Sashe 203
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
105
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
......... Alhamdulillah Allah yayi mun gama zagaya ko ina sai yaba gidan ake ana an dai kashe kuɗi, cike da tsokana Dad ɗin su Haisam wato Mr President yace mashi anya bazai sa EFCC su bincike shi ba don an kashe ma gidan kuɗi da yawa duk akai dariya Hajiya tace in an tashi bincikar tashi sai a haɗa dashi tunda ai shine ƙarfin nashi, Dad ɗin na yar dariya yace shi ai gida kawai yasan ya bashi amman ba hannunshi a wannan uban kayan daya zuba ma gidan Hajiyar tace aikuwa shike da hannu tunda ai shiya biya mashi yaje yayi karatun fasahar da yake samun kuɗi duk akayi dariya harda Security dake biye dasu, itama Mom yaba ma Jidderh tayi tace bata san kamfaninta sun ƙware haka ba sai yanzu gaba ɗayan kayan da aka zuba ma gidan sun hau kuma sunyi kyau nan fa duk aka shiga yaba mata tanata dariyar jin daɗi haka mijinta Sadeeq shima yaji daɗin yabon nata da ake Dad ɗin su har yana cewa zai bata kwangilar zuba ma gidan su kaya in ya sauka zasu koma, cike da jin daɗi tayi mashi godiya Aunty ma tace zata rinƙa samo mata kwangila kuwa tunda sun ƙware haka Hajiya Zainab ma itama tace zata rinƙa samo mata dama harda ita aka zo don yanzu sunfi zama a Abuja bayan an ba Dad ɗinsu Sameer Minister, Fauzy dai basu ƙasar kuma har yanzu bata sake haihuwa ba itama don Sameer yace sai ta huta sosae ba kamar daya ga Cs aka yi mata, ganin Dad ɗinsu na niyyar tafiya yasa Haisam ce mashi please ya bari suci abinci ya ɗan buɗa mashi ido kafin yace ai baya jin yunwa Jidderh dake murmushi tace ai na murnar sabon gida ne ya kamata yaci yana murmushi yace to tunda hakane a bashi ya tafi da abunshi duk akayi dariya dama ya iya barkwanci, Fanan ce ta nufi cikin gidan da sauri dama sunyi Order ɗin abinciccika saboda masu rako su sabon gidan, bada jimawa ba ta fito ruƙe da manyan ledoji guda biyu ta nufo shi dasu, har rige rigen amsa muƙarrabanshi daya zo dasu suke amman sai yace masu su bari shi zai ruƙe abunshi don kada wani ya cinye mashi aikuwa mi za'ai ba dariya ba kuma shi ɗin ya kar6i abun shi anata ya kawo don Allah a ruƙe ya ƙi badawa, Addu'o'i yayi masu na Allah ya sanya alkhairi yasa sun dawo a sa'a ya karesu daga dukkan sharri anata amsawa daga baya sukai sallama aka buɗe mashi mota duk sauran abokan tafiyar nashi suma suka shiga motocin saida aka ga tafiyar su sannan suka koma cikin gidan harda su Mom, a falo aka zazzauna zaman cin abincin abun gwanin sha'awa su Mom sai kace ba First lady ba sun saki jiki cikin yan uwa ana ta cin abinci ana hirar nishaɗi. Sai gab da Magrib Fatuu ta iso Haisam yaje ɗaukkota tasha gayun doguwar rigar shadda, tun a bakin gate ɗin gidan ta fara sakin baki don itama ba sanin gidan tayi ba ta dai san shi a hoto, lokacin su Mom duk sun tafi sai su Mino da Aysha da kuma Jidderh da suka tsaya su tarbeta, sosae aka nuna farincikin dawowarta bama kamar su twins, Esha tana ganinta ta ƙanƙameta tana mata welcome tare da nuna mata sabon gidan su, sam Fatuu ta kasa 6oye al'ajabinta da kuma farincikin gidan sai faman bin gidan take da kallo idanu waje tana kuma sakin murmushi duk a lokaci guda, zagayawa suka shiga yi da ita harda Fanan Haisam kuma ya tafi Masallaci, bayan sun gama ganin ko ina ciki suka dawo don yin salla, sosae Fatuu tayi