← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 124 OF 211

Sashe 124

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Kamar yadda Hajiya tace taje tayi ma Haulat d'in gaisuwa tare da Saude suka je bayan sun dawo ne tayi masu Aiken kayan abinci masu yawa, sosae Fatuu keta gyara kanta bayan Aunty ta aiko mata da magungunan Saude kuma ta samo mata mai tayata rainon su twins tare suke zuwa Makaranta da ita, sosae take missing d'in Haisam sai bayan wata d'aya da dawowar su sannan yazo suka shiga shan sabon Amarci lokacin ne yayi ma Sameer magana kan zuwa Funtua gaishe da iyayen Fauzy da yake yana a K'asar, ya amince zai je harda cewa jirgi zasu hau ko Haisam na dariya yace mashi ai ba Airport acan dole a Mota zasu anan suka tsaida Ranar da zasu Haisam ya fad'i ma Fatuu ita kuma ta kira Aunty Mareeya ta sanar mata aikuwa sosae taji dad'i tace dole zata je don a tarbesu yadda yakamata. Ana saura kwana biyu suje Haisam ya tafi Abuja don daga can zasu wuce Aunty kuma washe gari ta tafi Funtua, Ranar da zasu zo ta kama Asabar da wuri suka taho Mota biyu sukai d'aya wadda suke ciki driver na jan su sai kuma d'ayar ta security, gaba d'ayan su farar shadda ce a jikin su anyi masu kalar d'inkin da suka fi so sai baza k'amshi suke k'afafuwan su na sanye da dakakkun takalma haka agogunan hannunsu ba sai na fad'i masu tsada bane yau dai kawunan su sun samu Arzik'in huluna amman shi Sameer bai saka ba tana dai ajiye k'ilan sai sun isa zai saka, duk tafiyar ta fara gundurar Sameer don har Fuskar shi ta nuna tun yana yin shiru har takai ya fara tambayar driver ko sun kusa isa sai yace mashi da saura, Haisam daya lura ran shi ya fara 6aci yana murmushi yace mashi gara ya saba kafin Ranar d'aurin aure ai tun kafin ya rufe baki ya fara girgiza mashi kai yace bazai k'ara wannan tafiyar ba Haisam da still Murmushi yake yace to ya za'ai Ranar d'aurin auren fuska a tamke yace oho shidai bazai zo a Mota ba, lokacin da suka iso garin gaba d'aya ran Sameer ya gama 6aci Haisam ya fara bashi hak'uri yana nuna mashi ai sun iso ya yamutsa fuska yace to mi akai tunda zasu koma, Yaya Mubarak ya kira ya sanar da shi gasu sun shigo gari yace Ok yana fara mashi bayanin inda zasu nufo su had'e ya mik'a ma driver wayar yaci gaba da mashi bayani, sai faman bin garin Sameer yake da kallo haka Haisam ba laifi Sameer yaga ba k'auye bane kamar yadda ya zata, lokacin da suka had'e da Yaya Mubarak yana ganin Motocin ya gane sune yay ma driver d'in alamun ya tsaya, nufar Motocin yay da sauri aka sauke mashi glass cikin girmamawa ya gaishe dasu tare da yi masu sannu da zuwa Haisam ne ke amsawa shi kuwa Sameer tunda ya d'aga mashi kai sau d'aya bai k'ara ba balle ya tanka, bayan sun gama gaisawar yace ma driver d'in ya biyo shi a baya ya koma Motar shi suka tafi, lokacin da suka k'arasa anata aikin gyaran gidan don Kusan ma an kusa gamawa don an d'aura bene komai dai ya kusa kammaluwa, a falon Baban su aka sauke su wanda tuni an canza mashi fasali don shi yace ko angama ginin bazai hau sama ba dama kuma da k'asan aka fara gyaran, sosae aka nuna farincikin zuwan nasu duk samarin gidan da yan'uwan mahaifin nasu harda shi mahaifin nasu sun zo sun gaisa dasu sai basu girma ake ba laifi Sameer d'in ya d'an saki fuska amman kowa daya gan su yake gane shine wanda Fauziyya zata aura don sun san labarin shi, Aunty Mareeya na a falon tana gabatar masu dasu da kuma dangantakar su haka suma su Haisam d'in tana gabatar masu da dangin nasu nan aka shiga yi masu godiya yawanci dai Haisam ne ke magana, koda Aunty tayi masu Maganar Abinci cewa sukai a k'oshe suke sai da ta matsa masu sannan suka d'an ci wanda ta kawo masu kan c-table dama tasan ana iya yin hakan shiyasa basu wani yi Abinci masu yawa ba, bayan sun gama zama tayi tana k'ara yi masu sannu da zuwa da godiya ta lura da yanayin Sameer duk da tasan halin shi tana murmushi tace "K'ani na ansha gajiyar Mota ko" kallon Sameer d'in Haisam yayi yana murmushi shima ya d'an yi kad'an ba tare daya ce komai ba, basu yi awa da zuwa ba suka ce zasu tafi lokacin iyayensu sun dawo cikin parlon aka ce basu bari su k'ara hutawa Haisam yace Saboda hanya kada yamma tayi masu, godiya Haisam ya shiga yi masu na auren da aka basu sai lokacin Sameer ya bud'e baki yay godiyar shima duk suka ce ba komai ai sune da Godiya anata faman dawainiya dasu, a tare gaba d'aya aka fito yi masu rakiya harda Aunty da k'annansu mata harda masu aure da suka zo su Fareeda Mahaifiyarsu ce kawai bata fito ba amman har gwaggo ma ta fito rako su, har zasu shiga Mota Sameer ya dakata ya kira Yaya Mubarak da sauri ya nufo shi, magana yayi mashi saidai ni kaina banji mi yace mashi ba kawai dai sunga Yaya Mubarak d'in nata d'aga kai daga baya ya juya ya shige security ya rufe mashi k'opar anata d'aga masu hannu suka tafi, bayan tafiyar su cikin parlon suka koma gaba daya aka dasa hirar su Haisam d'in sai faman yaba kyaun su ake ana fad'in Fauziyya tayi dace ta ko ina Mijinta yayi k'anin mahaifin su ne yace saidai yaga kaman magana na mashi wahala ga Fauziyya da surutu ya kenan zasu yi zaman auren duk akayi dariya Aunty Mareeya tace haka yake amman in yaso yana d'an yi, Yaya Mubarak ne yayi masu bayanin kiran shi da yayi yace Maganar aikin da ake ne ya tambaye shi ko da matsala sannan ya tambaye shi anan akwae furniture masu kyau yace mashi eh to yanzu yace in aka k'arasa aikin aje a za6i wanda ake su da za'a saka a ko ina sai yayi mashi magana nan fa aka shiga fad'in Ma sha Allah wannan hidima haka abu yayi kyau saidai iyayen Fauzy sun ma kasa magana don Al'amarin ya girmi tunanin su, bayan su Aunty Mareeya da sauran yan gidan mata sun koma part d'in da aka ware masu suke zaune Saboda aikin da ake nan suka dasa hirar su Haisam kowa na fad'in wanda yafi mata wasu suce Haisam yafi burge su wasu suce dukkan su sun yi don suna kama ai sosae,

