← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 94 OF 211

Sashe 94

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Alhamdulillah Allah yayi dare gari ya waye an shigo Asabar lafiya, tun da sassafe yan gidan suka tashi aka hau gyaran gida masu aikin Abinci duk acan gidan Yaya Mubarak d'in suka kwana, Misalin k'arfe sha biyu na rana bak'in suka iso garin, kiran Mahaifin su Fauzy sukai suka sanar dashi game da isowar tasu don aje ayo masu jagora, dama Yaya Mubarak na gidan isowar su kawai ake jira shi ya tafi don ya taho da su, bada jimawa ba suka iso layin gidan Motoci guda biyu ne d'aya jibgegiyar bakar Jeep ce wadda anan bakin suke sai k'arama wadda itama bak'a ce sai faman salk'i motocin suke anan kuma security ne cikinta gaba da baya don a cikin bak'in harda Commissioner wanda d'an uwa ne kuma abokin mahaifin Sameer d'in ne sai sauran mutum biyun d'aya k'anin Governor d'in ne uwa d'aya uba d'aya sai d'ayan cousin brother d'in Governor d'in ne matsayin Yayan shi yake, Mahaifin su Fauzy ne tare da yanuwan shi guda biyu sai Yaya Mubarak da wasu daga cikin manyan Yayan shi maza guda ukku suka tarbe su cikin girmamawa kowanne cikin bak'in na sanye da babbar riga ta alfarma mutum biyu farar shadda ce sai d'aya ash, security d'in wanda jami'an yan sanda ne guda biyu sai guda biyu na civil defence ne su basu shiga ba suna a cikin Motar amman sun bud'e kopopin sai lokacin Jama'a suka samu abun baza ido da kyau yara da Almajirai ba sosae ba duk sun tsaya cirko cirko suna kallon Motocin haka Mutanen dake wucewa kowa idon shi na akan Motocin da kuma wad'anda ke zaune a bakin shaguna sai faman tambayar juna abunda ke faruwa a gidan suke wanda kuma ba mai amsa. A mutunce aka shiga gaggaisawa parlon sai zabga uban k'amshi yake daga baya aka fara gabatar da kai, su Aunty Mareeya ne suka fara shigowa da kayan abinci suna jerawa a saman Dining duk sun yi wanka sun sa kaya masu kyau, bayan sun gama suka shigo parlon duk suka zauna a saman Carpet suna masu sannu da zuwa tare da gaishe su, haka akai ta shigowa gaishe dasu ana fita, k'anin Governor d'inne da fara'a ya tambayi harda Amaryar acikin wad'anda suka zo gaishe dasu Yaya Mubarak yace a'a ita tana Katsina acan take zaune a wurin Yayarta yayi masu kwatancen Aunty Mareeya suka ce sun gane yace to a wurinta take, bayan an gama yan gaishe gaishen Yaya Mubarak yayi masu Maganar Abinci suka ce da su fara abunda ya kawo su tukun don ba dad'ewa zasu yi ba, neman Auren Fauzy sukai aka basu sannan aka fara maganar saka rana, a yadda suka ce shi Angon so yake asa lokacin da zata gama karatu amman in hakan bai masu ba suna da damar saka duk lokacin da yayi masu, shawara suka shiga yi Yaya Mubarak ne yace yana ganin su shiga ciki sai a tattauna harda iyayen su mata duk suka amince da hakan, ce masu suka yi bari su basu wuri su ci Abinci bayan sun gama sai a k'arasa saka ranar bak'in suka ce to ba matsala duk suka mik'e suka nufi cikin gidan Yaya Mubarak ne ya tsaya don yayi serving nasu Abincin,

A can cikin gidan gaba d'aya sun taru a parlon Mahaifiyar Fauzy harda Aunty Mareeya anata shawarwarin kan lokacin da za'a saka, shi mahaifin Fauzy nuna masu yake gaskiya wata bakwae kamar yayi kusa don yanzu lokaci gudu yake kaman gobe ne za'a ga yayi azo kuma ba'a gama shiryawa ba,

"Ni a ganina Baba kawai a amince da lokacin da Sameer d'in ke so Maganar shiryawa kuma in sha Allahu ba abunda zai gagara watak'il ma fa suce basu son ayi mata kayan d'aki" Aunty ta fad'a,
Malam Sama'ila k'anin Baban nasu ne yace "nima abunda nike tunani kenan tunda dai ai sun fi k'arfin duk wani abu da za'a yi ma Yarinyar",

