Sashe 208
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Kwance tashi cikin Fanan ɗin har ya fito kuma bata wani laulayi sosae don har ta koma aiki, lokacin da cikin ya kai wata takwas ne aka tabbatar da in aka bari ta haihu da kanta zata iya samun matsala don haka aka yanke yi mata Cs in ya kai wata tara, Hajiya Maryam na jin haka tace zata fitar da ita waje kawai ta haihu a can amman Fanan ɗin taƙi amincewa tace ko taje can duk abu ɗaya ne don anyi mata bayanin matsalar da ake hasashe ta kuma gamsu da hakan don saida aka yi mata duk binciken daya dace kafin a tabbatar kuma likitan da yayi mata binciken ƙwararre ne kuma shima da a ƙasar wajen yake aiki wato likitansu mai aiki Germany dole Hajiya Maryam ta ƙyale ta, bayan cikin ya shiga wata na tara kafin zuwa ranar da za'ayi su Fatuu duk cikin zullumi suke duk da Fanan ɗin lafiyarta lou, ana gobe za'ayi aikin ranar ta kama lahadi amman Fatuu bata iya ta koma Zaria ba, gaba ɗaya duk sun shiga damuwa suna ta Addu'oi a ranar kusan raba dare Fatuu da Haisam sukai suna nafilfilin roƙon Allah yasa ayi aikin lafiya itama Fanan ɗin ta yi ma kanta Addu'oin, har su twins Fatuu ta tada sukai Nafila suma sukai mata Addu'a, Washe gari Monday su Esha ƙin zuwa Makaranta sukai saboda aikin da za'ayi ma Mommynsu, misalin ƙarfe goma na safe aka shiga da ita aikin Fatuu harda ƙwallarta haka su Esha sauran yan'uwa ma duk suna a asibitin anata fatan nasara, Hajiya Maryam dai har bata iya magana saboda fargaba sai Addu'o'i take a cikin ranta, bayan an shiga da ita a Office ɗin Doctor ɗin wanda yake mai girma ne akwae kuma kujeru suka zazzauna kowa yayi jigum, bayan kamar minti arba'in da biyar da shiga aikin Doctor Taj wanda shine likitansu na Germany kuma shine yayi aikin ya shigo cikin office ɗin ai suna ganinshi duk suka mimmiƙe kusan gaba ɗaya suka haɗa baki wurin tambayarshi yadda ake ciki yana murmushi yace anyi aikin cikin nasara an fiddo mata da Baby Boy, zo kaga murna Haisam da Fatuu da Hajiya Maryam a tare suka duƙa sukai sujjada su Esha na ganin sun yi suma duk suka yi haka ma Farha da Jidderh, tura baki Esha tayi bayan ta gama yin sujjadar tace miyasa Momy ta haiho Baby Boy ita Baby Girl take so ta samu ƙanwa duk akai dariya akace tayi haƙuri in zata ƙara haihuwa in sha Allah zata haiho mata Baby Girl ɗin, Aunty ce ta kawo masu Babyn wanda ina gani na furta Ma sha Allah saboda tsananin kyaun shi sak Haisam ya biyo hakan yasa yay kama da yan biyun Fatuu sosae, sam bakunansu sun kasa rufuwa sai faman kar6a kar6ar Babyn ake, a ɗaki na musamman dake Amenity aka kwantar da Fanan din duk yan uwa sun cika shi itama Fanan ɗin idonta biyu tana amsa ya jiki da barkar da ake mata fuskarta ɗauke da murmushi, zuwa yamma duk yan'uwan da abokan arzuƙi anata zuwa dubata sai yaba Babyn ake, wuraren ƙarfe biyar Dad ɗinsu Haisam yazo tare da muƙarrabanshi suka dubata tare da yi ma Baby addu'a, kwananta biyu a Asibitin kafin aka sallameta suka koma gida, a ranar da suka koma da daddare lokacin su Esha sunyi bacci Fatuu ma ta koma part ɗinta sai Fanan ɗin tare da Iya babyn kuma na kwance cikin net yana bacci Haisam ya shigo jikinshi sanye da jallabiya, bayan sun gaisa da Iya ta miƙe don ta basu wuri, murmushi suka shiga sakar ma juna ya tambayi ya jikinta