Sashe 69
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read
"Rabu dashi bazaki je ba, da da babu ke wake had'a mashi bashi ke had'a kayan shi ba, duk da abu ne mai kyau amman ai yasan halin da kike ciki ko" kallon ta Fatuu tay tana d'an kikkafta ido a hankali tace mata ai lafiyar ta lau bata jin komai, yar harararta Hajiyar tay "dama ai ba'a ce baki lafiya ba ko saidai gudun janyo ciwon ake" da sauri Fatun ta juyar da fuskar ta, d'an murmushi Hajiya tay tace mata taje taci gaba da kallonta bazata hau bene ba a halin da take ciki in dole sai ita yake so ta had'a mashi kayan tace ya kawo nan sai ta tayata su had'a mashi, jiki sukuku Fatuu ta mik'e ta nufi hanyar fita ta koma parlor, idanunta ne suka ciko da kwalla ta zauna tay shiru. Bayan sallar isha Haisam yazo dubata kaman ko yaushe lokacin tana a cikin Bedroom zaune a saman gado, ya lura da yanayin ta cike da kulawa ya tambayi mike damunta kawai sai ta saka mashi kuka tace ba shine zai tafi ba, rarrashinta ya shiga yi da k'yar ya samu tayi shiru daga baya ya tafi, bayan tafiyar shi cigaba da matse kwalla tay wani irin k'unci take ji acikin ranta, tunani ta shiga yi na ko in Hajiya tayi bacci ta tafi wurin shi don shi kan shi ta fahimci yana son hakan kawai ba yadda zai yi ne, to kuma in ta farka fa don tabbas Hajiyar na tashi da daddare wani lokacin toilet take zuwa kuma bata da nauyin bacci don sau da yawa in Fatun ta farka ko zata toilet data ji motsinta ita ke kunna lamp har ta tambaye ta lafiya, tasan muddin ta tafi da k'yar in bata farka ba taga bata a d'akin hakan kuma itama tasan zai ja masu matsala, sak'e sak'e ta ci gaba da yi bayan zuciyarta ta raya mata wanccan tunanin tana haka kawai sai wani abu yazo mata a rai lokaci guda ta hau jinjina kai alamar ta samu mafita, saida ta kai idonta kan k'opar shigowa tay d'an jimm kafin ta kai hannunta gefe da sauri ta d'auki wayarta ta shiga call log, layin Nameer ta shiga kira bugu biyu ya d'auka ya furta "Yayata ta kaina" bata ce komai ba kan hakan k'asa k'asa da murya tana yi tana kallon kopar ta tambayi yana ina, ce mata yay bai nan yana cikin gari ta tambayi yaushe zai dawo gida yace d'an anjima, jin tayi shiru yasa shi ce mata in da wani abu ta fad'i mashi ko tana son wani abu ne,
"Eh, don Allah akwae wani magani ne da nike son ka siyo man zan turo maka sunan shi saidae ni yanzu nike son shi gashi kuma kace sai d'an anjima zaka dawo" sai zare ido take tana kallon k'opa tay Maganar, da sauri yace mata ba matsala ai sai yazo ya kawo mata dama a kusa da inda yake akwae babban pharmacy, jin hakan har saida ta d'an yi murmushi tace to bari ta turo mashi, da sauri ta cire wayar daga kan kunnan ta hannunta har yar rawa yake ta fara k'ok'arin tura mashi sak'on sunan Maganin, bayan ta tura zuciyarta ta raya mata yanzu in ya kawo kuma Hajiya na zaune a parlor kuma ya bata fa gashi ansan ba kowanne magani take sha ba sannan tace mata na miye, wani irin bugu gabanta yay da sauri ta zuru da k'afafunta cikin sand'a ta nufi k'opar, a hankali ta d'an lek'a cikin parlon ta hango Hajiyar zaune da Aunty, wani irin waro ido Fatuu tay baki bud'e da sauri ta dawo cikin d'akin, can k'arshen gadon ta koma sosae hannuwanta ke rawa ta shiga sake kiran Nameer duk bugu d'aya tare yake da fad'uwar gabanta, har ta yanke bai d'auka ba a rud'e ta hau sake kiran nashi can k'asan mak'oshi take furta don Allah