← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 80 OF 211

Sashe 80

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Where is our Baby, ya fara kicking?" waro ido tay ta d'an bud'e baki sai kuma ta saki dariya tace ai bai isa wannan ba ko abunda ko antenatal bata fara zuwa ba, tambayar ta yay sai yaushe zata fara zuwa tace kaman in yayi 4 Month amman ko yanzu tunda ta ya wuce 3 months zata iya fara zuwa ya jinjina mata kai, shiru suka d'an yi sai kuma tace bari babyn yaga Daddy d'inshi ta kai hannu ta d'aga rigarta farar fatar cikin da ya turo ta bayyana ta kai wayar saitin cikin, Kusan kullum ne in sukai waya sai yaga cikin wani lokacin shi ke cewa ta nuna mashi wani lokacin kuma ita ke nuna mashi kamar yanzu, maido wayar tay saitin fuskarta tana dariya shima ita yake yi yace mata yaga ya k'ara girma tace eh ai bata dad'e da gama cin Abinci ba taci ta k'oshi stiil yar dariya yake yace ai an fad'i mashi Abinci take ci sosae, jin haka yasa ta fara bashi labarin yadda a kai ta mamaki wai tayi uban kumatu harda Maganar da Hajiya tayi d'azun tace Saboda cin Abincin da take ko yan hud'u akace zata Haifa ba za'ai gardama ba dariya yay itama ita take yi, bin juna da kallo su kai mai cike da tsantsar k'auna bayan sun lafa da dariyar sun koma yin murmushi,

"Yar fillo zata Haifa yaron Ya Handsome" suna cikin kallon junan taji ya furta hakan, dariya ta k'ara sakawa ta kai hannu ta rufe idanunta alamar kunya can ta cire idanunshi akanta yana murmushi tace mashi mamaki yake a hankali ya girgiza mata kai alamar a'a, tambayar shi tay yaushe zai zo d'in yay d'an jimm kafin yace mata yay postponing lokacin sai nan da 3 weeks, k'amewa tay tana mashi wani kallo ta tsuke fuska yay d'an murmushi, yamutsa fuska ta shiga yi kaman zatai kuka tace ita dae bata yarda ba kenan ma bai yi missing d'inta ba an kusa fa wata biyu da tafiyar shi kuma shine yanzu zai ce ya d'aga lokacin da zai dawo, sigh yay yace itama tasan ko bai fad'i mata ba yana missing nata in every second yana jin kewarta a tare da shi,

"To miyasa ka d'aga dawowar" ta tambaya a shagwabe, hannu ya kai ya shafi gaban kanshi calmly yace mata an kusa bikin Saleem ne shine ya bari sai lokacin yazo so that he can stay a bit long, k'una k'unin shagwa6a ta shiga yi tana jujjuya kai ya hau bata hak'uri yana d'an murmushi, ganin tak'i barin abunda take yi yasa shi ce mata "Ok, in kina so in zo this coming week zan zo but bazan dad'e ba zan dawo tunda ina son zuwa bikin Saleem d'in amman hakan zai sa a ga na fara wasa da aiki tunda ban dad'e dana dawo ba kuma kinga na d'au lokaci anan" dakata tay da abunda take yi na shagwabar tace "Shikenan to na yarda ka bari sai lokacin ka zo amman fa sai ka maimaita man lokacin da kayi anan in kazo wata biyu da rabi zakai sannan ka koma" ta k'arasa ta d'an kumburo baki, yar dariya yay yace tayi mashi hak'uri kar tasa a kore shi a wurin aiki, kafin ta bashi amsa taji an turo k'opar bedroom d'in ta d'aga ido, Fauzy ce ta lek'o suka had'a ido tay mata murmushi, juyawa tay ta koma dama sun dawo ne shine ta lek'o taga mi Fatun ke yi,

"To ba Shikenan ba in sun kore kan sai ka baro masu K'asar su ka dawo nan kawai" ta bashi amsa,
d'age gira yay "to in na dawo ya zamu rink'a samun kud'i?" da sauri tace "to mi zamuyi da kud'in tunda muna da komai" yana yar dariya yace ta ta6a ganin rayuwa ta yuwu ba kud'i dole ai su buk'aci abubuwa kaman Abinci, kaya, da kuma kud'in yin wasu hidindimun gashi ma zata haihu dole su buk'aci kud'i,

nok'e kai tay tace "to ba sai Hajiya dasu Daddy ba su rink'a mana wannan" fad'ad'a dariyar shi yay itama dariyar take yace mata ta dai bari gara su nemi nasu yadda bazasu takura ma kowa ba har a gaji da su,

"to ai zaka iya samun wani aikin ma anan ko da baka fara ba kafin ka tafi" d'an rolling eyes d'in shi yay yace mata ai anfi samun kud'in sosae anan, tambayarshi tay wai dama Saleem bai yi aure ba yace eh an dai dad'e da akai engaging nasu to wadda zai auran tana karatu a London da za'ai auren sai tayi completing karatun a gidan shi daga baya kuma sai aka bari ta gama don shima Saleem d'in yaje ya k'aro karatu sai yanzu za'ai Auren, jinjina kai Fatun tay suka cigaba da hirar su ta k'auna, ganin ta fara hamma yace bari ya barta tayi bacci kar a takura ma Baby tay yar dariya, tambayarta yay ko akwae abunda take buk'ata da sauri ta d'aga mashi kai alamar eh yace miye take so, ce mashi tay irin tuwan Madara da gullisuwa da Popcorn d'in da yake siyo mata take son ci yace Ok zai ma Nana magana sai a kawo mata tomorrow, jin sunan Nana yasata tambayar wai tana nan yace eh, ta tambayi har yanzu bata yi Aure ba yace eh amman anyi engagement,

