Sashe 130
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Ana gama d'aura Aure ba 6ata lokaci aka shiga shirin tafiya da Amarya don tafiyar Mota za'ai zuwa Abuja anan za'ai Dinner in an je daga baya sai a wuce da ita Nasarawa amman an sanar ma Aunty Mareeya cewa ba mutane da yawa za'a dasu Nasarawa ba iya mutum goma suke buk'ata zuwa dai Abuja wannan ko mutum nawa suka bada lafiya lou, tun bayan da su Mujaheed suka iso kopar gidan wuri suka samu daga can gefe don kopar gidan dank'am yake da mutane ga marok'a dake ta aikin kirari da masu kad'e kad'e, rasa ta yadda zasu ga Fauzyn sukai Usman yace mashi dama saida ya fad'i mashi bafa zai iya samun ganinta ba gara su tafi daga baya shi zai mashi k'ok'arin samun lambarta sai ya kirata ya rok'eta yafiyar, Shiru Mujaheed yayi shi kad'ai yasan abunda yake ji a cikin ranshi ga tsananin mamaki da yake ganin wai duk wannan taron Fauzy akai ma shi a ranshi ya shiga raya Allah kenan sosae nadama ke dawainiya dashi. Dank'ara Dank'aran Motoci ne suka shararo cikin layin zasu kai goma sai kuma motocin Security dake a gaba da baya tare da ta yan jarida abun burgewa gaba d'aya motocin bak'ak'e ne sai k'yalli suke, cirko cirko mutane sukai suna kallon yadda ake shirya motocin, bayan an gama ne aka sanar cikin gidan cewa a fito da Amarya, rantsattsan leshi Fauzy ta saka wuyanta da hannunta na sanye da gold an d'aura mata alkyabba sai walwali take, su Aunty Mareeya iyayen hidima itama kaya ta canza daga ankon atamfar da suka yi zuwa had'add'an kuma tsadaddan lace da aka mata half gown ta coge d'aurin kallabi ya kalli gabas maso kudu harda uban glass ta k'wama, haka sauran yan gidan su ma duk sun canza shiga zuwa lace su Fatuu ma duk lace d'in ne a jikin su, ba tare da 6ata lokaci ba yan kai Amaryar suka fara fita, Akan idon Mujaheed Aunty Mareeya ta fito da ita ta rungumo kafad'arta yana ganinta ya zabura zai nufeta aikuwa da sauri Usman ya maido shi yana ce mashi bai ga Jami'ai bane a wurin, wata jibgegiyar bak'ar Jeep dake ta salk'i aka bud'e ma Aunty anan za'a saka amaryar ta kalli Fatuu dake biye da ita tace mata itama ta shigo ta zagaya ta d'aya 6angaren aka bud'e mata ta shiga itama Fauzyn aka shigar da ita tana ta yar sheshsheka da tun bayan da akayi mata fad'a take kukan, Bayan Aunty ta saka Fauzyn fitowa tayi ta rufe k'opar ta shiga nuna wanda za'ai tafiyar dasu ana bud'e masu motocin suna shiga, su gwaggo dai Motar Abbas suka shiga ita da Feenah da Saude sai Kawu Amadu Haulat kuma da Mino Mota d'aya suka shiga da Jidderh haka su Zainab k'awayen Fauzy suma Mota guda akai masu su Mom dai dama da Jeep d'insu suka zo ita suka shiga su Twins d'in Fatuu na hannunta ita da Aunty laila, saida Aunty Mareeya ta tabbatar da an shigar da kowa Mota cikin masu tafiya sannan ta dawo tasu ta bud'e ta shige ba wanda ya shiga gaban tasu don bayan driver da zai ja Motar akwae Security zaune a seat d'in gefe, wai akace ga k'oshi ga kwanan yunwa tun bayan da aka shigar da Fauzy Mota Mujaheed keta kallon Motar gaba d'aya takaici ya cika shi ji yake tamkar ya fasa ihu, da shi a haukanshi da Usman bai hana shi ba zuwa zai yi wurinta yanzu kuwa saidai sukai tsaye suka bi sahun yan kallo, sai bayan da Aunty ta koma cikin Motar ne ta natsu tana k'are mata kallo tana yi tana jinjina kai a ranta tana raya ta dai had'u ba k'arya kuma da gani sabuwa ce don seats d'in harda ledar sabuntar su ga kujerun lumtsuma lumtsuma gwanin taushi a gaban seat d'in da suke akwae screen manne da kowacce kujera da mutum zai iya yin kallo ko yayi game har internet ma zaka iya shiga ko kai connecting Bluetooth da wayar ka da dai sauran su, tsakanin su da Mutanen