kayi picking Nameer, saida ta kusa yankewa sannan ya d'auka yace "Sorry Yayata ina cikin pharmacy d'in ne amman gashi nan na siyo yanzu zan kawo maki da sauri cikin rawar murya idanunta akan k'opa tsoronta kada Aunty d'in ta shigo dubata tace "N...namer..r ka gane, don Allah ban son asan da maganin kada ka bari kowa ya gani" d'an jimm yay sai kuma ya tambayeta amman to maganin miye, gabanta ne ya fad'i cikin yar in ina tace mashi maganin bacci ne saboda halin da take ciki bata samun isasshen bacci shine take so tasha ko tayi baccin amman in aka gani za'a iya hanata sha tunda ba kowanne magani take sha ba amman shi wannan baida wata illa zata iya sha, ce mata yay ta tabbatar dai bazai mata komai ba da sauri tace mashi eh wllh ai yasan dai bazata sha abun da zai mata illa ba yace Ok kada ta damu bazai bari kowa ya gani ba gashi nan zuwa, wani irin sanyi ta ji a ranta ta koma ta haye saman gadon, dama Aunty shigowa tay su gaisa da Hajiya bayan sun gama gaisawar ta tambayi ya mai bed rest Hajiya ta d'an ta6e baki tace tana cikin d'aki tana ta nukurci miji zai tafi, murmushi Aunty tay tayi mata sai da safe,
"Eh, don Allah akwae wani magani ne da nike son ka siyo man zan turo maka sunan shi saidae ni yanzu nike son shi gashi kuma kace sai d'an anjima zaka dawo" sai zare ido take tana kallon k'opa tay Maganar, da sauri yace mata ba matsala ai sai yazo ya kawo mata dama a kusa da inda yake akwae babban pharmacy, jin hakan har saida ta d'an yi murmushi tace to bari ta turo mashi, da sauri ta cire wayar daga kan kunnan ta hannunta har yar rawa yake ta fara k'ok'arin tura mashi sak'on sunan Maganin, bayan ta tura zuciyarta ta raya mata yanzu in ya kawo kuma Hajiya na zaune a parlor kuma ya bata fa gashi ansan ba kowanne magani take sha ba sannan tace mata na miye, wani irin bugu gabanta yay da sauri ta zuru da k'afafunta cikin sand'a ta nufi k'opar, a hankali ta d'an lek'a cikin parlon ta hango Hajiyar zaune da Aunty, wani irin waro ido Fatuu tay baki bud'e da sauri ta dawo cikin d'akin, can k'arshen gadon ta koma sosae hannuwanta ke rawa ta shiga sake kiran Nameer duk bugu d'aya tare yake da fad'uwar gabanta, har ta yanke bai d'auka ba a rud'e ta hau sake kiran nashi can k'asan mak'oshi take furta don Allah kayi picking Nameer, saida ta kusa yankewa sannan ya d'auka yace "Sorry Yayata ina cikin pharmacy d'in ne amman gashi nan na siyo yanzu zan kawo maki da sauri cikin rawar murya idanunta akan k'opa tsoronta kada Aunty d'in ta shigo dubata tace "N...namer..r ka gane, don Allah ban son asan da maganin kada ka bari kowa ya gani" d'an jimm yay sai kuma ya tambayeta amman to maganin miye, gabanta ne ya fad'i cikin yar in ina tace mashi maganin bacci ne saboda halin da take ciki bata samun isasshen bacci shine take so tasha ko tayi baccin amman in aka gani za'a iya hanata sha tunda ba kowanne magani take sha ba amman shi wannan baida wata illa zata iya sha, ce mata yay ta tabbatar dai bazai mata komai ba da sauri tace mashi eh wllh ai yasan dai bazata sha abun da zai mata illa ba yace Ok kada ta damu bazai bari kowa ya gani ba gashi nan zuwa, wani irin sanyi ta ji a ranta ta koma ta haye saman gadon, dama Aunty shigowa tay su gaisa da Hajiya bayan sun gama gaisawar ta tambayi ya mai bed rest Hajiya ta d'an ta6e baki tace tana cikin d'aki tana ta nukurci miji zai tafi, murmushi Aunty tay tayi mata sai da safe,