Sashe 60
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"Yanzu yaushe yace zai zo Katsina?" ta tambayeta taci serious Fauzy kau mi zatai in ba dariya ba, harara ta wurga mata tace ba tambayarta tay ba, cikin dariya tace "to ni Aunty Mareeya bansan mi zan ce maki ba sai kace baki fahimci bayanin dana yi maki ba, ni fa bai ce yana sona ba bai kuma nuna ko alamar hakan ba kece kike ganin haka, ba har na fad'i maki shawarar da ya bani dana bashi labarin abunda Mujaheed yay man ba" d'an jimm tay tana nazarin Maganar can ta sauke ajiyar zuciya tace "na fahimci komai, amman kinsan mi, ina tunanin yana son ki ba tare daya sani ba don mutum irin wannan hakanan bai iya sake maki haka gaskiya, in ma ace yana da kirki zai iya biyan ki wayar taki gaskiya bana tunanin da irin wannan tsadaddiyar duk gadai wayoyi iri iri nan cike da gari sai kawai ya siyo maki wannan don ya fasa maki glass d'in waya, ai kawae yar gidan Hajiya komar ki ta kamo mana gingimemen kifi wllh, Allah Ubangiji ka tabbatar mana da abun nan wllh har bansan irin farincikin da zan yi ba" ta k'arasa tana ta washe baki ita dai Fauzy murmushi kawai take can tace "to Aunty koda ace sona d'in yake ni ba sai in yayi man ba...." Tunkan ta gama Maganar ta kai hannu zata buge ta tana fad'in "Wllh yayi maki mak'aryaciya kawai, wannan d'in zaki ce wani bai maki ba, ke ko bai maki ba indai ya nuna yana son ki Allah kema sai kin so shi tunda ni yayi man, yanzu irin wannan yaushe ma ake jira sai sunce suna so ai da mutum ya samu dama yake cusa kan shi in da rabo sai kiga an dace haka kema ya kamata ki yi" tura baki tay tace Allah ita bazata wani cusa kanta a wurin shi ba hakanan ya wulakanta ta,
"Ai dama ba ina nufin kice kina son shi ba, tunda kinga kin samu dama ke zaki rink'a yin abubuwan da zaki jawo hankalin shi gare ki har ya furta yana son ki" shiru Fauzy tay tana jinjina zancen wai Sameer ya bud'e baki ya ce yana son ta tirkashi, tambayarta tay ai tana da lambar shi ko tace mata eh d'azun daya kirata, tace Yauwa to yanzu ta kira shi tay mashi godiya, d'an waro ido Fauzy tay tace amman fa dare yayi sosae ta bari sai gobe mana, harararta tay tace da zafi zafi ake bugun k'arfe ai sai yaga ma bata yaba ba tunda yasan dole a daren zata bud'e ta gani su fa ta irin haka ake janyo hankalin su, ba yadda Fauzy ta iya haka ta fara k'ok'arin kiran nashi Aunty Mareeyar sai kwatanta mata yadda zatai mashi godiyar take ita kuwa gabanta sai d'an fad'uwa yake, kiran ya shiga yana ta ringing amman bai d'aga ba har ya yanke, cire wayar tay tace mata ta sake kira k'ilan bai kusa da wayar yanzu kuma tunda yaji ringing d'inta zai taho don ya d'auka, yamutsa fuska Fauzy tay tace ita gaskiya bazata sake kira ba hakanan ta ja ma kanta wulakanci sufa irin su ba'a zak'e masu don ba'a cika yi masu gwaninta ba, jinjina kai Aunty tay alamar yarda da Maganarta tace Shikenan suje, Fauzyn ta tambaye ta yanzu ya zatai da wayar ita bata son a gani gaskiya tace mata to ta 6oye ta in suka koma gida sai taci gaba da amfani da abunta ta d'aga mata kai, suna niyyar juyawa su shiga wayar Fauzy ta fara ringing da sauri gaba d'ayan su suka kai idanun su kan screen d'in, ganin lamba yasa Aunty Mareeya ce mata waye idon Fauzy a d'an ware tace mata shine,
