← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 127 OF 211

Sashe 127

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Zaune yake a cikin parlon part d'in shi dake a cikin gidan su, dama gidan nasu Family House ne gaba d'aya shi da matar shi Rukky iyayen su anan suke dama Cousin ne shi da ita, gaba d'aya ya canza kamar ba Mujaheed d'an gayu ba yanzu sam ba wannan gayun don tun bayan daya yi aure kwanciyar hankali tayi mashi k'aranci, tashin farko matsalar daya fara fuskanta da Rukky itace bai sameta a budurwa ba bayan da suka yi auren haka dai aka yi Amarcin aka gama ba tare daya nuna mata komai ba don ita a zaton ta bai gane ba Saboda gyaran da ta sha, matsala ta biyu daya k'ara fuskanta itace k'azama ce sam bata san ta gyara muhallin da suke ciki ba ta dai iya tayi wanka tayi kwalliya amman kullum gida kaca kaca gashi sam bata iya wani girki ba, matsala ta ukku daya fuskanta a tare da ita itace sam bata bashi lokaci yadda yakamata Saboda aikin Asibiti da take dama da suka yi karatu a Malaysia ita medicine ta karanta shi kuma Business admin, a daddafe auren su yayi shekara guda don matsalolin daya ke fuskanta a tattare da ita sunyi yawa gashi har lokacin ko 6atan wata bata ta6a yi ba, Babbar Matsalar daya fuskanta a tare da ita wadda ta kusa zauta shi itace kamata da yayi red-handed tana aikata lesbian a cikin gidan shi, a lokacin yayi kuka kamar kamar me ita kanta hankalinta ya tashi sosae ta dingi bashi hak'uri tana ta tuba bazata k'ara ba amman ina dama ya gaji da auren ta hakan yasa ya tunkari iyayen su ya zayyana masu irin matsalolin da yake fuskanta a tare da ita k'arshe har lesbian daya kamata tana yi bai 6oye masu ba, suma hankalin su ya mugun tashi bama kamar Mahaifiyar shi anan tace ma Daddyn shi gaskiya a raba su amman ga mamakin su sai cewa yayi baza ayi hakan ba tunda dai abun duk na gida ne in abun ya bud'u to suma zai shafe su k'imar gidan ce zata ta6u a bari su kirata sai suyi mata fad'a insha Allahu zata bari, wani k'ululun bakin ciki ne ya tokare Mujaheed yana kuka ya shiga rok'on mahaifin nashi kan shidai a raba su kawai ya shiga girgiza mashi kai yana fad'in baza'ayi haka ba ai ba had'a su akai ba su suka fara son juna har sukai aure don haka kawai yayi hak'uri ayi mata fad'an, a lokacin Mujaheed ji yayi kamar ya mutu, bayan an kirawo ta sosae mahaifin nasu yayi mata fad'a ya nuna ta bashi mamaki yana ganinta mai hankali mai ilimi wanda a addinance da kuma a aikinta na likitanci duk tasan illolin hakan taya zata 6ata wayonta haka, sosae take kuka tana fad'in ayi hak'uri sharrin shaid'an ne amman ta bari in sha Allah zata gyara duk wasu matsalolinta da Mujaheed ya fad'a, sam Mahaifiyar shi bata so hakan ba amman ba yadda zata yi tunda Mahaifin nasu ya kafe, a haka suka ci gaba da rayuwa ba laifi a lokacin ta d'an gyara saidai sam shi hakan bai burge shi ba don ta riga ta fitar mashi a rai gaba d'aya sai lokacin ne ya gane dalilin da yasa ya sameta a ba budurwa ba ya shiga tunanin Allah kad'ai yasan tsawon lokacin da ta d'auka tana aikata hakan ashe shiyasa sam bata damu da ta bashi hakkin shi ba saboda tana bin mata yan'uwanta, yasan Rukkyn ta waye sosae amman bai ta6a tunanin zata