Sashe 84
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
A kwana a tashi ba wuya har sati ukkun da Haisam yace zai dawo sun yi, tun ana gobe zai dawo Fatuu ke ta farinciki har Fuskarta ta kasa boyewa ranar ta kasance Juma'a Tk na d'aukko ta daga makaranta ita da Mino suka wuce kasuwa siyayyar kayan da zata mashi Abinci, Washe gari da wuri ta tashi ta hau shirin tarbar mai gida, anan part d'inta ta fad'i ma Hajiya za'ai abinci gaba d'aya hakan yasa Saude zuwa nan suka shiga Kitchen tare Mino kuma ta hau gyaran part d'in Tk kuma aka sa ya gyara harabar part d'in, zuwa sallar Azahar sun gama komai sai uban k'amshin girkin da sukai kala ukku ke tashi drinks ma kala ukku sukai harda lafiyayyen kunun Aya sannan sunyi had'addan tsiren hanta da grilled lamp daya gasu ya sha vegetables nad'e a cikin foil paper, bayan sun gama komai aka zuba na su Hajiya Saude ta tafi dashi Mino ma ta zuba mata wanda zata kai ma gwaggo tace ta shiryo daga nan zasu je d'aukko shi Airport a d'okance tace to ta tafi, tana shiga Bedroom ta fad'a toilet bata d'au lokaci ba ta fito don tafi son jirginsu yay landing suna a Airport d'in, shiryawa ta shiga yi tayi make up wadda rabon data yi irinta ta manta saidai ko wadda akayi mata da bikin ta, tana cikin yin shafar Haisam d'in ya kirata ya sanar mata gasu zasu taso daga Kano cike da zumud'i tace to tay mashi fatan isowa lafiya, shaf shaf ta k'arasa don tasan bada jimawa ba zasu iso, wata rantsattsar marron d'in shadda sabuwa dal a cikin kayan lefenta take tasha ubansun aiki ta fiddo, ba 6ata lokaci ta saka ta tayi d'aurin kallabi mai kyau ta fiddo jewellery da suka hau da kayan ta saka harda hannunta tasa Agogo da zobuna ita kanta taga kyaun da tayi data kalli Madubin, jaka da takalma da gyale ta fiddo wanda suka hau da aikin shaddar ta saka sosae tay kyau ga cikinta ya fito, tana gamawa ta kira Tk tace mashi sun kusa k'arasowa yace Ok su a had'u a parking space, lokacin data fito har ya fiddo Motar cikin harabar yana hangota ya tunkarota da Motar bayan ya tsaya ta bud'e baya ta shiga yaja suka tafi, a kan hanya suka had'u da Mino itama tayi wanka tayi kwalliya tana sanye da riga da skirt na blue lace ta yafa blue d'in gyale bakinta yasha jan jambaki sosae itama tayi kyau, gaban Motar ta bud'e ta shiga suka tafi. Basu fi minti biyu ba da zuwa jirgin su Haisam d'in ya sauka gaba d'aya Fatuu a k'agare take data gan shi don ba K'aramin missing d'in shi tay ba, gaba d'aya sun baza ido suna kallon masu shigowa can sai gashi ya shigo yana janye da trolley d'ayan hannun shi ruk'e da jakar laptop jikin shi sanye da bak'ak'en riga da wando ya d'aura jar coat, Fatuu na hango shi ta tafi da gudu har saida tasa hankalin shi ya d'an tashi ganin yadda ta nufo shi gashi takalman k'afarta half cover ne masu d'an tsini, da sauri ya saki akwatin itama jakar laptop d'in ya ajeta k'asa ya nufota da sauri yana fad'in ta tsaya tare da yi mata nuni da hannu amman ina ai saida ta k'araso tana niyyar fad'a mashi ya ruk'eta yana murmushi ita kuma ta washe baki gaba d'aya k'amshin jikin shi ya karad'e wurin, ce mata yay miyasa tasan halin da take ciki zatai gudu haka bata ce mashi komai ba sai faman dariyar farinciki take duk hankalin mutane ya dawo kan su, k'arasowa wurin su Mino da Tk sukai suna murmushi sukai mashi sannu da zuwa fuskar shi a sake ya amsa masu, kama trolley d'in Tk yay Mino kuma ta d'auki jakar laptop d'in ya tallabo kafad'ar Fatun gwanin sha'awa suka nufi barin wurin idonta akan shi sai faffad'an murmushi take shima haka, sosae yaga ta canza mashi kan yadda yake ganinta a Vedio call, inda Motar su take suka nufa ita dashi suka shiga baya Mino ta zauna a gaba suka tafi, kwantar da kanta tayi a saman shoulder d'in shi tana ta bashi labarai harda koya mata Motar da ake yana ta jinjina kai fuskar shi d'auke da Murmushi a haka har suka k'araso Unguwar su, a gida Mino tasa aka ajeta tayi ma Haisam Allah ya huta gajiya sukai sallama da Fatuu sannan suka wuce.
