Sashe 101
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"D...dama akwae abunda nike son tambayar ka ne.....Ina so ka fahimce ni don Allah...." shiru tay tana jiran taji mi zai ce idonta akan shi taji yace yana sauraron ta, ci gaba tayi "dama akan aurena da zaka yi ne, nasan ba wani abu a tsakanin mu sai kawai naji Maganar aure kuma bacin bamu ta6a haka da kai ba...to shine nike son in tambaye ka miyasa zaka Aure ni tunda baka ta6a nuna kana...so na ba" da k'yar ta k'arasa Maganar da in ina tare da d'an nishi duk a lokaci guda, maida idon shi yay ya koma kallon gaban shi ta kafe shi da ido tana son gane yanayin fuskar shi da yake akwae haske sosae a layin ya d'an haska cikin Motar, sun d'an d'auki lokaci kafin taji ya furta "why did you ask me that?" Yay tambayar tare da Kallon ta, abu ta had'iya a Sanyaye tace "kawai hakanan ne inason in sani Saboda nayi mamakin hakan" tana rufe baki yace bata yarda dashi ba kenan da sauri tace "a'a wllh...kawai dai kai ne ka ta6a ce man kar in rink'a bada yarda gaba d'aya to shiyasa nike son in ji dalilin da yasa kake son aure na" kauda idon shi yay daga barin kallon ta sannan ya furta shima bai sani ba hakanan zai aure ta, tsit kake ji wani iri Fauzy take ji a cikin ranta hakan da ya fad'a, kallon ta yay daidai lokacin itama ta d'ago ido ta kalle shi calmly ya ce in tana ganin hakan bai mata ba lokaci bai k'ure ba za'a iya fasawa ai, tun kafin ya rufe baki k'irjinta ya hau bugun uku uku hannunta ya fara d'an rawa, kafeta yay da ido alamar amsarta yake jira ta fara motsa baki da k'yar cikin rashin dad'in rai ta furta "Shikenan, in hakan yayi maka nima yayi man" tana k'arasa Maganar da sauri ta sunkuyar da kanta jin k'walla sun fara tarun mata a cikin idanunta sam ba haka ta so taji daga gare shi ba a ranta ta raya Mujaheed yayi tarayya da ita don tana burgeshi shi k'ilan ma tasan koma burge shi d'in bata yi, kallon shi tay bayan tayi kokarin maida kwallar ta d'an k'ak'alo murmushi tace "Nagode Allah ya saka da Alkhairi Allah kuma ya maida ka lafiya" jinjina mata kai yayi tace mashi saida safe bin ta da ido kawai yay ya d'an yi jimm can ta juya ta kai hannu zata bud'e kopar..,
"I will marry u because....i love you Fauziyyah" kaman saukan aradu haka taji Maganar ta sauka akanta, da sauri ta juyo tana kallon shi idon shi na akanta amman sai ka rantse ba shi yay Maganar ba don Kalmar k'arshe daya furta kalma ce mai matuk'ar tsada a wurin shi in ba Mom d'in shi ba ba wadda ya ta6a fad'i ma hakan duk da uban matan dake rok'on shi kan ya furta masu hakan, d'an murmushi tay ta fara motsa baki cikin yar in ina tace "are you telling the truth?" wani irin lumshe ido yay duk da acikin duhu ne ta gani ta d'an hasken cikin Motar, dad'i ne ya kama Fauzy har bata san lokacin data ce mashi don Allah ba don taji dad'i ya fad'i hakan ba, d'an ta6e baki yay yace dama mutum na auren wanda baya so ne, murmushi kawai Fauzy ke saki tace mashi ta gode in sha Allahu zata zame mashi mata ta gari wadda zata bashi Farin ciki na har abada tana ganin d'an murmushin gefen da yayi, sai faman k'ayataccen murmushi take gaba d'aya dad'i ya cikata don abunda take fata ne ya kasance yana son ta, ce mata yayi taje sai sunyi magana tace to, har zata juya taji yace haka yakamata su rabu dakatawa tayi ta maido idonta kan shi ko da bai fito ya fad'i ba ta gane yadda yake nufin yakamata su yi bankwana, shiru tayi a cikin ranta tana raya gaskiya bai kamata tana biye mashi ba tunda hakan ba kyau kuma in dai tana son ta hana shi hakan dole ta fara ta kan su, cikin yar rawar murya tace "k...kayi hak'uri naga bamu kai ga yin aure bane ina tsoron mu samu zunubi....kuma hakan na iya shafar rayuwar Auren mu don naji anata wa'azi akan hakan" shiru yay still idanun shi na akan ta sai kame kame take can taji yace ta tafi wani iri taji sai taga kaman yayi fushi ne zata so ace tayi mashi abunda zai faranta mashi ba kamar da shima yanzu yay mata abunda ya saka ta farinciki amman tasan hakan shi yafi masu Alkhairi, a sanyaye ta furta mashi "Gud nyt" kai ya d'an jinjina mata kafin yace karta manta da abun baya daga yadda ya furta Maganar bazata iya gane yanayin da yake ciki ba. Lokacin data shiga cikin gidan a parlor ta iske Aunty Mareeya da su Hanif tana yi masu Assignment, da sallama ta shiga suka taso da gudu suna mata oyoyo, amsar ledojin suka yi ta dafa Shoulder d'in iman suka nufi cikin parlon idon Aunty a kan su tana ta washe baki, a kusa da ita ta zauna tace "yan tafiya an dawo?" Fauzyn ta d'aga mata kai,
