← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 179 OF 211

Sashe 179

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Bayan President Ali ya hau mulki da wasu watanni ya za6i Ministocin da zasu yi aiki tare ciki harda Hajiya Maryam ita ya za6a matsayin Minister of Industry, Trade and Investment wato Ministan Masana'antu, Kasuwanci da Zuba jari wanda babban muƙami ne acikin ministoci kuma ya bi cancanta ne shiyasa ya bata saboda kasuwanci ta karanta gata babbar yar kasuwa, Haisam ma yaso ya bashi Minister of Communication and Digital Economy lokacin daya tuntu6eshi kan yana son bashi muƙamin Haisam ɗin ya nuna mashi hakan zai iya zama wani abun magana ace yaba ɗan shi Minister Daddyn nashi yace shi ba ruwan shi tunda cancanta ya bi ba son rai ba amman Haisam ɗin ya bashi haƙuri yace yaba wani wanda ya cancanta saboda shi yafi son ya maida hankali akan Companyn shi da ake cikin ginawa anan Abuja, ƙarshe sai dai wani ɗin aka ba dama kujerar sonta ake, Mahaifin Sameer ma ya bashi Minister of Foreign affairs wato Ministan harkokin waje haka Kawunsu Mani mijin Gwaggo ya bashi P.A ɗin shi haka dai akaita rarraba muƙamai saidai duk cancanta ya bi bayan an tantance su a National Assembly suka shiga gudanar da aiyukansu su Hajiya Maryam an samu dalilin soke kallabi da hujja,

Bayan shigar su Hajiya Maryam Office tace ma Farha ta dawo Lagos don ta kula da ƙannanta saboda ita yanzu bata cika zama a Lagos ba, gaba ɗaya ita da Kamal sun shiga damuwar rabuwa da juna don sun shaƙu sosae haka dai suka rabun ta tafi Abuja don Hajiya Maryam ɗin na can Villa a apartment ɗin da Ministoci ke zama daga baya Farhar tare da Dad ɗin su da ƙannan nata suka koma Lagos saboda karatun su da kuma aikin Dad ɗin su, su Gwaggo Matar P.A Duniya sabuwa jin daɗi na musamman ake tuni har ta fara canzawa gashi wani ikon Allah sosae Kawu Mani ke ji da ita duk da tafi sauran matanshi manyan taka, cikin Haulat na cika wata tara ta haiho ƙaton saurayi mai kama da Kawu Amadu sak kowa yayi murna karma Fatuu taji Lokacin data ga Vedio ɗin jaririn ji tayi Kamar tayi tsuntsuwa ta taho yaron yaci sunan mahaifin Amadu wato Abdullahi,

Tun bayan da Farha ta koma gida ta rasa mike mata daɗi don gaba ɗaya kewar Kamal ta addabeta duk da suna yin waya sosae suna kuma yin Vedio call duk hakan bai mata ba so take kawai ta gan su a tare hakan yasa ta gane ta kamu da son shi ta shiga tunanin yadda zata sanar mashi, ana haka Cousin brother ɗinta wato ɗan Yayan Mahaifinta mai suna Emran shima Bature ne ɗan America da suke soyayya dashi duk iyayensu sun san da Maganar yayi mata Maganar aure tunda ta gama karatu, yana mata zancen aure taji gaba ɗaya ya fitar mata a rai bata son auren shi hakan yasa tace mashi ba yanzu zata yi aure ba don zata cigaba da Karatu ne ya nuna mata ai lafiya lou zasu iya yin auren sai taci gaba da karatun a America, ganin ya takura mata da Maganar ita kuma sai kauce kauce take mashi yaƙi ya k
Ƙyaleta ƙarshe ma sai cewa yayi zai ma Dad ɗin shi Maganar suyi Magana da Dad ɗinta sai kawai ta fito mashi a mutum tace mashi itafa ta daina son shi don haka bazata aure shi ba, sosae hankalinshi ya tashi da yake Vedio call suke ta faɗi mashi hakan harda ƙwallan shi yana faɗin ya zata yi mashi haka bayan suna son junansu duk an sani yanata zaman jiranta har ta gama karatu kuma sai yanzu tace bata son shi, magiya ya shiga yi mata kan in laifi yayi mata tayi haƙuri ta faɗi mashi zai gyara in kuma wani abu take so ko minene ko nawa yake ta faɗi mashi zai siya mata amman don Allah kar ta guje shi don itace rayuwar shi bazai iya rayuwa ba tare da ita ba, duk yadda yay da ita taƙi canza ra'ayi ƙarshe ma sai ta faɗi mashi ta samu wani ne shi take son ta aura aukuwa wannan Maganar ba ƙaramin dugunzuma ran shi tayi ba, bayan sun gama yin wayar zugudum tayi ta rasa mike mata daɗi don tabbas tasan Emran na masifar sonta sosae yake mata ɗawainiya kullum cikin turo mata kuɗi yake kuma itama tana son shi amman yanzu gaba ɗaya taji ya fitar mata a rai ba wanda ke mata yawo a cikin zuciya sai Kamal, sanin tabbas Emran ɗin zai faɗi ma iyayenta abunda ya faru kuma za'a iya kiranta a tambayeta waye wanda tace yanzu shi take so yasa ta yanke faɗi ma Kamal cewa tana son shi, Vedio call ta kira shi lokacin da yamma ne bai daɗe da dawowa daga Makaranta ba yayi wanka ya ɗan kwanta yana hutawa kafin a kira Magrib, yana murmushi suka gaisa daga haka tayi shiru tana ta kallonshi ya lura kaman tana cikin damuwa hakan yasa ya tambayeta wani abu na damunta ne ta ɗaga mashi kai alamar eh, jin haka yasa shi tashi zaune da sauri cikin nuna kulawa ya tambayi mike damunta ne, shiru ta ɗan yi kafin tace mashi in yaji damuwarta zai mata magani ne da sauri yace in yana da ikon yin hakan zai yi tace yayi alƙawari yace mata eh,

"Kamal ina son ka, kuma so nike muyi Aure ni da kai" Kamar saukar aradu haka yaji Maganar gaba ɗaya ya zaro idanun shi yana kallonta cikin rawar murya yace amma dai tana mashi wasa ne ko ta girgiza mashi kai kafin tace da gaske take bayan ta dawo ne ta gane ta kamu da son shi, gaban shi ne ya shiga faɗuwa don bai ta6a zaton zatayi mashi irin wannan Maganar ba koda suke shiri da juna, gaba ɗaya rasa amsar da zai bata yayi sai kallonta kawai yake itama haka can tace mashi yayi shiru bai ce komai ba gashi yayi mata alƙawarin maganin damuwarta da ƙyar ya buɗe baki yace mata shi ai baisan wannan ce damuwarta ba, da ɗan alamun tashin hankali tace kenan bai amince da soyayyarta ba,
Chapter 179 · 0% Book details