← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 211

Sashe 87

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Aerospace...Kaman ana nufin aeroplane ko?" ta tambaya tare da d'age baki, still da murmushi akan Fuskar shi yace "Yeah Kusan haka, shi engineer ne yana aiki da wani company a K'asar U.k, suna k'era jirgin sama ne bama shi kad'ai ba da wasu abu da suka danganci sama kaman satellites and rocket" zaro ido Fatuu tay a d'an rud'e ta furta "rocket kuma! ba itace mai kaman katuwar bindiga ba da in aka harba bullet d'inta ke fita kaman bomb ya tafi shuuuu yaje ya tarwatsa wuri??" dariya ta bashi yadda ta zaro idon yace mata eh shi wannan missile kenan shima rocket d'in ne, "Yanzu su ke had'a su?" Kai ya jinjina mata alamar eh kafin yace amman shi Sameer yafi experience sosae ta bangaren had'a jirgi don ya k'ware a kan haka shiyasa har wasu companies suna gayyatar shi aiki kaman a France da Germany, har nan US akwai wani Company da yake zuwa aiki a Washington, a nan Nigeria ma yana aiki da Ministry of aviation shiyasa akwai lokacin da yake d'an zama a Nigeria amman yafi zama a UK" jinjina kai ta shiga yi jin irin aikin da Sameer d'in yake can ta furta amman dai tasan yana samun kudi Haisam d'in yay yar dariya yace mata sosae,

"To amman kai ma kana samun kud'i kaman shi" wani kallo yay mata ta waro ido da sauri tace itafa hakanan ta tambaya tunda taga shima a K'asar wajen yake aiki, kawai sai gani tay yay d'an murmushi yace "tunda ina aiki ai dole in samu kud'i ko kawai kice kina son ki ji ni da shi waya fi samun kudi right?" Ya d'age mata gira ta d'an tura baki had'i da girgiza kai, sigh yay yace "kowa da kalar aikin shi so dole salary ya bambanta amman ta wani bangaren Kusan duk damar mu d'aya ne da shi kuma aikin namu suna da alak'a tunda duk sun danganci technology ne don akwae abubuwan da company d'in mu ke yi wanda suke amfanin da shi and nima kuma ina zuwa wasu Wuraren aiki saidai shi ya riga ni fara aiki abroad Saboda ni farko dana gama first degree na anan nayi aiki shi kuma tun daga School Company d'in suka zo suka d'auke shi nima tun lokacin an so a d'auke ni amman Dad ya hana don yana jin haushin yadda duk suke d'auke Mutanen mu masu hazaka a cewar shi hakan ne ya hana tamu K'asar cigaba kuma hakan ne, bayan naje yin Master's degree d'ina nan suka matsa na fara yi masu aiki amman dana gama sai Dad yace in dawo gida nan zan yi aiki lokacin sai na nuna masa interest dina kan yin aiki da su Saboda ina son bud'e Company shine ya amince amman sai na fara aikin anan, a lokacin nayi missing Hajiya sosae don tunda na tafi Karatu na bar wurinta haka dana dawo na fara aiki a Abuja sai dai in kawo mata ziyara har na sake komawa degree na biyu a lokacin tana kewa na sosae duk da bata fad'a man amman na sani duk na kawo mata ziyara in zan tafi sai naga idanunta sun canza ga kuma rashin mijinta da a lokacin yana damunta sosae wannan dalilin ne yasa na buk'aci canza wurin aiki nazo in zauna tare da ita......." dakatawa yay yana numfashi a hankali idon shi akan Fatuu da itama nata idanun na acikin nashi,

"........ashe zaman nawa wani babban Alkhairi ne zai same ni na had'uwa dake Baby, tunda kika shigo rayuwata farinciki na ya k'aru and I couldn't remember in akwae wani rana da nayi bakin ciki Saboda ke in ma akwae shi kenan, ban ta6a shiga damuwa ba sosae kaman ranar da zamu rabu zan yi aure, tun lokacin dana fahimci kin canja man na fara shiga damuwa har zuwa ranar, sosae kikai breaking heart d'ina har yanzu ina ganin image d'in wannan moment na ga Zarah a duk'e tana kuka sosae Saboda Ya Handsome d'inta gashi ni kuma ba abunda zan iya yi mata kan hakan, idanuwa na sun cika da tears a lokacin wanda bazan tuna when last naji hakan ba, koda muka shiga jirgi saidai kawae na d'age kai na na runtse ido ba komai nike ba sai tunanin halin dana baro ki a haka har muka isa Abuja...." Murmushi kawai Fatuu ke yi yayin da zuciyarta ta shiga tariyo hoton rabuwar tasu a airport, a lokacin wani irin soyuwa zuciyarta ke yi gaba daya ji tay kaman rayuwarta tazo k'arshe she felt empty, rayuwa kenan yanzu gashi komai ya zamo tarihi a gare ta duk sanadiyyar hak'uri da tawakalli,