"Amman wai tun da kuka fitan kuna government House d'in?" Kai ta d'an girgiza mata ta fad'i mata duk inda suka je, tambayar ina Sameer d'in tayi tace ya tafi kafin ta d'aga kai, hannu Aunty ta kai ta d'aukko jakar kwalin da ta ja hankalinta tace miye aciki Fauzy tace bata sani ba First Lady ce ta bata, bud'e ta Aunty tayi ta kai hannu ta fara fiddo abubuwan ciki, turare na guda ukku iya kwalin su abun kallo ne sai miski a yar babbar kwalba mai kyau tun ba'a fiddo turarurrukan daga cikin kwalin su ba har k'amshin su mai dad'i ya karad'e wurin, sosae Aunty ta yaba bayan ta maida su cikin jakar ta tambayi yadda suka kar6eta ta fad'i mata hakan ma taji dad'i sosae harda 6akar Fauzy a kafad'a tana fad'in ta dai zama dangin gwabnoni ita dai yar dariya tayi, tambayarta yadda Fatuu take ta k'ara yi tace halan tana nan tana ta ja tace mata eh, kallon ledojin tayi da yake akwae tambarin wurin da aka siyo kayan ciki tana dariya tace daga ziyarar chilling kenan suka wuce still Fauzy murmushi kawai tayi, fara janyo ledojin tayi su Hanif na Mik'o mata sauran ta shiga bubbud'a su, tarkacen su ice cream ne flavour daban daban dasu yoghurt sai su shawarma da pizza abubuwa dai kala kala kili guda tana cikin dubawa tace "ashe su suriki na ba iya kud'i aka iya badawa ba" tambayar Fauzy tayi cikin wurin suka shiga aka siyo tace a'a ta fad'i mata kawo masu akai tace ai dama ta d'an ji mamakin ace shiga sukai dashi aka siya, Hanif ne ya d'auki ice cream yace ma Aunty ya sha tace na Aunty Excellency ne ya tambayeta Fauzy ta d'an yamutsa fuska tace "kai Aunty don Allah" tana dariya tace tuba take, babbasu komai tayi kowa ya natsu suka fara ci itama ta d'auki shawarma tana ci, kallon Fauzy data jingina da kujera tayi shiru Aunty tayi tace "wai lafiya Fauziyya, na lura kamar akwai abunda ke damun ki tun bayan da kika shigo kin k'i sakin jiki sosae" d'an ta6e baki Fauzy tay ta furta "uhmm" dakatawa Aunty tayi da cin abun da take gaba d'aya ta maida hankalin ta kanta tace mata ya akai ne, ajiyar zuciya tayi ta fara motsa baki kafin ta shiga bata labarin yadda sukai da Sameer na tambayar da tayi mashi kan dalilin daya sa zai aure ta da amsar daya bata har zuwa yadda suka rabu,
"Ni Aunty ina ganin kaman yayi fushi" shiru Aunty ta d'an yi can tayi yar ajiyar zuciya ta dafa Shoulder d'inta tace "ba lalle ba, in dai da gaske yana da ilimin Addini to bazai ji komai ba tunda yasan gaskiya kika fad'i sai ma dai yaji dad'in hakan tunda ya gane wace kalar mata zai aura, kuma fa tana iya yuwuwa ma gwada ki yake kinsan Mutane in suna abunda suka san ba daidai ba to basu son su Auri mace mai hakan don haka karma ki wani damu wllh" kai kawai Fauzy ta jinjina amman ita tasan ba wani gwadata da yayi Saboda abubuwan da yayi mata, daga baya sakin jiki tayi suka cigaba da cin abubuwan anan Aunty ta ce yakamata ta sa yazo yayi breakfast gobe Fauzyn tace anya zai zo don yace gobe zai tafi amman dai zatayi mashi magana. Bayan ta koma d'aki a bakin gado ta zauna ta shiga tunanin ko ta kira shi saidai tana jin d'ar d'ar can dai tay k'arfin halin kiran nashi, har ta yanke bai d'auka ba ta ruk'e wayar tana dakon kiran shi kamar yadda suka saba bada jimawa ba kuwa sai gashi ya kira d'in har saida tayi murmushi taji d'an sanyi a ranta, bayan ya d'auka ya ya koma tayi mashi ya amsa mata daga haka suka yi shiru can taji yace da wani abu tace mashi eh dama Aunty d'in ta ce tace tayi mashi magana yazo da safe don Allah yayi breakfast, ce mata yay bazai samu zuwa ba don Flight d'in safe zai bi tace to tayi mashi saida safe itama yayi mata, bin wayar tayi da kallo tama rasa tunanin da zata yi jikinta ya d'an yi sanyi can dai ta mik'e don tayi shirin kwanciya...........
