Sashe 98
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Amman dai Fauziyya wani lokacin kaman d'an kai gare ki wllh ya zaki bar shi a waje maimakon ki shigo da shi" a d'an harzuk'e tayi maganar Fauzy ta bata amsa da ai shine yace ta shigo ta fad'i, da sauri Aunty ta mik'e tana fad'in don Allah taje ta shigo da shi ta nufi gaban wardrobe don ta saka kaya, a tare da shi suka shigo cikin parlon yana biye da ita, nuna mashi kujera tayi tana murmushi tace "have a sit" saida ya kalleta cikin ido sannan ya nufi kujera 2 seater ya zauna, tsaye tay ta had'e hannuwanta tana kallon shi da murmushi shi ma idon shi na kanta yana bin ta da wani kallo da sai kace yar harararta yake amman ta fahimci wani lokacin haka yake kallon shi, ganin tayi mashi kerere yasa ya furta mata bata iya neman wuri ta zauna, kujerar dake gefen tashi ta nufa ta zauna,
"Aunty tana zuwa yanzu" bayan d'an wani lokaci ta fad'a ya jinjina mata kai,
"Ka zo lafiya" ta tambaya still Murmushi take yay shiru sai kuma ya amsa mata da lafiya, janye idon shi yay daga kan ta ya jinginar da shi ajikin kujerar tare da lumshe ido, tana ta kallon shi can ta furta ya gaji ne yana a yadda yake ya d'an girgiza mata kai, juyar da kai tayi daga barin kallon shi a ranta tana raya magana dashi aiki ce babba, lokacin Aunty ta fito ta nufo cikin parlon tana sanye da doguwar rigar had'addan lace ta sa d'an kunnan zinari hannunta sanye da Agogo haka kanta tayi d'aurin kallabi mai kyau, tun kafin ta k'araso ta shiga washe baki idon ta akan Sameer da ya lumshe ido, saida tayi sallama sannan slowly ya bud'e idon nashi, a kujerar gefen wadda Fauzy take ta zauna tana faffad'an murmushi tace "Barka da zuwa, fatan an zo lafiya" amsa mata yay da lafiya lou ya janye idon shi daga kanta, k'ara tambayar ya ya baro Mutanen gida tayi ya amsa da lafiya ba tare daya k'ara kallon ta ba, shiru duk sukai tana murmushi idon ta akan shi can ta k'ara cewa "an gode da abubuwan Alkhairi Allah ubangiji ya k'ara girma da daukaka" slowly ya furta "Ameen" ta d'an kalli Fauzy dake d'an murmushi itama shine akan fuskar tata, shiru duk sukai parlon sai kace ba mutane Aunty Mareeya sai d'an kai idon ta take tana kallon shi acikin ranta ta shiga tuno da ranar data fara ganin shi da suka zo Abuja bata ta6a zaton akwai ranar da zasu zauna haka da shi bama balle ta kai ga zancen Auren k'anwarta, mik'ewa tay tayi ma Fauzy alamar ta biyo ta da hannu ta mik'e saida ta kalleshi tace mashi tana zuwa ya d'aga mata kai, wurin dining suka nufa Aunty ta nuna mata kayan abinci dake sama k'asa k'asa da murya tace "gashi nan sai ki mashi magana yazo ki serving nashi" kai Fauzy ta d'aga idon ta akan jigunannun Warmers d'in da aka jera a saman table d'in set biyu babba da k'arama set d'aya na Aunty ne ta san su d'ayan kuma sam bata san Aunty dasu ba a ranta ta raya k'ilan duk na chef d'inne amman sun had'u ba k'arya, bubbud'e mata su ta shiga yi babba d'aya farar shinkafa ce washarr washar gata zak'o zak'o sai k'aramar warmer d'inta tana bud'e