dake zaune a gaba akwae d'an labule na leather kalar seat d'in Motar hakan yasa basu ganin su sannan gaba d'aya glass d'in Motar tinted ne ta yadda ba'a iya hango wanda ke ciki sai dai kai kaga na waje, sosae Motar dai ta jugunu sanyin Ac nata ratsa sassan jikin su, Bayan kowa ya shiga Umarnin tafiya ake jira daga wurin Jami'an dake clearing Main titi da zasu hau su tafi, hannu Aunty Mareeya ta d'aura jikin Fauzy tace "Amarsu har yanzu kukan ake" shiru Fauzyn bata ce komai ba kuma bata d'ago ba daga sadda kan da tayi hular Alkyabbarta ta rufe mata fuska Fatuu dake latsa wayarta ta d'ago ta d'aura idonta akanta tana d'an murmushi can ta kira Sunanta k'asa k'asa ta amsa tace mata tayi hak'uri ta daina kuka don Allah,
"Uhm kukan gulma ne ba wani abu ba, nan data shige daga ciki sai munci sa'a zata tuna damu" yar dariya Fatuu tay Aunty Mareeyar tace Allah kuwa Zarah, hannu Fatuu takai ta janye hular Alkyabbar ta d'an d'ago da Fuskar Fauzyn suka had'a ido idanunta sunyi jajur ta kai hannu tana goge mata k'wallan tana fad'in ya isa hakanan kada tayi ciwon kai tana Amarya Aunty tace ta fad'i mata dai, saida tasata ta daina yin Kuka ta d'ago Fuskarta sosae, a hankali ta fara bin Mutanen dake tsaye cirko cirko suna kallon Motocin nasu da kallo, tana haka idanunta suka sauka akan Mujaheed daya tsura ma saitin inda suke ido, har zata janye idanun nata sai kuma ta tsaya kamar an dakatar da ita ta k'ura mashi ido farko bata gane shi ba kawai dai sai take jin kamar tasan mutumin dake a tsaye saida ta d'an d'auki lokaci tana kallon shi ne ta fara ganin kamar shi, a ranta ta raya anya kuwa shine taya zai zo nan k'arshe ta yanke bashi bane k'ilan dai mai kama dashi ne tana janye idanunta ta d'aura su akan Usman dake gefen shi, tana ganin shi ta ganeshi a ranta ta raya Usman tana fad'in hakan da sauri ta maido idonta kan Mujaheed lokaci guda ta shaida shine da tsananin mamaki ta furta "M...UJAHEED!" har Kusan rigen kallonta su Aunty sukai da sauri tace "ina Mujaheed d'in" hannu Fauzy ta d'aga tana nuna saitinshi ta cikin glass gaba d'ayansu harda Fatuu suka zuba mashi ido shima kuma har lokacin saitin su yake kallo saidai baisan suma kallon nashi suke ba,
"Uhm kukan gulma ne ba wani abu ba, nan data shige daga ciki sai munci sa'a zata tuna damu" yar dariya Fatuu tay Aunty Mareeyar tace Allah kuwa Zarah, hannu Fatuu takai ta janye hular Alkyabbar ta d'an d'ago da Fuskar Fauzyn suka had'a ido idanunta sunyi jajur ta kai hannu tana goge mata k'wallan tana fad'in ya isa hakanan kada tayi ciwon kai tana Amarya Aunty tace ta fad'i mata dai, saida tasata ta daina yin Kuka ta d'ago Fuskarta sosae, a hankali ta fara bin Mutanen dake tsaye cirko cirko suna kallon Motocin nasu da kallo, tana haka idanunta suka sauka akan Mujaheed daya tsura ma saitin inda suke ido, har zata janye idanun nata sai kuma ta tsaya kamar an dakatar da ita ta k'ura mashi ido farko bata gane shi ba kawai dai sai take jin kamar tasan mutumin dake a tsaye saida ta d'an d'auki lokaci tana kallon shi ne ta fara ganin kamar shi, a ranta ta raya anya kuwa shine taya zai zo nan k'arshe ta yanke bashi bane k'ilan dai mai kama dashi ne tana janye idanunta ta d'aura su akan Usman dake gefen shi, tana ganin shi ta ganeshi a ranta ta raya Usman tana fad'in hakan da sauri ta maido idonta kan Mujaheed lokaci guda ta shaida shine da tsananin mamaki ta furta "M...UJAHEED!" har Kusan rigen kallonta su Aunty sukai da sauri tace "ina Mujaheed d'in" hannu Fauzy ta d'aga tana nuna saitinshi ta cikin glass gaba d'ayansu harda Fatuu suka zuba mashi ido shima kuma har lokacin saitin su yake kallo saidai baisan suma kallon nashi suke ba,