Kwana ukku da dawowar shi ya tafi Abuja hidimar bikin Saleem Fatuu ji tay kamar ta bishi saidai Saboda makaranta ta hak'ura Saboda yanzu karatun suke da zafi zafi Saboda shekarar k'arshe ce. Ranar Friday aka d'aura ma Saleem aure da amaryar shi Saleema wadda d'iyar Minister of Health ce sai fatan Allah ya sanya Alkhairi ya bada zaman lafiya da zuria dayyiba, Ranar Sunday Haisam ya dawo Katsina.
Bayan sati biyu.......
Ranar Friday Fauzy ta dawo Weekend gidan Aunty Mareeya kamar yadda ta saba, da yamma tana kwance akan gadonta cikin d'akinta tana lallatsa wayar ta, jin an turo k'opa yasa ta juyo taga Aunty Mareeya ce ta shigo tana sanye da riga da skirt na jan lace kanta ta d'aura kallabi daga baya ta lankwasa igiyoyin kitson ta Sosae kayan suka amshi jikinta sun bayyanar da k'irarta ta dirarrar giant d'in mace, gadon ta nufo hannunta ruk'e da wayarta ta zauna a baki idon ta akan Fauzy, ganin irin kallon da take mata ga yanayin fuskarta kamar da alamun tashin hankali ko kuma ace Al'ajabi yasa Fauzy tashi zaune itama riga da skirt d'in atamfa ne a jikinta kanta ba kallabi anyi mata kitso shuku jelar ta sauka k'asa,
"Aunty lafiya?" Fauzy ta tambaya ta d'an waro ido da alamun fargaba akan fuskar ta, ajiyar zuciya Aunty ta sauke ta d'an motsa baki tama rasa ta ina zata fara, hakan da tayi yasa hankalin Fauzy tashi tace "Aunty don Allah minene, ki fad'i man kin ji" wata ajiyar zuciyar ta sake saukewa ta yarfa hannu tace "to ai Fauziyya nama rasa ta ina ne zan fara tsabar mamaki wllh" da sauri tace mata mi akai,
"Dama kun fara soyayya ke da Sameer ne baki fad'i man ba?" da mamaki Fauzy ta furta
"Soyayya!" Kai Aunty Mareeya ta d'aga mata, girgiza kai ta hau yi "a'a wllh, ni ba wata soyayya da muke yi duk yadda muke da shi ai kin sani ko daga haka ba wani abu" shiru Aunty tay duk tayi zuru zuru,
"Amman Aunty miyasa kika ce haka?" Hannu ta kai ta ruk'e ha6a tace "Wai kinsan yanzu Baba ya kira ni da alamun tashin hankali yake tambayata wai wane yaro ne kike tare dashi basu sani ba kuma Sameer ne yake magana akai"
zaro ido Fauzy tay ba shiri ta gyara zama Aunty taci gaba "Wai kiran shi akai daga gidan gwamnatin Nasarawa kan ya bada rana za'a zo neman Auren ki kuma harda rana za'a saka" tun kafin ta k'arasa Fauzy ta k'ara zaro ido ta bud'e baki Aunty tace "Wllh, ke duk yadda nike fatan hakan baki ji yadda hankali na ya tashi ba don ban tsammaci abun haka ba" gaba d'aya bakin Fauzy ya mutu sai ido kawai sosae taji Al'ajabin Maganar don ita an fi sati ma ko ta WhatsApp basu yi magana da Sameer d'in ba, da k'yar ta iya cewa "Yanzu shi baban miya ce masu??" Aunty tace "wai ce masu yay don Allah su bashi lokaci zai kira su ya sanar masu don farko ma gardama masu yay kan bake bace saida aka tabbatar mashi ta hanyar yi mashi bayanin ki ya gasgata tabbas ke d'in shi shine ya kira ni yaji yadda abun yake baki ji yadda hankalin shi ya tashi ba bayan nayi mashi bayanin tsakanin ki da shi sosae yay mamaki" Fauzy ba baki sai ido kawai wani irin bugu k'irjinta yake mata sosae Al'amarin ya d'aure mata kai,
Kwana ukku da dawowar shi ya tafi Abuja hidimar bikin Saleem Fatuu ji tay kamar ta bishi saidai Saboda makaranta ta hak'ura Saboda yanzu karatun suke da zafi zafi Saboda shekarar k'arshe ce. Ranar Friday aka d'aura ma Saleem aure da amaryar shi Saleema wadda d'iyar Minister of Health ce sai fatan Allah ya sanya Alkhairi ya bada zaman lafiya da zuria dayyiba, Ranar Sunday Haisam ya dawo Katsina.