ta wani irin kamshi mai dadi ne ya karad'e wurin vegetable soup ce gwanin kyau a ido ingredients d'inta an yanka su manya manya taji hanta, d'ayar babbar Warmer d'in kuma fried spaghetti ce tayi brown gwanin burgewa itama sai faman zuba k'amshin spices take gashi tasha vegetables su tsanwan tattasai Karas koran wake da dai sauran su gashi tasha nama ca6a ca6a, d'ayar warmer d'in ta k'arshe kuma pepper chicken ne ciki, bayan ta gama bubbud'a mata tace mata akwae coleslaw a cikin Fridge,
"Amman Aunty duka order d'in nasu kikai?" Fauzy ta tambaya k'asa k'asa,
"eh mana daga lokacin da kika fad'i man zai zo zuwa yanzu ina zan iya yin wani lafiyayyen Abinci har gara ma spaghetti za'a iya yi amman kuma ba komai nike da shi ba na kayan had'ata tayi kyau haka, kai Fauzy ta jinjina tace hakane, "amman ai sun yi haka ko?" da sauri Fauzy tace "ah sosae ma kin yi mana dubara naji dad'i wllh" yar dariya Aunty tay tace "jin dad'in ki your excellency shine nawa" hannu Fauzy ta kai ta gumtse dariya,
"Yanzu kije ki mashi magana yazo ya ci" kai Fauzy ta d'aga sai kuma tace "Allah ma yasa ba wahalar banza akai ba ta tanadar su don yana iya k'in ci wllh" da sauri Aunty Mareeya tace "in ya ki ci ai ke zaki sashi dole yaci ko, taya zai tako yazo kuma yace bazai ci komai ba ke kuma ki bishi da ido, anya Fauziyya, gaba d'aya wani lokacin sai ki kaman ba wayyaya ba wllh na lura kaman baki iya soyayya ba ko dai kin k'arar da ita a wurin shashasha d'in can, kije ki mashi magana in ya nuna bazai ci ba kice baki yarda ba sai ya ci a cikin sigar yar shagwaba shagwaba zaki mashi magana dole fa sai kin zage damtse wllh ke ce zaki koya mashi sakin jiki da mutane bama kamar ke in ba haka ba yana a haka d'in can wllh kece Masha wuya ki ga fa yadda magana ke mashi mugun wahala ga ba sakin fuska don ma dai d'aurewar na mashi kyau tunda kyakkyawan ne....kinga an bar shi shi kad'ai jeki ki mashi magana bari in d'aukko coleslaw d'in akwai ma lemuna a cikin Fridge d'in sai ki tambayi wanda yake so in kuma sai giyar da kika ce yana sha sai kije ki nemo mashi" gwalo ido Fauzy tay jin Maganar tata ta k'arshe Auntyn ta sa dariya ta juya tana fad'in taje, komawa tayi cikin parlon Sameer d'in nata latsa waya har zata zauna a inda ta tashi sai kuma ta tuna da hud'ubar Aunty a d'arare ta nufi inda yake a hankali ta zauna daga gefen shi, idonta akan shi tace "am sorry an bar ka kai kadai naje yin abu ne" kai ya jinjina mata ba tare daya kalleta ba,
"Muje ka ci Abinci" d'an jimm yay kafin ya juyo suka had'a ido tana mashi murmushi, kokarin mik'ewa ta fara taji yace mata ya k'oshi hakan yasa ta koma ta zauna,
"Amman ya zaka ce ka k'oshi bayan nan kazo dole ai kaji yunwa" d'an girgiza mata kai yay yace ba nan ya fara zuwa ba so ya ci Abinci a inda ya sauka, tambayar shi tay a ina ya sauka ya bata amsa da Government House, marairaice mashi fuska tay tace "to amman dai ai nan ma yakamata kaci Abinci tunda nasan Saboda n...." Kasa k'arasa Maganar tay idon shi a kanta slowly yace yana jin ta alamar taci gaba, kikkafta idanu ta shiga yi tana motsa baki ganin irin kallon da yake mata ne yasa da k'yar ta furta "Saboda ni ka zo" kawai sai gani tay yay d'an murmushin gefe wanda tunda yazo bai yi kamar shi ba don har gefen fuskar tashi ya d'an lotsa, d'age mata gira yay yace "Who told you dat?" shiru tay tana cigaba da kikkafta ido taji ya sake cewa ba tambayar ta yayi ba,