"Yauwa to, ki d'auka sai kice dama kinga wayar ne shine kika kira ki yi mashi godiya, kar kiyi mashi magana kaman wata sakarai kiyi exactly yadda na kwatanta maki d'azun" Aunty Mareeya da tay k'asa k'asa da murya ta fad'a har saida tasata dariya, picking kiran tay ta kai wayar kunne sai had'iyar miyau take Aunty na mata nuni da ta natsu da hannu, shiru yay bayan ta d'auka cikin kwantar da murya tay sallama nan ma shiru bai amsa ba, d'ago ido tay ta kallo Aunty da ta gwale ido tana kallon ta, alamun miye tay mata da hannu Fauzyn ta girgiza mata kai tay mata alamar bai yi magana ba, yi mata alamar taci gaba da magana kawai tay ta d'aga mata kai, a nutse tace mashi dama ta ga wayar ne shine ta kira tayi mashi godiya, tana rufe baki taji yace "You ave done that already" abu ta had'iya cikin yar in ina tace "eh, dama naga wayar babba ce shiyasa nace bari in k'ara yin godiyar, Allah ya saka da Alkhairi ya k'ara bud'i na Alkhairi" d'an shiru yay daga baya ya furta "Ameen" shiru sukai Fauzy sai kikkafta idanu take Aunty Mareeya tay mata k'uri sai tsuma take, can bayan wani lokaci taji ya furta "Gud nyt" da sauri tace mashi haka itama, tana ciro wayar Aunty Mareeya ta kai hannu kan kafad'unta ta jawota jikinta cikin washe baki tace haka yakamata tace "Gud nyt Masoyi na" yadda ta mak'e muryar ne yasa Fauzy kyalkyacewa da dariya itama dariyar farinciki take suka nufi ciki, lokacin da suka shiga cikin parlon ba kowa duk sun tashi an kashe kayan kallon, sakin kafad'ar Fauzyn tay cikin washe baki tace "ranki ya dad'e kije ki kwanta" dariya Fauzy ta saki tana fad'in kai Aunty Mareeya, sai da Safe tay mata tana washe baki tace "to your excellency Allah ya tashe mu lafiya" sosae Fauzy ke dariya ta juya ta tafi itama Aunty Mareeyar dariyar take ta nufi d'akin su, bayan Fauzy ta shiga bakin gado ta nufa ta zauna ta kai hannu cikin jakar ta fiddo kwalin wayar, bin shi tat da kallo can ta d'aura a saman cinyoyinta ta bud'e, bin wayar tay da kallo cikin ranta tana k'ara yin mamakin ta, Maganganun Aunty Mareeya ta shiga tunanowa na Sameer son ta yake, acikin ranta ta shiga mamakin taya hakan zata kasance wanda tasan tabbas dole yana da yan mata kuma bama k'ananu ba kamar ta, sannan y'ay'an Mayan masu kud'i da Mulki, zuciyarta ce ta tambaye ta yanzu in da gaske son nata yake zata so shi? jimm tay ta kasa amsa ma kanta don gaba d'aya ita gani take ba abu bane mai yuwuwa ma hakan yasa ta kauda ma tunanin gaba d'aya, d'aukar wayar tay ta fara jujjuya ta tana k'are mata kallo da d'an murmushi akan fuskar ta, aje wayar tay ta kai hannu ta tallabo ha6arta ta shiga tunano duk maganganun da sukai dashi a Mota, sosae tay mamakin yadda ya sake mata har sukai magana haka sai faman sakin murmushi take can ta maida wayar acikin kwalin ta saka cikin jakar ta mik'e, wurin kayanta ta nufa bayan ta bud'e akwatinta ta saka, ko tunanin ta saka kayan bacci bata yi ba ta wuce gado ta haye, rufe ido tay nan take zuciyarta ta shiga dawo mata da suffar Sameer.