godiya ga Allah da yadda yake ta mata ni'imomi da bata ta6a zaton samu ba a rayuwarta, harda kukan daɗinta sannan tayi ma Mijinta Addu'o'i sosae shima, bayan sallar isha aka zo ɗaukar su Mino anata mata Addu'ar Allah ya raba ta da cikinta lafiya haka Aysha amarya ma ba'a daɗe da ɗaukar Mino ba itama angonta Na'eem yazo ya ɗauketa, Jidderh ce ta ƙarshe da aka ɗauka duk saida mazajen nasu sukai ma Fatuu Allah ya sanya alkhairi kafin su tafi don ɗazun da suka zo bata nan, bayan Haisam ya dawo a tare gaba ɗaya suka zauna cin abinci a dining area fuskokin kowannensu cike take da annuri, bayan sun gama cin abincin ne Haisam yace suyi alwala suyi Nafila duk suka ce to harda yaran, anan babban falon sukayi sallar raka'a biyu ta godiya ga Allah bayan sun gama kowa yayi addu'a Esha tana yi tana dariya tana leƙen fuskokin su twins, a falo suka zauna nan Fatuu tayi ma Haisam ɗin godiya da Addu'oin Allah ya ƙara mashi lafiya da arzuƙi mai amfani harda su Fanan dasu Esha ake amsawa, kallo suka yi zuwa ƙarfe tara da rabi Haisam yace ma su twins suje ya rakasu su kwanta aikuwa Esha na jin haka ta fara tura baki tana ƙunƙunin ita ba'a yi mata ɗaki ba a saka mata ɗan gadonta itama duk sukai dariya Fatuu tace ita dake da ma ɗakuna har biyu ga ɗayan na part ɗinta ga kuma na Momynta sai inda take so zata kwana ta tura baki tace ai duk gadon sun mata ƙato ita kalar nasu twins take so, Haisam dake a tsaye yana murmushi yace mata tayi haƙuri in ta samu sister sai ayi masu ɗakinsu suma su biyu ta wani yarfa hannu tace to ba Aunty da Momyn suƙi su haihu ba tayi ƙanwa duk sukai dariya, jawota Fanan tayi jikinta tana bata haƙuri tace bada daɗewa ba zata yi ƙanwa da Aunty ta gama karatu,
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
......... Alhamdulillah Allah yayi mun gama zagaya ko ina sai yaba gidan ake ana an dai kashe kuɗi, cike da tsokana Dad ɗin su Haisam wato Mr President yace mashi anya bazai sa EFCC su bincike shi ba don an kashe ma gidan kuɗi da yawa duk akai dariya Hajiya tace in an tashi bincikar tashi sai a haɗa dashi tunda ai shine ƙarfin nashi, Dad ɗin na yar dariya yace shi ai gida kawai yasan ya bashi amman ba hannunshi a wannan uban kayan daya zuba ma gidan Hajiyar tace aikuwa shike da hannu tunda ai shiya biya mashi yaje yayi karatun fasahar da yake samun kuɗi duk akayi dariya harda Security dake biye dasu, itama Mom yaba ma Jidderh tayi tace bata san kamfaninta sun ƙware haka ba sai yanzu gaba ɗayan kayan da aka zuba ma gidan sun hau kuma sunyi kyau nan fa duk aka shiga yaba mata tanata dariyar jin daɗi haka mijinta Sadeeq shima yaji daɗin yabon nata da ake Dad ɗin su har yana cewa zai bata kwangilar zuba ma gidan su kaya in ya sauka zasu koma, cike da jin daɗi tayi mashi godiya Aunty ma tace zata rinƙa samo mata kwangila kuwa tunda sun ƙware haka Hajiya Zainab ma itama tace zata rinƙa samo mata dama harda ita aka zo don yanzu sunfi zama a Abuja bayan an ba Dad ɗinsu Sameer Minister, Fauzy dai basu ƙasar kuma har yanzu bata sake haihuwa ba itama don Sameer yace sai ta huta sosae ba kamar daya ga Cs aka yi mata, ganin Dad ɗinsu na niyyar tafiya yasa Haisam ce mashi please ya bari suci abinci ya ɗan buɗa mashi ido kafin yace ai baya jin yunwa Jidderh dake murmushi tace ai na murnar sabon gida ne ya kamata yaci yana murmushi yace to tunda hakane a