"Ba kowa, ni nayi tunanin hakan" shiru yay yana kallon ta cikin k'arfin hali ta furta "hakane?" wani kalan motsa baki yay tare da yi mata wani kallo yace in ta cancanci hakan to hakane, faffad'an murmushi tayi tace "eh nayi deserving hakan" d'an ta6e baki yay da alamun murmushi yace a matsayinta na wa ba tare da jin wani d'ar ba ta furta "Your wife to be in sha Allah" bin ta yay kawai da ido sai murmushi take tana niyyar k'ara yin magana Mijin Aunty Mareeya ya sawo kai cikin parlon da sallama su Hanif na biye da shi gaba d'aya suka kai idon su akan shi ganin shine yasa Fauzy saurin sauke kanta don sai taji kunyar zamanta a kujera d'aya da Sameer ta kamata, inda suke ya nufo yana zuwa gaban Sameer cikin sakin fuska ya bashi hannu suka gaisa yayi mashi an zo lafiya nan ma ya amsa mashi, d'an rankwafawa Hanif yayi yace mashi ina wuni ganin haka yasa su sultan ma suka yi duk ya amsa masu fuskar shi a d'an sake, juyawa Abban Hanif yay bayan sun gama gaisawar ya nufi hanyar Bedroom su Hanif na biye dashi gaba d'ayan su Uniform ne ajikinsu sun goya School bag da gani daga Makaranta ya d'aukko su ,
"Pls muje kaci Abincin" Fauzy ta fad'a da yar sigar shagwaba idon shi akanta yay shiru, mikewa tayi tana mashi wani kallo a kokarin ta na tayi abunda Aunty tace, shiru ya d'an yi kafin yace shi bai cin Abinci in ya riga ya koshi ya fad'a mata ya riga ya ci so ba sai yaci wannan ba, tsaye tayi tana kallon shi bayan ya gama yin Maganar shima kallon nata yake can ta nufi kujerar gefen shi ta zauna ta maida fuskarta tana kallon gefe,
"Aunty tana zuwa yanzu" bayan d'an wani lokaci ta fad'a ya jinjina mata kai,
"Ka zo lafiya" ta tambaya still Murmushi take yay shiru sai kuma ya amsa mata da lafiya, janye idon shi yay daga kan ta ya jinginar da shi ajikin kujerar tare da lumshe ido, tana ta kallon shi can ta furta ya gaji ne yana a yadda yake ya d'an girgiza mata kai, juyar da kai tayi daga barin kallon shi a ranta tana raya magana dashi aiki ce babba, lokacin Aunty ta fito ta nufo cikin parlon tana sanye da doguwar rigar had'addan lace ta sa d'an kunnan zinari hannunta sanye da Agogo haka kanta tayi d'aurin kallabi mai kyau, tun kafin ta k'araso ta shiga washe baki idon ta akan Sameer da ya lumshe ido, saida tayi sallama sannan slowly ya bud'e idon nashi, a kujerar gefen wadda Fauzy take ta zauna tana faffad'an murmushi tace "Barka da zuwa, fatan an zo lafiya" amsa mata yay da lafiya lou ya janye idon shi daga kanta, k'ara tambayar ya ya baro Mutanen gida tayi ya amsa da lafiya ba tare daya k'ara kallon ta ba, shiru duk sukai tana murmushi idon ta akan shi can ta k'ara cewa "an gode da