"Allah sarki na taya ta murna wllh, kai dai ai ka k'i ta" ta fad'a tana murmushi, shiru ya d'an yi sai kuma yace ai lokaci bai k'ure ba in tana son ya auretan da yayi Magana yasan za'a fasa da wanda aka sa masu rana sai ayi dashi, wani kallo tay mashi a d'an k'ufule tace "to a'a wllh, ba kasan da wasa nike ba" yadda ta yi ne ya bashi dariya yace "tunda tana sona da ki bari in k'ara da ita kinga kema kin yi man Alfarma irin na Fanan" yana rufe baki da sauri ta hau yamutsa tana girgiza kai tare da yarfa hannu tana fad'in "Don Allah Hubby mu bar Maganar nan, tunda an sa mata rana ba Shikenan ba nima dama ai wasa nike ko" dariya kawai yake ganin yadda tay k'utun k'utun da rai sai kace ba ita ta ja Maganar ba, ganin irin kallon da yake mata yasa taci gaba da fad'in "Allah ka gama aure, ba wata da zaka k'ara aura mu biyu mun ishe ka" dariya ya k'ara yi har jerarrun hakoransa suka bayyana sosae ita kuma taci gaba da yamutsa fuska tana k'una k'unin Allah bazai k'ara aure ba,

"Ki kwantar da hankali, tunda na same ki Baby na gama aure am just teasing you" wani irin murmushin jin dad'in Maganar ta shiga saki harda d'age kai sama, sauke kan nata tay idanunta suka shiga cikin nashi a wani slow ta lumshe mashi ido ta furta "Ina son ka har abada abadan abada Hubby" shima lumshe mata idon yay cikin cool voice d'in shi ya furta "You are the best thing that has ever happened to me Baby, you made me feel complete" murmushi kawai take saki looking at him with much luv, sallama sukai yace ta kwanta shima sun samu break ne zai yi lunch tace to ai duk yama cinye lokacin suna hira yana murmushi yace ba wani abu ai ko bai ci komai ba ganinta da yayi ya k'osar dashi tana dariyar jin dad'i tace duk da haka dai yaje ya ci Abincin kuma Baby yace ya tabbatar yaci ya k'oshi, yace a fad'i ma Babyn Dad d'in shi zai bi umarni gaba d'aya sukai dariya daga haka suka gama Vedio call d'in, kwance tay saman gadon tana ta faman sakin murmushi wani irin nishadi na ratsata ita kanta tasan ba K'aramin so take ma Haisam ba a yadda take ji yanzu da suka zama d'aya she can't survive without him, a haka bacci yay awon gaba da ita, bada jimawa ba Fauzy ta shigo don tayi wanka ganin yadda Fatun tay bacci yasa ta yin d'an murmushi, saida ta tashe ta don ta gyara kwanciyar ta sannan ta nufi hanyar laundry, d'aure da towel a kirjinta ta fito ta nufi gaban mirror don ta shafa mai bayan ta gama ta nufi closet ta bud'e, wata doguwar rigar baccin Fatuu ta fiddo don ta saka, tana gama shiryawa Mino ta shigo ita dama tun a can gida da suka je ta shiryo cikin kayan bacci riga da wando, gado ta nufa tana fad'in wllh bacci take ji Fauzy data juya tana kallonta tace ta hak'ura da ganin k'arshen film d'in kenan tace eh ai taga basu da niyyar gamawa daga haka ta haye gadon ta ja duvet ta lullube, bakin gado Fauzy ta nufa ta zauna tay shiru, gaba d'aya ganin Fatuu da ciki ya k'ara mata jin son yin aure, dama dalilin auren Fatun taji ta fara sha'awar itama tayi, "gashi ba mijin..." wata zuciyar ta raya mata har saida tay yar dariya, ita gaba d'aya ma ta kasa gane ko tana son Sameer kawai dai tasan yana burgeta, wayarta dake ruk'e a hannunta ta bud'e ta fara latsa ta, gallery ta shiga ta bud'e inda hotunan bikin Fatuu suke ta bud'o wani hoton Sameer da aka yi mashi a wurin Dinner dama tana yawan kallon hoton, k'ura mashi ido tay yana a hakimce kan kujera fuskar nan ba annuri a cikin Zuciyarta ta shiga raya shin da gaske yana sonta, in hakane to miyasa yak'i bayyana mata, kai anya ma kuwa ita sam bata tunanin hakan gaskiya don tana ganin bata kai ya so ta ba,
"in yanzu yazo yace yana son ki zai aure ki zaki amince?" wata zuciyar ta jefo mata tambayar tay shiru kamar mai nazarin wani abu lokaci guda jikinta yay sanyi tunowa da wasu abubuwa, fita tayi daga wurin hoton a sanyaye ta mik'e ta nufi bedside table ta aje wayar har zata juyo ta dakata ta kai hannu ta kunna lamp sannan ta juyo, wurin Switch ta nufa ta kashe hasken d'akin kafin ta juyo ta dawo wurin gadon ta haye gefe ta yadda sun saka Fatuu a tsakiya, lamo tay tana ta zancen zuci ta d'auki lokaci a haka kafin daga baya bacci ya d'auketa.
Chapter 80 · 0% Book details