi maki hakan ne?" Haisam daya ɗago yana kallonta ya furta, da alamun rashin fahimta tace to ita akan mi za'a kaita wurin likitan kwakwalwa, yana murmushi yace saboda da tana kamarta itama tana buƙatar hakan amman ba'a kaita ba to don haka itama ba sai an kaita ba zata bari ne kuma in ma tana tunanin tana da matsalar kwakwalwa to ita tata matsalar da tana yarinya ta linka tata tunda ita Esha har yanzu bata fasa ma wani glass ɗin Mota ba, waro ido Fatuu tay jin abunda yace ta bishi da kallon mamaki bakinta a ɗan buɗe shi kuma sai murmushi yake, da alamun mamaki ta furta "kana son kace nayi hauka lokacin?" ɗan ƙanƙance ido yay cike da tsokana ya furta kusan hakane, ƙara zaro ido tay ya shiga yi mata faffaɗan murmushi can ta miƙe a fusace ta nufe shi, lokacin data tashi har saida alƙalamina ya kusa su6ucewa ganin irin haɗaɗɗar rigar baccin dake jikinta gaba ɗaya ta fito da dirinta na babbar mace yar 30s tana tafiya ko ina na jikinta na amsawa abun saidai ace tubarkalla, tana zuwa gaba ɗaya ta faɗa jikinshi har saida yay ɗan sautin zafi batai wata wata ba ta hau bugunshi saidai bugun yafi kama da a kirashi dana soyayya, haƙuri ya fara bata yanata dariya har haƙuranshi sun bayyana cike da shagwa6a data riga ta zame mata jiki ta shiga faɗin Allah bata yin haƙurin tunda ya kirata da mahaukaciya yana ta dariya yace shifa bai ce mata haka ba itace ta kira kanta da haka, cigaba da bugun nashi tayi tana faɗin ai haka yake nufi ko yace to tayi haƙuri taga ƙopa a buɗe take amman taƙi bari aikuwa ya nuna mata ƙarfi ya burkice da ita ta yadda ko ƙwaƙkwaran motsi bata iya yi, ɗaure mata fuska yay yace tunda abun yar haka ce ya bata haƙuri taƙi to shima ya warware yarjejeniyar dake tsakaninsu ta glass, tana ɗan nishin nauyi tayi murmushi tace ai yanzu ba wannan yarjejeniyar tunda tayi abunda yace a lokacin, fuskarshi a daure yace shi ba ruwan shi sai ta biya shi, ɗage mashi gira tayi tace in don dai miliyan goma yanzun nan zata biya shi ya ɗaga ta, girgiza mata kai yay yace ba kuɗi yake so ba ta kanne mashi ido tace to mi yake so, ce mata yay yara zata haifa mashi yawan hakan yanzu tayi biyar saura biyar kuma a lokaci ɗaya yake son ta haiho mashi yan biyar, bata san lokacin data ƙyalƙyace da dariya ba tace kawai yace mata ya gaji da ita so yake ta mutu in ba haka ba taya zata haifi yara har biyar, still fuskar shi a ɗaure take yace ai ana haihuwan har ma fin hakan tana dariya tace ta sani amman ita dai bata iyawa yayi haƙuri yace bazai yi ba sai ta ƙara mashi yara biyar lokaci guda, lumshe mashi ido tay tace yafi ƙarfin hakan a wurinta don haka indai ya bata yara biyar ɗin to zatayi ƙoƙari ta haifa mashi, jin abunda tace yasashi sakin murmushi itama shi take mashi ya mirgina gefenta suka shiga bin juna da wani irin azababben kallo mai cike da tsagwaron ƙauna can Fatun ta saki yar ajiyar zuciya ta fara magana,

"Thank you Hubby, Thank you for your support and guidance. You didn't just change my life, you became a part of it and loved me unconditionally. You have shown me what true is.Thank you for choosing me to be your life partner. You are truly my best friend and my soulmate, and I couldn't imagine my life without you. Thank you from the bottom of my heart for everything that you have done for me......"

( Nagode Hubby, Nagode da taimakon ka da jagorancinka a gare ni, ba wai kawai ka canza rayuwata ba, ka zama wani bangare a cikinta kuma ka so ni so mara iyaka, ka nuna man mene ne soyayya ta gaskiya. Na gode da za6ata a matsayin abokiyar rayuwarka. Haƙika kai ne babban abokina kuma abokin ruhina sannan bana iya tunanin rayuwa ba
tare da kai ba, Ina mai matuƙar godiya a gareka daga can ƙasan zuciyata akan duk abin da ka yi min....." muryarta ce ta karye hawaye suka shiga gangaro mata, matsar da fuskarshi yay saitin tata ya shiga kissing hawayen kafin can ƙasan maƙoshi yace shima yana godiya a gareta sosae data saka shi yake jin yafi kowane namiji sa'ar mata a duniya, haɗe fuskokinsu yay inhaling each others breathe, ganin yana ƙoƙarin hade lips ɗinsu da sauri ta ankarar dashi ƙopa a buɗe take hakan ya sashi dakatawa, saukkowa yay don yaje ya rufe a lokacin nima naga ya dace na bar masu cikin ɗakin.