abubuwan Alkhairi Allah ubangiji ya k'ara girma da daukaka" slowly ya furta "Ameen" ta d'an kalli Fauzy dake d'an murmushi itama shine akan fuskar tata, shiru duk sukai parlon sai kace ba mutane Aunty Mareeya sai d'an kai idon ta take tana kallon shi acikin ranta ta shiga tuno da ranar data fara ganin shi da suka zo Abuja bata ta6a zaton akwai ranar da zasu zauna haka da shi bama balle ta kai ga zancen Auren k'anwarta, mik'ewa tay tayi ma Fauzy alamar ta biyo ta da hannu ta mik'e saida ta kalleshi tace mashi tana zuwa ya d'aga mata kai, wurin dining suka nufa Aunty ta nuna mata kayan abinci dake sama k'asa k'asa da murya tace "gashi nan sai ki mashi magana yazo ki serving nashi" kai Fauzy ta d'aga idon ta akan jigunannun Warmers d'in da aka jera a saman table d'in set biyu babba da k'arama set d'aya na Aunty ne ta san su d'ayan kuma sam bata san Aunty dasu ba a ranta ta raya k'ilan duk na chef d'inne amman sun had'u ba k'arya, bubbud'e mata su ta shiga yi babba d'aya farar shinkafa ce washarr washar gata zak'o zak'o sai k'aramar warmer d'inta tana bud'e ta wani irin kamshi mai dadi ne ya karad'e wurin vegetable soup ce gwanin kyau a ido ingredients d'inta an yanka su manya manya taji hanta, d'ayar babbar Warmer d'in kuma fried spaghetti ce tayi brown gwanin burgewa itama sai faman zuba k'amshin spices take gashi tasha vegetables su tsanwan tattasai Karas koran wake da dai sauran su gashi tasha nama ca6a ca6a, d'ayar warmer d'in ta k'arshe kuma pepper chicken ne ciki, bayan ta gama bubbud'a mata tace mata akwae coleslaw a cikin Fridge,
"Amman Aunty duka order d'in nasu kikai?" Fauzy ta tambaya k'asa k'asa,
"eh mana daga lokacin da kika fad'i man zai zo zuwa yanzu ina zan iya yin wani lafiyayyen Abinci har gara ma spaghetti za'a iya yi amman kuma ba komai nike da shi ba na kayan had'ata tayi kyau haka, kai Fauzy ta jinjina tace hakane, "amman ai sun yi haka ko?" da sauri Fauzy tace "ah sosae ma kin yi mana dubara naji dad'i wllh" yar dariya Aunty tay tace "jin dad'in ki your excellency shine nawa" hannu Fauzy ta kai ta gumtse dariya,
"Yanzu kije ki mashi magana yazo ya ci" kai Fauzy ta d'aga sai kuma tace "Allah ma yasa ba wahalar banza akai ba ta tanadar su don yana iya k'in ci wllh" da sauri Aunty Mareeya tace "in ya ki ci ai ke zaki sashi dole yaci ko, taya zai tako yazo kuma yace bazai ci komai ba ke kuma ki bishi da ido, anya Fauziyya, gaba d'aya wani lokacin sai ki kaman ba wayyaya ba wllh na lura kaman baki iya soyayya ba ko dai kin k'arar da ita a wurin shashasha d'in can, kije ki mashi magana in ya nuna bazai ci ba kice baki yarda ba sai ya ci a cikin sigar yar shagwaba shagwaba zaki mashi magana dole fa sai kin zage damtse wllh ke ce zaki koya mashi sakin jiki da mutane bama kamar ke in ba haka ba yana a haka d'in can wllh kece Masha wuya ki ga fa yadda magana ke mashi mugun wahala ga ba sakin fuska don ma dai d'aurewar na mashi kyau tunda kyakkyawan ne....kinga an bar shi shi kad'ai jeki ki mashi magana bari in d'aukko coleslaw