93
_ASM BY ZAINAB BATURE _
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
"I will marry u because....i love you Fauziyyah" kaman saukan aradu haka taji Maganar ta sauka akanta, da sauri ta juyo tana kallon shi idon shi na akanta amman sai ka rantse ba shi yay Maganar ba don Kalmar k'arshe daya furta kalma ce mai matuk'ar tsada a wurin shi in ba Mom d'in shi ba ba wadda ya ta6a fad'i ma hakan duk da uban matan dake rok'on shi kan ya furta masu hakan, d'an murmushi tay ta fara motsa baki cikin yar in ina tace "are you telling the truth?" wani irin lumshe ido yay duk da acikin duhu ne ta gani ta d'an hasken cikin Motar, dad'i ne ya kama Fauzy har bata san lokacin data ce mashi don Allah ba don taji dad'i ya fad'i hakan ba, d'an ta6e baki yay yace dama mutum na auren wanda baya so ne, murmushi kawai Fauzy ke saki tace mashi ta gode in sha Allahu zata zame mashi mata ta gari wadda zata bashi Farin ciki na har abada tana ganin d'an murmushin gefen da yayi, sai faman k'ayataccen murmushi take gaba d'aya dad'i ya cikata don abunda take fata ne ya kasance yana son ta, ce mata yayi taje sai sunyi magana tace to, har zata juya taji yace haka yakamata su rabu dakatawa tayi ta maido idonta kan shi ko da bai fito ya fad'i ba ta gane yadda yake nufin yakamata su yi bankwana, shiru tayi a cikin ranta tana raya gaskiya bai kamata tana biye mashi ba tunda hakan ba kyau kuma in dai tana son ta hana shi hakan dole ta fara ta kan su, cikin yar rawar murya tace "k...kayi hak'uri naga bamu kai ga yin aure bane ina tsoron mu samu zunubi....kuma hakan na iya shafar rayuwar Auren mu don naji anata wa'azi akan hakan" shiru yay still idanun shi na akan ta sai kame kame take can taji yace ta tafi wani iri taji sai taga kaman yayi fushi ne zata so ace tayi mashi abunda zai faranta mashi ba kamar da shima yanzu yay mata abunda ya saka ta farinciki amman tasan hakan shi yafi masu Alkhairi, a sanyaye ta furta mashi "Gud nyt" kai ya d'an jinjina mata kafin yace karta manta da abun baya daga yadda ya furta Maganar bazata iya gane yanayin da yake ciki ba. Lokacin data shiga cikin gidan a parlor ta iske Aunty Mareeya da su Hanif tana yi masu Assignment, da sallama ta shiga suka taso da gudu suna mata oyoyo, amsar ledojin suka yi ta dafa Shoulder d'in iman suka nufi cikin parlon idon Aunty a kan su tana ta washe baki, a kusa da ita ta zauna tace "yan tafiya an dawo?" Fauzyn ta d'aga mata kai,
"Amman wai tun da kuka fitan kuna government House d'in?" Kai ta d'an girgiza mata ta fad'i mata duk inda suka je, tambayar ina Sameer d'in tayi tace ya tafi kafin ta d'aga kai, hannu Aunty ta kai ta d'aukko jakar kwalin da ta ja hankalinta tace miye aciki Fauzy tace bata sani ba First Lady ce ta bata, bud'e ta Aunty tayi ta kai hannu ta fara fiddo abubuwan ciki, turare na guda ukku iya kwalin su abun kallo ne sai miski a yar babbar kwalba mai kyau tun ba'a fiddo turarurrukan daga cikin kwalin su ba har k'amshin su mai dad'i ya karad'e wurin, sosae Aunty ta yaba bayan ta maida su cikin jakar ta tambayi yadda suka kar6eta ta fad'i mata hakan ma taji dad'i sosae harda 