aikata haka ba, a lokacin ne son Fauzy ya taso shi a gaba kullum cikin aikin tunanin ta yake haka cikin baccin shi yayi ta mafarkin ta saidai shi kan shi yasan samunta a lokacin abu ne mai matuk'ar wahalar gaske don yasan mahaifinta ba laifi yana da zafi hakan yasa bai ma yi tunanin zuwa gidan su ba, da yaga abun yayi mashi yawa ne ya yanke ya fara tuntu6arta in ta saurare shi sai yayi duk yadda zai yi yaga ya shawo kanta watak'il a bashi ita, Da wani yammaci ne ya shirya cikin Motar shi ya nufi gidan su Fauzy lokacin daya je a d'an nesa da gidan ya parker yana ta kallon kopar gidan yana dakon fitowar wani saida aka d'auki lokaci sannan yaga wani k'aninta da suke ce ma Abba ya dawo daga islamiyya a saman Keke yana ginin shi ya fito da sauri ya fara kiran sunan shi hakan yasa Abban tsayawa ya juyo Mujaheed d'in ya nufe shi ai koda yay arba da fuskar shi kawai sai gani yay ya tamke mashi fuska hakan yasa Mujaheed shan jinin jikin shi amman duk da hakan ya dake yana d'an murmushi yayi mashi sallama tare da ce mashi an dawo daga islamiyya ne kaman bazai amsa ba can dai cikin d'aure fuska yace mashi eh, jinjina mashi kai yayi yace yayi kyau Allah ya bada sa'a anan Abban bai amsa mashi ba sai ma ce mashi yay zai shiga gida da sauri Mujaheed ya dakatar da shi cikin yar in ina yace "a...m Fauziyya na nan?" Wani kallo mai kamar harara yayi mashi kafin yace bata nan, tambayar shi yay tana ina cikin kumbura baki yace "Oho ban sani ba nima" yana fad'in hakan ya ja keken shi ya shige, tsaye Mujaheed Yay sototo hakan da yayi mashi ba K'aramin k'aryar mashi da zuciya yay ba don bai zata yaron zai mashi hakan ba Saboda lokacin da yana tare da Fauzy suna shiri sosae da yaron don mutumina ma Mujaheed d'in ke ce mashi, da k'yar yaja k'afafun shi ya koma cikin Mota a ranshi ya shiga tunanin yaro ma yayi mashi hakan to ina ga Mahaifin kuma Fauzyn, jiki a mace ya ja Mota ya fara kokarin barin layin, yana driving yana tuna rayuwar shi da Fauzy a ranshi yana raya yasan da ita ya aura da ba K'aramin more mata zai yi ba don yarinyar na bala'en son shi kuma duk yadda yake so haka zai tafiyar da ita, haka ya dingi tuna abubuwa har ta kai yana kai ma steering Motar d'an bugu alamun takaici, tunanin yadda zai ga Fauzy ya shiga yi don tun kafin ya taho saida yayi trying layinta bai shiga, yana haka abokin shi Usman ya fad'o mashi a rai yay tunanin watak'il shi zai san inda take da sauri ya d'auki wayar shi ya kira shi bayan ya d'aga sun gaisa ne ya tambayi yana ina yace mashi gashi nan gidan shi yana shirin zuwa Masallaci yace Ok bari yazo, a tare suka tafi Masallacin bayan an gama sallar suka dawo ganin ya tsaya a bakin Motar shi Usman d'in yace mashi su shiga mana ya girgiza mashi kai, shiru yay yana kallon Mujaheed d'in don duk matsalolin da yake ciki ya sani,

"Kayi hakuri ka daina saka damuwa haka sosae a ranka Mujaheed kada ka ja ma kan ka wata matsalar kuma, ka dage da Addu'a Allah kad'ai ne zai maka maganin matsalar da kake ciki" shiru yay kafin ya jinjina mashi kai tare da kai hannu ya shafi gaban kan shi can yace "Usman bazaka gane ba amman ina cikin matsala wllh" ya k'arasa tare da cize lip d'in shi na k'asa,
Chapter 127 · 0% Book details