"Ni wllh wannan farin yafi burge ni da yanzu zai ce yana sona da gudu zan yarda ni koma matsayin mai aikin shi ce in dai zai aure ni" wata k'anwar su ce Nusaiba tayi Maganar dama ga yanayin Maganar ta kamar ta sakarkaru aikuwa gaba d'aya aka saka dariya Aunty Mareeya tafi kowa 6a66aka dariyar ta kai hannu ta bugi shoulder d'in ta tana fad'in "Su an Nusi Nusi anga fari rainon Madara da carpet an rud'e ko, wato in zai aure ki to kima fidda rai don wanccan da kike gani ya auru zuciyar shi a gark'ame take da k'aton kwad'o da Zarah ta rufeta da shi kima fidda rai don ba samu zaki ba" tura mata baki Nusaibar tayi tace kaji Aunty Mareeya da mugun fata tasan abun Allah itama yace yana sonta kamar yadda ya faru da Yaya Fauziyya, Mahaifiyar su da tunda suke abun su bata saka masu baki ba sai murmushi kawai tace "aikuwa Nusaiba koda ace hakan ta faru bazaki aure shi ba, baki ji ana fad'in ana barin halak ko don kunya ba kar ki manta matar shi fa itace silar duk wannan Alkhairan dake samun mu" Gwaggo tace gaskiya kam, tura baki Nusaibar tayi ta juyar da kai sai kace Haisam d'in yace yana son ta yadda tayin ne duk ya k'ara basu dariya,
Chapter 124 · 0% Book details