6akar Fauzy a kafad'a tana fad'in ta dai zama dangin gwabnoni ita dai yar dariya tayi, tambayarta yadda Fatuu take ta k'ara yi tace halan tana nan tana ta ja tace mata eh, kallon ledojin tayi da yake akwae tambarin wurin da aka siyo kayan ciki tana dariya tace daga ziyarar chilling kenan suka wuce still Fauzy murmushi kawai tayi, fara janyo ledojin tayi su Hanif na Mik'o mata sauran ta shiga bubbud'a su, tarkacen su ice cream ne flavour daban daban dasu yoghurt sai su shawarma da pizza abubuwa dai kala kala kili guda tana cikin dubawa tace "ashe su suriki na ba iya kud'i aka iya badawa ba" tambayar Fauzy tayi cikin wurin suka shiga aka siyo tace a'a ta fad'i mata kawo masu akai tace ai dama ta d'an ji mamakin ace shiga sukai dashi aka siya, Hanif ne ya d'auki ice cream yace ma Aunty ya sha tace na Aunty Excellency ne ya tambayeta Fauzy ta d'an yamutsa fuska tace "kai Aunty don Allah" tana dariya tace tuba take, babbasu komai tayi kowa ya natsu suka fara ci itama ta d'auki shawarma tana ci, kallon Fauzy data jingina da kujera tayi shiru Aunty tayi tace "wai lafiya Fauziyya, na lura kamar akwai abunda ke damun ki tun bayan da kika shigo kin k'i sakin jiki sosae" d'an ta6e baki Fauzy tay ta furta "uhmm" dakatawa Aunty tayi da cin abun da take gaba d'aya ta maida hankalin ta kanta tace mata ya akai ne, ajiyar zuciya tayi ta fara motsa baki kafin ta shiga bata labarin yadda sukai da Sameer na tambayar da tayi mashi kan dalilin daya sa zai aure ta da amsar daya bata har zuwa yadda suka rabu,
"Ni Aunty ina ganin kaman yayi fushi" shiru Aunty ta d'an yi can tayi yar ajiyar zuciya ta dafa Shoulder d'inta tace "ba lalle ba, in dai da gaske yana da ilimin Addini to bazai ji komai ba tunda yasan gaskiya kika fad'i sai ma dai yaji dad'in hakan tunda ya gane wace kalar mata zai aura, kuma fa tana iya yuwuwa ma gwada ki yake kinsan Mutane in suna abunda suka san ba daidai ba to basu son su Auri mace mai hakan don haka karma ki wani damu wllh" kai kawai Fauzy ta jinjina amman ita tasan ba wani gwadata da yayi Saboda abubuwan da yayi mata, daga baya sakin jiki tayi suka cigaba da cin abubuwan anan Aunty ta ce yakamata ta sa yazo yayi breakfast gobe Fauzyn tace anya zai zo don yace gobe zai tafi amman dai zatayi mashi magana. Bayan ta koma d'aki a bakin gado ta zauna ta shiga tunanin ko ta kira shi saidai tana jin d'ar d'ar can dai tay k'arfin halin kiran nashi, har ta yanke bai d'auka ba ta ruk'e wayar tana dakon kiran shi kamar yadda suka saba bada jimawa ba kuwa sai gashi ya kira d'in har saida tayi murmushi taji d'an sanyi a ranta, bayan ya d'auka ya ya koma tayi mashi ya amsa mata daga haka suka yi shiru can taji yace da wani abu tace mashi eh dama Aunty d'in ta ce tace tayi mashi magana yazo da safe don Allah yayi breakfast, ce mata yay bazai samu zuwa ba don Flight d'in safe zai bi tace to tayi mashi saida safe itama yayi mata, bin wayar tayi da kallo tama rasa tunanin da zata yi jikinta ya d'an yi sanyi can dai ta mik'e don tayi shirin kwanciya...........
93
_ASM BY ZAINAB BATURE _
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~