Bayan sati biyu.......
Ranar Friday Fauzy ta dawo Weekend gidan Aunty Mareeya kamar yadda ta saba, da yamma tana kwance akan gadonta cikin d'akinta tana lallatsa wayar ta, jin an turo k'opa yasa ta juyo taga Aunty Mareeya ce ta shigo tana sanye da riga da skirt na jan lace kanta ta d'aura kallabi daga baya ta lankwasa igiyoyin kitson ta Sosae kayan suka amshi jikinta sun bayyanar da k'irarta ta dirarrar giant d'in mace, gadon ta nufo hannunta ruk'e da wayarta ta zauna a baki idon ta akan Fauzy, ganin irin kallon da take mata ga yanayin fuskarta kamar da alamun tashin hankali ko kuma ace Al'ajabi yasa Fauzy tashi zaune itama riga da skirt d'in atamfa ne a jikinta kanta ba kallabi anyi mata kitso shuku jelar ta sauka k'asa,
"Aunty lafiya?" Fauzy ta tambaya ta d'an waro ido da alamun fargaba akan fuskar ta, ajiyar zuciya Aunty ta sauke ta d'an motsa baki tama rasa ta ina zata fara, hakan da tayi yasa hankalin Fauzy tashi tace "Aunty don Allah minene, ki fad'i man kin ji" wata ajiyar zuciyar ta sake saukewa ta yarfa hannu tace "to ai Fauziyya nama rasa ta ina ne zan fara tsabar mamaki wllh" da sauri tace mata mi akai,
"Dama kun fara soyayya ke da Sameer ne baki fad'i man ba?" da mamaki Fauzy ta furta
"Soyayya!" Kai Aunty Mareeya ta d'aga mata, girgiza kai ta hau yi "a'a wllh, ni ba wata soyayya da muke yi duk yadda muke da shi ai kin sani ko daga haka ba wani abu" shiru Aunty tay duk tayi zuru zuru,
"Amman Aunty miyasa kika ce haka?" Hannu ta kai ta ruk'e ha6a tace "Wai kinsan yanzu Baba ya kira ni da alamun tashin hankali yake tambayata wai wane yaro ne kike tare dashi basu sani ba kuma Sameer ne yake magana akai"
zaro ido Fauzy tay ba shiri ta gyara zama Aunty taci gaba "Wai kiran shi akai daga gidan gwamnatin Nasarawa kan ya bada rana za'a zo neman Auren ki kuma harda rana za'a saka" tun kafin ta k'arasa Fauzy ta k'ara zaro ido ta bud'e baki Aunty tace "Wllh, ke duk yadda nike fatan hakan baki ji yadda hankali na ya tashi ba don ban tsammaci abun haka ba" gaba d'aya bakin Fauzy ya mutu sai ido kawai sosae taji Al'ajabin Maganar don ita an fi sati ma ko ta WhatsApp basu yi magana da Sameer d'in ba, da k'yar ta iya cewa "Yanzu shi baban miya ce masu??" Aunty tace "wai ce masu yay don Allah su bashi lokaci zai kira su ya sanar masu don farko ma gardama masu yay kan bake bace saida aka tabbatar mashi ta hanyar yi mashi bayanin ki ya gasgata tabbas ke d'in shi shine ya kira ni yaji yadda abun yake baki ji yadda hankalin shi ya tashi ba bayan nayi mashi bayanin tsakanin ki da shi sosae yay mamaki" Fauzy ba baki sai ido kawai wani irin bugu k'irjinta yake mata sosae Al'amarin ya d'aure mata kai,