d'in akwai ma lemuna a cikin Fridge d'in sai ki tambayi wanda yake so in kuma sai giyar da kika ce yana sha sai kije ki nemo mashi" gwalo ido Fauzy tay jin Maganar tata ta k'arshe Auntyn ta sa dariya ta juya tana fad'in taje, komawa tayi cikin parlon Sameer d'in nata latsa waya har zata zauna a inda ta tashi sai kuma ta tuna da hud'ubar Aunty a d'arare ta nufi inda yake a hankali ta zauna daga gefen shi, idonta akan shi tace "am sorry an bar ka kai kadai naje yin abu ne" kai ya jinjina mata ba tare daya kalleta ba,
"Muje ka ci Abinci" d'an jimm yay kafin ya juyo suka had'a ido tana mashi murmushi, kokarin mik'ewa ta fara taji yace mata ya k'oshi hakan yasa ta koma ta zauna,
"Amman ya zaka ce ka k'oshi bayan nan kazo dole ai kaji yunwa" d'an girgiza mata kai yay yace ba nan ya fara zuwa ba so ya ci Abinci a inda ya sauka, tambayar shi tay a ina ya sauka ya bata amsa da Government House, marairaice mashi fuska tay tace "to amman dai ai nan ma yakamata kaci Abinci tunda nasan Saboda n...." Kasa k'arasa Maganar tay idon shi a kanta slowly yace yana jin ta alamar taci gaba, kikkafta idanu ta shiga yi tana motsa baki ganin irin kallon da yake mata ne yasa da k'yar ta furta "Saboda ni ka zo" kawai sai gani tay yay d'an murmushin gefe wanda tunda yazo bai yi kamar shi ba don har gefen fuskar tashi ya d'an lotsa, d'age mata gira yay yace "Who told you dat?" shiru tay tana cigaba da kikkafta ido taji ya sake cewa ba tambayar ta yayi ba,
"Ba kowa, ni nayi tunanin hakan" shiru yay yana kallon ta cikin k'arfin hali ta furta "hakane?" wani kalan motsa baki yay tare da yi mata wani kallo yace in ta cancanci hakan to hakane, faffad'an murmushi tayi tace "eh nayi deserving hakan" d'an ta6e baki yay da alamun murmushi yace a matsayinta na wa ba tare da jin wani d'ar ba ta furta "Your wife to be in sha Allah" bin ta yay kawai da ido sai murmushi take tana niyyar k'ara yin magana Mijin Aunty Mareeya ya sawo kai cikin parlon da sallama su Hanif na biye da shi gaba d'aya suka kai idon su akan shi ganin shine yasa Fauzy saurin sauke kanta don sai taji kunyar zamanta a kujera d'aya da Sameer ta kamata, inda suke ya nufo yana zuwa gaban Sameer cikin sakin fuska ya bashi hannu suka gaisa yayi mashi an zo lafiya nan ma ya amsa mashi, d'an rankwafawa Hanif yayi yace mashi ina wuni ganin haka yasa su sultan ma suka yi duk ya amsa masu fuskar shi a d'an sake, juyawa Abban Hanif yay bayan sun gama gaisawar ya nufi hanyar Bedroom su Hanif na biye dashi gaba d'ayan su Uniform ne ajikinsu sun goya School bag da gani daga Makaranta ya d'aukko su ,
"Pls muje kaci Abincin" Fauzy ta fad'a da yar sigar shagwaba idon shi akanta yay shiru, mikewa tayi tana mashi wani kallo a kokarin ta na tayi abunda Aunty tace, shiru ya d'an yi kafin yace shi bai cin Abinci in ya riga ya koshi ya fad'a mata ya riga ya ci so ba sai yaci wannan ba, tsaye tayi tana kallon shi bayan ya gama yin Maganar shima kallon nata yake can ta nufi kujerar gefen shi ta zauna ta maida fuskarta tana kallon gefe,