*Alhamdulillah!* *Alhamdulillah!!* *Alhamdulillah!!!💃💃💃💃💃💃💃*

*A nan na kawo karshen littafin A Sanadin Makwabtaka wanda na ɗau lokaci ina rubutawa😍*

_Dukkan godiya da yabo sun tabbata ga Allah subhanahu wata'ala, the Most Compassionate, the Most Omnipotent and the Most Omniscient da ya bani ikon kammalawa cikin ƙoshin lpy kamar yadda na fara, to him be all the glory🙏, tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta Annabi muhammad(S.A.W) da Ahalinsa da Sahabbansa baki ɗaya😍, Darussan dake ciki Allah ubangiji yasa mu amfana dasu🙏 ya sadar da ladan gareni da mahaifana da zuri'ata, yan'uwana da malamai na, kura kuren ciki ina roƙon Allah ubangiji ya yafe man Alfamar Annabin rahama (S.A.W)🙏_

_Gaisuwar ban girma ga Mahaifiyata Hajiya Rabi'atu Yahaya, she is my first luv and my everything💘,Allah ya ja da rai ya ƙara maki lafiya my sweetheart😘, My beloved Siblings💞waɗanda littafin nan Sadaukarwa ne a garesu, Nafisat, Aisha, Khadija, Maimunatu, Hafsat, Abdul'azeez, Fatima, Maryam, Ameenatu, I luv you so so much, kune ni, in baku bani, I really appreaciate ur Encouragement💪,prayers and all-round support👍, Allah ya kara haɗa kawunanmu ya jiƙan Mahaifinmu, Ameen_

_Gratitude To my Sweetheart😍, who is ever glad at every inch of my progress, I really appreaciate ur Support, Encouragement and prayers, Allah ya bar mu tare ya ƙara daukaka, Amin_.

_Special thanks to My lovely Sis Hafsat Bature Writer Of Abban Sojoji and Kurkukun Ƙaddara na gode da ƙarfafa man Gwuiwa Allah ya baki ikon Kammala naki cikin ƙoshin Lafiya yasa ya amfani al'umma Amin, Abubakar Sadeeq AlQuramy, Uncle Isma'il ina matuƙar godiya a gareku da taimakon da kuka bani Allah ya ƙara taimakon ku a dukkan Al'amuran rayuwar ku🙏, My P.A Munah Bature sannu da ƙokari Allah ya ƙara ma rayuwar ki Albarka ya kawo miji nagari Amin, ina matuƙar godiya agareki😘_

*To My Novel's Fans*

*Ina matuƙar godiya a gareku musamman waɗanda suka saka kuɗin su suka sayi littafin nan ina roƙon Allah ya ƙara arzuƙi yasa ku amfana da littafin, Members Of Comment Section na gode da ƙaunarku da uzurinku a gareni kamar su, Asma'u sani, Asma'u Kebbi, Bajatu, Bahillot, Dr Hamida Gandi, Mrs Mu'utassim, Sofix, Minat Sgy, Shafa Adill, Zeefakhad Collecion, MaryamSalisu, Rababs222, Angel love, A'isha Abdurrahman, Fadeelamande, Queen, Shafar Dauran, Aunty wasee, Amina Sulaiman, Habibty, Aunty Hadiza, Aunty Sa'adatu, Salma Nijar, Fatima Fannami, Hauwaabubakar, First Lady, Maman Amir, Ummulkhairi Nijar, Satheyer, Maman Naeem, Deejarh da sauran waɗanda bansamu na lissafo sunayensu ba, ina sane daku, ina matuƙar godiya a gareku ur comment means a lot to me, bansan da wane kalmomi zanyi amfani wurin gode maku ba, sai dae ince Allah ya barmu tare don ku ɗin kun wuce fans kun zama yan'uwa agareni,*

*Ina Gwanar wata ga tawa💃😍 Jinjina a gareki Hajiya Kubrah (Momy) Mace mai irin halin Hajiyar Sanata, Allah ya ƙaro mana irin ku acikin al'umma, har bansan da wane irin kalmomi zanyi godiya a gareki ba sai dai kawai ince Allah ya ƙara girma da ɗaukaka ya raya maki zuriya ya ƙara danƙon kauna keda Oga yasa afi haka ya kuma sa a gama da Duniyar nan lafiya, ya bar mana zumunci daga nan har Aljanna, Amin ya Hayyu ya Ƙayyum🙏*

*Ban mance da irin gudunmawar da kika bani ba Miss Walida Ɗanwaire Fulanin Yola ina matuƙar Godiya a gareki Allah ya barki da Oga ya raya Baby Maryam, Maman Afra kema ban mance da irin taki gudunmawar ba ina miƙo godiya lodi lodi Allah ya raya zuri'a ya bar ƙauna keda Oga, ya jiƙan Habiba (Ummy), Amin ya Rabbi, haka ban mance da taki gudunmawar ba wato Nabila Yar Gata Fulanin Daura kema Allah ya bar ƙauna keda Oga ya baku zuriya ɗayyiba*

*Allah Ya bar mana zumunci daga nan har Gidan Aljanna, Allah Yabiya maku dukkan buƙatunku, Allah ya baku ikon Yin amfani da darussan dake acikin Labarin nan, Ina matuƙar godiya Da irin haƙurin da kuka yi da kuma uzirin da kukayi mun har Allah ya bani Ikon Kammala Littafin nan, Yanzu gashi komai Ya wuce no more kiran ayi man uzuri, lols😂*

*Littafin nan Ya ƙunshi darussa daban daban Na rayuwa,Ya ilmantar,Ya faɗakar,Ya kuma nishaɗantar, Manyan darussan cikin shi sune Muhimmacin Haƙuri da kuma Taimako wanda gaba ɗaya labarin ya ginu ne akan hakan💃💃💃*

*Taku Mai ƙaunarku da zuciya ɗaya, ZAINAB BATURE (Zee Laluh/Oum Imam).*

*Ga mai buƙatar wannan littafin Complete tun daga na ɗaya har zuwa na ukku sai ya tuntu6i ɗaya daga cikin waɗannan lambobin wayar, 09013804524 ko 08169856268.

  
Chapter 211 · 0% Book details