← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 46 OF 211

Sashe 46

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

daga su sai wasu had'add'un royal sofas da aka jera suma suna kallon gaban hall an jera k'ananun table d'in kujerun a gaban su a nan Hajiya Zainab take da yaran ta daga gefe kuma Mom ce da wasu matan manya harda matar Speaker house of rep da wasu matan ministoci, daga can d'ayan side d'in nan hamshaki Sameer yake a hakimce dasu Salim da Najeeb da wasu Abokan su yayan masu fad'a a ji duk ankon mazan ne a jikin su kuma gaba d'aya d'inki iri d'aya, sauran cikin hall d'in anyi seat arrangements na kujeru masu round an zagaye su da kujeru guda hud'u kowanne table an kuma nad'e su da covers kalar da suka hau da decoration d'in bangon hall d'in a kowanne table an d'aura flower mai kyau, iya dai hall d'in ka gani kasan ba k'ananun kud'i ya ci ba, bayan su Laila sun shigo wurin yan mata taje ta za6o wasu ta wuce wurin dasu Aunty Mareeya suke tace ma Fanan ta taso a shigo da ita tace to itama tana sanye da ankon anyi mata fitted gown wuyanta sanye da yar ziririyar sark'ar diamond da barima harda d'an hannu tayi kyau ba k'arya, Su Yadikko ma da gwaggo duk suna zaune sun sha anko Yaya ma na sanye da k'uri adakan leshin ta mai kaman bambalasta, Abbas ma wurin su Najeeb yaje ya sanar dasu su taso a shigo dasu Haisam, saida Laila ta je wurin masu Dj ta sanar dasu wak'ar da zasu saka sannan ta yi ma babban MC magana kan shigowar, bada jimawa ba MC ya sanar da shigowar su aka saki wakar Aure Martaba gaba d'aya hall d'in ya d'auka, su Haisam d'inne a tsakiya yana ruk'e da hannun Fatuu na dama Fanan na ruk'e da na hagu daga bayan su su Jidderh ne a 6angare d'aya sai su Abbas a d'ayan bangaren hamshak'i Sameer dai dama bai taso ba, suna shigowa ciki aka saki wata k'ara mai kaman jiniya, saida aka raka su saman kafin suka dawo cikin hall d'in, sakin dry ice smoke akai gaban hall d'in ya turnuk'e da hayak'i ya shiga fita yana bada k'ayataccen design kowa kaga fuskar shi d'auke take da murmushi, bayan duk an natsu Mc yay welcoming kowa da bayanin dalilin daya sa sukai gathering a wurin, agenda ta farko Abbas aka kira yazo yayi jawabin maraba, bayan ya fito cikin harshen turanci bayan yayi Addu'a yay ma kowa sannu da zuwa da dalilin taruwar su k'arshe yay ma ma'auratan fatan Alkhairi yayi godiya ga mahalarta taron musamman manyan iyayen su, bayan ya gama Mc ya fad'i next abunda za'ai wanda takaitaccen tarihin Ango za'a bada ya ambaci sunan Sameer matsayin wanda aka sa zai bada tarihin, yana a Hakimce akan kujera ya d'aura k'afa d'aya akan d'aya kai kace ba sunan shi aka kira ba duk wanda suka san shi idon su na akan shi sai da ya mula bayan Mc ya k'ara kiran sunan sannan ya d'an d'aga hannu yayi mashi alamar ya kawo mashi lasifikan, da yawa basu yi mamakin hakan da yayi ba ciki harda wanda suka ga lokacin da suka zo gidan su Haisam, bayan an Kawo mashi sai da ya d'an d'auki lokaci sannan ya d'an kai ta kusa da bakin shi cikin isa ya fara magana, tsit kake ji kowa shi yake saurare cike da gwanancewa da kwarewa yake bada tarihin da turanci kai kace ba bahaushe bane duk da dai za'a iya cewa ba cikakken bahaushen bane, zuru Fauzy tay tana kallon shi ta can gefen shi da suke zaune duk da gefen fuskar shi kawai take iya gani, sosae yasa jikin wasu tsuma yana gamawa ya janye lasifikan ya d'aurata saman table d'in gaban shi duk da Mc d'in ya taho ya amsa aka shiga tafawa, bayan Mc ya d'auka harda yi mashi godiya