"Ai dama ba ina nufin kice kina son shi ba, tunda kinga kin samu dama ke zaki rink'a yin abubuwan da zaki jawo hankalin shi gare ki har ya furta yana son ki" shiru Fauzy tay tana jinjina zancen wai Sameer ya bud'e baki ya ce yana son ta tirkashi, tambayarta tay ai tana da lambar shi ko tace mata eh d'azun daya kirata, tace Yauwa to yanzu ta kira shi tay mashi godiya, d'an waro ido Fauzy tay tace amman fa dare yayi sosae ta bari sai gobe mana, harararta tay tace da zafi zafi ake bugun k'arfe ai sai yaga ma bata yaba ba tunda yasan dole a daren zata bud'e ta gani su fa ta irin haka ake janyo hankalin su, ba yadda Fauzy ta iya haka ta fara k'ok'arin kiran nashi Aunty Mareeyar sai kwatanta mata yadda zatai mashi godiyar take ita kuwa gabanta sai d'an fad'uwa yake, kiran ya shiga yana ta ringing amman bai d'aga ba har ya yanke, cire wayar tay tace mata ta sake kira k'ilan bai kusa da wayar yanzu kuma tunda yaji ringing d'inta zai taho don ya d'auka, yamutsa fuska Fauzy tay tace ita gaskiya bazata sake kira ba hakanan ta ja ma kanta wulakanci sufa irin su ba'a zak'e masu don ba'a cika yi masu gwaninta ba, jinjina kai Aunty tay alamar yarda da Maganarta tace Shikenan suje, Fauzyn ta tambaye ta yanzu ya zatai da wayar ita bata son a gani gaskiya tace mata to ta 6oye ta in suka koma gida sai taci gaba da amfani da abunta ta d'aga mata kai, suna niyyar juyawa su shiga wayar Fauzy ta fara ringing da sauri gaba d'ayan su suka kai idanun su kan screen d'in, ganin lamba yasa Aunty Mareeya ce mata waye idon Fauzy a d'an ware tace mata shine,
"Yauwa to, ki d'auka sai kice dama kinga wayar ne shine kika kira ki yi mashi godiya, kar kiyi mashi magana kaman wata sakarai kiyi exactly yadda na kwatanta maki d'azun" Aunty Mareeya da tay k'asa k'asa da murya ta fad'a har saida tasata dariya, picking kiran tay ta kai wayar kunne sai had'iyar miyau take Aunty na mata nuni da ta natsu da hannu, shiru yay bayan ta d'auka cikin kwantar da murya tay sallama nan ma shiru bai amsa ba, d'ago ido tay ta kallo Aunty da ta gwale ido tana kallon ta, alamun miye tay mata da hannu Fauzyn ta girgiza mata kai tay mata alamar bai yi magana ba, yi mata alamar taci gaba da magana kawai tay ta d'aga mata kai, a nutse tace mashi dama ta ga wayar ne shine ta kira tayi mashi godiya, tana rufe baki taji yace "You ave done that already" abu ta had'iya cikin yar in ina tace "eh, dama naga wayar babba ce shiyasa nace bari in k'ara yin godiyar, Allah ya saka da Alkhairi ya k'ara bud'i na Alkhairi" d'an shiru yay daga baya ya furta "Ameen" shiru sukai Fauzy sai kikkafta idanu take Aunty Mareeya tay mata k'uri sai tsuma take, can bayan wani lokaci taji ya furta "Gud nyt" da sauri tace mashi haka itama, tana ciro wayar Aunty Mareeya ta kai hannu kan kafad'unta ta jawota jikinta cikin washe baki tace haka yakamata tace "Gud nyt Masoyi na" yadda ta mak'e muryar ne yasa Fauzy kyalkyacewa da dariya itama dariyar farinciki take suka nufi ciki, lokacin da suka shiga cikin parlon ba kowa duk sun tashi an kashe kayan kallon, sakin kafad'ar Fauzyn tay cikin washe baki tace "ranki ya dad'e kije ki kwanta" dariya Fauzy ta saki tana fad'in kai Aunty Mareeya, sai da Safe tay mata tana washe baki tace "to your excellency Allah ya tashe mu lafiya" sosae Fauzy ke dariya ta juya ta tafi itama Aunty Mareeyar dariyar take ta nufi d'akin su, bayan Fauzy ta shiga bakin gado ta nufa ta zauna ta kai hannu cikin jakar ta fiddo kwalin wayar, bin shi tat da kallo can ta d'aura a saman cinyoyinta ta bud'e, bin wayar tay da kallo cikin ranta tana k'ara yin mamakin ta, Maganganun Aunty Mareeya ta shiga tunanowa na Sameer son ta yake, acikin ranta ta shiga mamakin taya hakan zata kasance wanda tasan tabbas dole yana da yan mata kuma bama k'ananu ba kamar ta, sannan y'ay'an Mayan masu kud'i da Mulki, zuciyarta ce ta tambaye ta yanzu in da gaske son nata yake zata so shi? jimm tay ta kasa amsa ma kanta don gaba d'aya ita gani take ba abu bane mai yuwuwa ma hakan yasa ta kauda ma tunanin gaba d'aya, d'aukar wayar tay ta fara jujjuya ta tana k'are mata kallo da d'an murmushi akan fuskar ta, aje wayar tay ta kai hannu ta tallabo ha6arta ta shiga tunano duk maganganun da sukai dashi a Mota, sosae tay mamakin yadda ya sake mata har sukai magana haka sai faman sakin murmushi take can ta maida wayar acikin kwalin ta saka cikin jakar ta mik'e, wurin kayanta ta nufa bayan ta bud'e akwatinta ta saka, ko tunanin ta saka kayan bacci bata yi ba ta wuce gado ta haye, rufe ido tay nan take zuciyarta ta shiga dawo mata da suffar Sameer.