gwaggo ce tace "hakane, amman dai bai kamata a dogara da hakan ba in dai basu suka ce kar ayin ba yakamata ayi mata komai daidai bakin gwargwado" Baban su ne ya kalli Mahaifiyar tasu yace ita bata ce komai ba tay dan murmushi a sanyaye tace "to ita a ganinta kawai a bi yadda yaron ke so don ko ya aka sa dai lokacin zuwa zai yi kuma indai a cikin wata bakwae ba'ayi shirin daya kamata ba to ko an wuce hakan ba lalle ayi yadda ya kamatan ba" Aunty Mareeya da Baba Sama'ila ne suka ce wannan gaskiya ne, suna haka Yaya Mubarak ya shigo ya gama zuzzuba masu Abincin, bayan ya zauna ya tambayi a wace matsaya aka tsaya Aunty tayi mashi bayani, to shima dai bayan Mahaifiyar su ya bi yace abunda ta fad'a gaskiya ne kawai a amince da hakan ayi fatan Allah ya kaimu ya kuma rufa asiri ai duk ba sai an zurfafa ba tunda dai ansan wacece za'a aura duk aka ce gaskiya ne, dariya Baba Rabi'u wanda Yayan mahaifin nasu ne yayi yace Fauziyya ta giggi6o masu aiki har sai anyi meeting sannan za'a saka mata rana duk akayi dariya. Lokacin da suka koma parlon har sun gama cin Abincin sun dawo sun zauna bayan sun zauna cikin girmamawa su Baba Sama'ila suka tambayi sun dai ci sosae ko suda suka yanko hanya suna fara'a suka ce Alhamdulillah sun gode, cigaba da zancen saka ranar sukai suka ce lafiya lou a saka hakan, tambayar Date d'in da zasu gama Makarantar sukai duk basu sani ba Yaya Mubarak ne ya tashi don ya tambayo Aunty Mareeya, itama cewa tayi bata sani ba aka kirawo Fauzy a waya tace itama bata san date d'in ba kawai watan ta sani, bayan Yaya Mubarak ya koma ya sanar masu yadda sukai k'arshe aka sa bayan ta gama Makarantar da sati biyu kawai, nan kowa ya amince aka hau Addu'oi da fatan Alkhairi, kud'i suka bada miliyan d'aya na neman aure da kuma kayan saka rana don basu taho da komai ba, anan parlon suka yi jam'in sallar Azahar gaba d'aya harda security d'in bayan sun gama aka shiga yin sallama su Aunty Mareeya ma duk suka zo suka yi masu sallama da godiya da kuma Addu'oin Allah ya maida su lafiya suna fara'a suke amsawa suka ce sai Allah ya kaimu biki kuma, tare duk suka fita dasu iyayen Fauzyn maza aka shiga k'ara yin sallama daga baya suka tafi, Aunty na komawa cikin gidan ta kira Fauzy lokacin tana zaune a saman gadonta tayi zuru tun bayan da aka kirata aka tambayi date d'in da zasu gama Makaranta gaba d'aya taji jikinta yay wani irin sanyi, lokacin da kiran Auntyn ya shigo har saida gabanta ya fad'i, hannunta har d'an rawa yake ta d'aukko wayar, tana yin picking Aunty ta rangad'a wata uwar gud'a tana fad'in Allah ya yarda an saka ranarta da Sameer suna gama Makaranta da sati biyu, runtse ido Fauzy tayi ta d'an cize baki Aunty tace bazata yi magana ba ko bata farinciki kawai sai ji tayi ta fashe mata da kuka, shewa Aunty tayi tace "yi kuka Fauziyya kin cancanci ki yi kukan farinciki" fad'i mata kud'in da suka kawo tayi cikin Muryar kuka ta tambayi yaushe zata dawo tace gobe in Allah ya kaimu, sauran yan gidan ne suka shiga amsar wayar suna mata Allah yasa Alkhairi harda gwaggo da Mahaifiyar ta, bayan sun gama wayar falon Baban suka koma baki d'ayan su harda iyaye mata aka cigaba da farinciki su Aunty suka sassauko da kayan Abincin nan cikin parlon kan Carpet aka cigaba da shagali don ba laifi sunyi abubuwa da d'an yawa kuma duka kad'an bak'in nasu suka ci, To Alhamdulillah sai fatan Allah ya nuna mana Auren Fauziyya da Sameer.......

92

_ASM BY ZAINAB BATURE_

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

.......A jiya Friday Haisam ya tafi Abuja daga can zai koma Us, lokacin da Fauzy ta kira Fatuu ta sanar mata da zancen saka ranarta tana a zaune parlon Hajiya, wata uwar k'arar murna ta saka ta hau yarfa hannu tana fad'in "Wayyo dad'i k'awata na taya ki murna wllh Allah ya sa Alkhairi ya kaimu lokacin da rai da lafiya" sai faman murna take ta kasa rufe baki, bayan ta gama wayar Hajiya ta tambayi abunda ya faru Fatun ta fad'i mata itama sosae tayi mamakin jin zancen Sameer zai auri Fauzy daga baya ta tayata murna tayi fatan Alkhairi, kiran gwaggo Fatuu tayi cike da Farinciki ta sanar mata dama tasan da Maganar itama murna ta tayata tayi fatan Alkhairi da Addu'oi,
Chapter 94 · 0% Book details