bai ko kalle shi ba nan fa wad'anda basu san shi ba suka fara tambayar waye shi, abu na gaba da Mc ya fad'i za'ayi shine bada takaitaccen tarihin Amarya wanda aka kira sunan Fauzy itace zata yi, mik'ewa Fauzy tay duk da ta shirya ma hakan sai da gabanta ya hau fad'uwa, gaban hall d'in ta nufa a d'arare duk kunya ta rufe ta Saboda rashin mayafi don bata saba ba ko Yaya ne in zata je abu irin haka tana saka gyale, wurin Mc d'in taje ya mik'a mata lasifikan bayan ta amsa tana juyowa ta sauke idanunta kan Sameer suka had'a ido wani irin bugu kirjin ta yayi da sauri ta maida idonta ya koma kallon k'asa, a nutse ta fara godiya da yabo ga Allah da neman tsira da aminci ga fiyayyen halitta kafin ta fara bada tarihin Fatuu, sosae tay k'ok'ari wurin yi da turanci ba wata gargada duk da fargabar da take ji, tana gamawa aka shiga tafa mata bayan ta bashi lasifikan ta nufo cikin hall d'in idanunta a k'asa Mc d'in na yaba mata, abu na gaba Amarya aka buk'aci ta bayyana irin farincikin da take ciki da kuma tarihin yadda suka fara soyayya da Angonta har suka yi aure, mik'ewa Fatuu tay gabanta nata d'an fad'uwa ta nufo saukkowa daga saman Mc d'in nata kod'a ta, mik'a mata lasifikan yay ta amsa ta juya ta kalli Mutane, ta saba yin magana a gaban mutane tun a Secondary School hakan yasa bata ji komai ba a nutse cikin sanyin murya ta fara magana, godiya tay ga Allah sannan tayi ga mahalarta taron, tiryan tiryan ta shiga bayyana tun farkon haduwarta da Haisam zuwa dawainiyar da yayi da ita a rayuwa da yadda Allah ya jarabe ta da son shi sakamakon kyautatawar da yake mata da kuma yadda ya zama mijin ta a lokacin da bata ta6a zata ba, gaba d'aya komai a tak'aice take fad'i, juyawa tay ta kalli Haisam ta fara yi mashi godiya akan sadaukarwar da yayi a gare ta wurin ganin ya maida ita mutum, sosae ta shiga yi mashi godiya tana nuna bata da abunda zata iya saka mashi saidai tayi mashi Alk'awarin zama mai biyayya da saka shi Farinciki, Haisam d'in sai kallon ta yake da d'an murmushi wani abun in ta fad'a sai ya lumshe mata ido, bayan ta gama nashi komawa tay kan Fanan farko yabonta ta fara yi tace tunda take a rayuwarta bata ta6a ganin mace irin ta ba, ta had'a komai na rayuwa amman hakan bai sa ta zama mai girman kai ba, ita a wurinta kirkinta har yayi yawa, tunda ta fara ganinta take k'aunarta har ta kai ta amince mata ta zauna da ita a matsayin kishiya ko kuma tace k'anwa Saboda farincikinta, nunawa tayi bata da kalmomin da zata iya yin amfani dasu wurin gode mata sai dai tayi mata Alk'awarin zama tamkar k'anwarta uwa d'aya uba d'aya da yardar Allah bazata zama matsala a gare ta ba saidae silar farincikin ta kuma tana son shaida masu ita da mijin su sune Mutanen da sukai mata kirkin da ba wanda ya ta6a mata irin shi a rayuwa duk da they're on a different level haka suka jata a jikinsu suka nuna mata duk d'aya suke, muryarta ce ta karye dama tuni k'walla sun fara zubo mata, Addu'oi ta shiga yi ma Fanan Mutanen cikin Hall d'in na amsa wa har ta kai kuka yaci k'arfinta kawai sai ta durk'ushe anan ana jiyo sautin kukan nata ta cikin loud speakers, Kusan a tare Fanan da Haisam suka mik'e suka nufota, Haisam ne ya riga saukkowa don da sauri ya nufo ta lokacin da Fanan ta k'araso ya d'ago ta tana zuwa kawae sai ta rungumeta ta saka kuka itama, baiwar Allah koda bata nuna kishi ba wai don bata jin shi bane ita kadae tasan battle d'in da take da zuciyarta kawai bata da mafita ne tasan hakan shi yafi mata Alkhairi,
Chapter 46 · 0% Book details