"Ranar da kika sanar man zaki abortion naji tashin hankali amman bai kai na ranar da kika fad'i ba a wurin Dinner party, that was the second day dana shiga tsananin tashin hankali a rayuwa ta, daga ranar dana rasa grandpa dina mijin Hajiya lokacin ina a Secondary school sai kuma wannan ranar ganin Zarah kwance a jikina bata numfashi , zuciyata tayi ta sak'a man abubuwa....." Labarin irin halin daya shiga lokacin da zasu kaita Asibiti harda kukan daya yi ya shiga bata yana ta murmushi har ya gama ta hau girgiza kai har saida taji idanunta sun ciko da k'walla wata irin k'aunar shi take ji na ratsa mata jinin jikinta, Sigh yay ya kalleta da murmushi yace daga bayanin aikin shi da yayi mata ta fahimci abunda take son sani na wanda yafi samun kud'i tsakanin shi da Sameer, yamutsa fuska ta shiga yi a shagwabe tace itafa wllh hakanan ta tambaya ba don wani abu ba kawae subul da baka ne,

"ai dama kin cancanci kisan komai game da aikin mijin ki ko" ya fad'a yana murmushi, d'age mashi gira tay tace "to in haka ne ka fad'i man nawa ne salary en ka" tana rufe baki yay mata wani kallo mai kaman harara ta saka dariya tace to ba shi yace ta cancanci tasan komai ba,

"Wannan sirri ne banda shi" ya fad'a yana yar dariya itama har lokacin Dariyar take tace mashi ita bata yarda ba sai ya fad'i mata ai shi yace, ce mata yay to zai fad'i mata amman a kunne zai rad'a mata don kar aji, har saida ta d'an Jujjuya kafin ta tsaida idonta akan shi tace to ba su kad'ai bane, hannu ya mik'a ya nuna mata cikinta yace Baby yake nufi kada ya fad'a mata ya ji wata rana in ya buk'aci ya siyo mashi/mata abu yace baida kud'i ace mashi yana dasu tunda an ji salary d'in shi daya fad'i ma Mom, dariya sosae Fatuu ke 6a66akawa tace to ita bai gudun tayi mashi hakan sai Baby yace ai ita ya gane tausayinshi take ji bata son yana kashe kud'i amman yasan k'ilan in ya fad'i mata ta daina jin tausayin nashi da sauri ta d'aga hannu tace to Allah bata son jin salary d'in tay Maganar tana dariya tare da girgiza kai shima still dariyar yake, bayan sun tsagaita gaba d'aya jingina sukai da jikin kujerar suna kallon juna kowannansu wani irin nishadi yake ji duk ya kasance da d'an uwan shi,

"Na dawo daga tafiya kin hana ni in huta da tambayoyin ki" ya fad'a bayan yayi yar hamma, jin haka yasa ta sauke k'afafunta daga saman jikinshi da sauri ta fara k'ok'arin mik'ewa tana fad'in yayi hak'uri to ya tashi suje su kwanta, nuna mata bowl data sha fruit salad yay yace ta kai Kitchen bari ya kashe kayan kallon tace to, lokacin data dawo cikin parlon har ya kashe kayan kallon yana ganinta ya mik'e tsaye ta nufo shi tana murmushi, tana zuwa gaban shi kawae sai ta juya mashi bayan ta d'an rankwafa tace wai ya hau ta goya shi tunda shi bai iya goya ta Saboda ciki, dariya sosae ta bashi aikuwa tana a yadda take taji ya sunkuce ta gaba d'aya ta saka dariya, nufar hanyar Bedroom yay yana d'auke da ita ta sak'alo hannuwanta a wuyan shi tace wai bai jin nauyinta Slowly ya furta ai dama gaba d'ayan su nauyin su na a kan shi don haka bai jin shi, suna zuwa bakin kopar d'akin yasa k'afa ya tura ya shige da ita.........

_Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268

91

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

............Washe gari Asabar Misalin k'arfe sha d'aya na safe Mom na kwance ta koma bacci bayan sun yi Breakfast, tana cikin baccin ta jiyo ringing d'in wayarta kamar bazata tashi ba da k'yar dai ta bud'e idanun ta ta kai hannu gabanta ta d'aukko wayar, duba screen d'in tay taga wanda ya kira har saida tay d'an yi murmushi ganin yar uwarta ce wato Hajiya Zainab, picking tay ta kara wayar a kunne, gaisawa sukai da juna jin yanayin muryar Mom d'in yasa tace yar gayu bacci ma take ko ta tasheta, Mom na murmushi tace gayu ai sai ita kawai ta koma bacci ne Hajiya Zainab na murmushi tace to ai saida hutu ake iya komawa baccin,

"Hhhh in wannan hutun ne ai kowa ma nada shi kema nasan baki so kwanciyar bane",

"Uhmm wani lokacin kam ai ko kaso ba dama ka koma Saboda schedules" Mom na murmushi tace ya za'ai sai Addu'a Allah ya k'ara d'aukaka ya kuma taimaka tace Amin,

"Sai kika ji Saraki ya samu Mata" shiru Mom tayi tana maimaita sunan Saraki da ta fad'a, da alamun rashin fahimta tace "mi kike son fad'i man, ba dai his Excellency ne zai aure ba?" Dariya Hajiya Zainab ta saki tace "inaaa, ai Excellency ya gama yin aure a gidan duniyar nan ya auru yadda ya kamata, Saraki wanda yay gadon Sarautar Grandpa nike nufi" shiru tay tana nazarin Maganar da tayi can tace "wai Son kike nufi?"
Chapter 87 · 0% Book details