bashi ya tafi da abunshi duk akayi dariya dama ya iya barkwanci, Fanan ce ta nufi cikin gidan da sauri dama sunyi Order ɗin abinciccika saboda masu rako su sabon gidan, bada jimawa ba ta fito ruƙe da manyan ledoji guda biyu ta nufo shi dasu, har rige rigen amsa muƙarrabanshi daya zo dasu suke amman sai yace masu su bari shi zai ruƙe abunshi don kada wani ya cinye mashi aikuwa mi za'ai ba dariya ba kuma shi ɗin ya kar6i abun shi anata ya kawo don Allah a ruƙe ya ƙi badawa, Addu'o'i yayi masu na Allah ya sanya alkhairi yasa sun dawo a sa'a ya karesu daga dukkan sharri anata amsawa daga baya sukai sallama aka buɗe mashi mota duk sauran abokan tafiyar nashi suma suka shiga motocin saida aka ga tafiyar su sannan suka koma cikin gidan harda su Mom, a falo aka zazzauna zaman cin abincin abun gwanin sha'awa su Mom sai kace ba First lady ba sun saki jiki cikin yan uwa ana ta cin abinci ana hirar nishaɗi. Sai gab da Magrib Fatuu ta iso Haisam yaje ɗaukkota tasha gayun doguwar rigar shadda, tun a bakin gate ɗin gidan ta fara sakin baki don itama ba sanin gidan tayi ba ta dai san shi a hoto, lokacin su Mom duk sun tafi sai su Mino da Aysha da kuma Jidderh da suka tsaya su tarbeta, sosae aka nuna farincikin dawowarta bama kamar su twins, Esha tana ganinta ta ƙanƙameta tana mata welcome tare da nuna mata sabon gidan su, sam Fatuu ta kasa 6oye al'ajabinta da kuma farincikin gidan sai faman bin gidan take da kallo idanu waje tana kuma sakin murmushi duk a lokaci guda, zagayawa suka shiga yi da ita harda Fanan Haisam kuma ya tafi Masallaci, bayan sun gama ganin ko ina ciki suka dawo don yin salla, sosae Fatuu tayi godiya ga Allah da yadda yake ta mata ni'imomi da bata ta6a zaton samu ba a rayuwarta, harda kukan daɗinta sannan tayi ma Mijinta Addu'o'i sosae shima, bayan sallar isha aka zo ɗaukar su Mino anata mata Addu'ar Allah ya raba ta da cikinta lafiya haka Aysha amarya ma ba'a daɗe da ɗaukar Mino ba itama angonta Na'eem yazo ya ɗauketa, Jidderh ce ta ƙarshe da aka ɗauka duk saida mazajen nasu sukai ma Fatuu Allah ya sanya alkhairi kafin su tafi don ɗazun da suka zo bata nan, bayan Haisam ya dawo a tare gaba ɗaya suka zauna cin abinci a dining area fuskokin kowannensu cike take da annuri, bayan sun gama cin abincin ne Haisam yace suyi alwala suyi Nafila duk suka ce to harda yaran, anan babban falon sukayi sallar raka'a biyu ta godiya ga Allah bayan sun gama kowa yayi addu'a Esha tana yi tana dariya tana leƙen fuskokin su twins, a falo suka zauna nan Fatuu tayi ma Haisam ɗin godiya da Addu'oin Allah ya ƙara mashi lafiya da arzuƙi mai amfani harda su Fanan dasu Esha ake amsawa, kallo suka yi zuwa ƙarfe tara da rabi Haisam yace ma su twins suje ya rakasu su kwanta aikuwa Esha na jin haka ta fara tura baki tana ƙunƙunin ita ba'a yi mata ɗaki ba a saka mata ɗan gadonta itama duk sukai dariya Fatuu tace ita dake da ma ɗakuna har biyu ga ɗayan na part ɗinta ga kuma na Momynta sai inda take so zata kwana ta tura baki tace ai duk gadon sun mata ƙato ita kalar nasu twins take so, Haisam dake a tsaye yana murmushi yace mata tayi haƙuri in ta samu sister sai ayi masu ɗakinsu suma su biyu ta wani yarfa hannu tace to ba Aunty da Momyn suƙi su haihu ba tayi ƙanwa duk sukai dariya, jawota Fanan tayi jikinta tana bata haƙuri tace bada daɗewa ba zata yi ƙanwa da Aunty ta gama karatu,