tace da sauki sosae ya jinjina kai kafin yace Allah ya ƙara mata lafiya ta amsa da Amin tay mashi godiya, juyawa yay yana kallon babyn ta cikin net ganin haka tace ko ta fiddo mashi shi ya girgiza mata kai alamar a'a, kallonta yay ya tambayi wane suna take son a saka mashi ne tace ai tayi zaton ma ya riga ya saka mashi suna ya ɗan girgiza mata kai kafin yace ya bari a sallameta sai ta za6ar mashi sunan da take so, shiru ta ɗanyi tana murmushi can tace mashi sunanshi take son a saka mashi wato Haisam, ɗan buɗa ido yay yana murmushi yace yayi tunanin zata saka mashi sunan Dad ɗinta ne tay shiru kafin tace "nafi son a saka mashi sunan ka Babe" ɗage mata gira yay ya tambayi saboda mi,
"Saboda ni a wurina sunan yafi kowane suna muhimmaci kuma shine sunan da ya cancanta a saka mashi, kayi man abubuwan alkhairi da yawa Babe, ka aure ni don ka faranta man sannan ka zauna dani tsawon lokaci ba tare dana haihu ba kuma daidai da rana ɗaya baka ta6a nuna man damuwarka ba ko kayi man wulaƙanci kaine ma kake ƙarfafa man gwuiwa kan hakan, kuma nasan ba don Allah ya ƙaddaro aure tsakaninka da Zarah ba na tabbatar zaka iya rayuwa dani a haka ba tare da ka ƙara aure ba kawai don farinciki na, kai na daban ne Babe, I know I can never repay you for everything you have done for me, amman ina son ka sani Babe ina son ka da kowanne bugun zuciyana sannan ina mai godiya a gareka mara iyaka Allah ya bar mu tare har abada, ina roƙon Allah ubangiji ya ƙara inganta rayuwar ka Babe ya dawwamar da kai a cikin farinciki ya saka maka da gidan aljanna maɗaukakiya..." ƙwallan da suka tarun mata a idanu ne suka fara zubowa tasa hannu tana gogewa, matsawa yay gabanta da yake a kishingiɗe take saboda aikin da aka mata ya kai hannu yana goge mata ƙwallan cikin cool voice ɗinshi yace mata ya isa haka shima yana matuƙar alfahari da ita sannan yana farinciki da Allah ya bata lafiya har ta haihu yayi Addu'ar Allah ya raya masu shi da sauran yaransu ta amsa da Amin ya Rabbi.
"Saboda ni a wurina sunan yafi kowane suna muhimmaci kuma shine sunan da ya cancanta a saka mashi, kayi man abubuwan alkhairi da yawa Babe, ka aure ni don ka faranta man sannan ka zauna dani tsawon lokaci ba tare dana haihu ba kuma daidai da rana ɗaya baka ta6a nuna man damuwarka ba ko kayi man wulaƙanci kaine ma kake ƙarfafa man gwuiwa kan hakan, kuma nasan ba don Allah ya ƙaddaro aure tsakaninka da Zarah ba na tabbatar zaka iya rayuwa dani a haka ba tare da ka ƙara aure ba kawai don farinciki na, kai na daban ne Babe, I know I can never repay you for everything you have done for me, amman ina son ka sani Babe ina son ka da kowanne bugun zuciyana sannan ina mai godiya a gareka mara iyaka Allah ya bar mu tare har abada, ina roƙon Allah ubangiji ya ƙara inganta rayuwar ka Babe ya dawwamar da kai a cikin farinciki ya saka maka da gidan aljanna maɗaukakiya..." ƙwallan da suka tarun mata a idanu ne suka fara zubowa tasa hannu tana gogewa, matsawa yay gabanta da yake a kishingiɗe take saboda aikin da aka mata ya kai hannu yana goge mata ƙwallan cikin cool voice ɗinshi yace mata ya isa haka shima yana matuƙar alfahari da ita sannan yana farinciki da Allah ya bata lafiya har ta haihu yayi Addu'ar Allah ya raya masu shi da sauran yaransu ta amsa da Amin ya Rabbi.