Sashe 167
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"To ko dai tana da wanda take so ta aura ne?" Gwaggo ta tambaya innar ta ɗan yi jimm kafin tace gaskiya bata tunani don har yanzu bata ga ta tsaya ma da wani ba tun bayan data gama takaba amman dai bari a kirata sai aji, Haulat na kwance a saman gado tun bayan data gama yin salla ta kwanta don tasa ummasalma bacci, tuni ma yarinyar tayi baccin ita kuma ta faɗa duniyar tunani wanda a yanzu ya zamar mata jiki ciki harda na Kawu Amadu don idan tace bata son auren shi to tayi ƙarya saidai gani take shi ba don yana sonta bane zai aure ta, innarsu ce ta shigo da sallama ta ɗago kai ta kalleta tare da amsa mata, tambayarta tay ko har ta fara bacci ne tace mata a'a ta kwantar da salma ne tace mata to tazo ɗakinta yanzu da sauri ta tambayeta lafiya innar tay ɗan murmushi tace in tazo taga ko menene ta juya, innar na shiga ɗakin itama ta shigo tana sanye da doguwar rigar bacci ta yafo gyale a kanta, koda taga Gwaggo bata kawo komai ba a ranta ta ɗauka an kirata ne su gaisa ta duƙa a gabanta tana ɗan murmushi ta gaishe da ita itama fuska a sake ta amsa ta tambayi Salma tace mata tayi bacci, shiru ta ɗan biyo baya can Gwaggo ta sauke yar ajiyar zuciya ta kalleta tace mata dama taji abunda ke faruwa tsakaninta da Amadu sai dai yadda tayi tunani ba haka bane ba wanda ya saka shi ya nemeta tsakanin ita da Fatuu basu ma san da yayi mata Maganar ba in ba yanzu daya faɗi mata ba kuma ita a ganinta koda sashi akai ya nemi Aurenta ai don an yaba da kyawawan halayenta ne,
"Ko akwai wanda kike so ne?" innar su ta jefa mata tambaya ta girgiza mata kai ba tare data ɗago ba Gwaggo tace to in dai har taji tana son Amadun ta bashi dama tunda ba haramun bane wai don yana saurayi sau nawa akai ga misali nan ma akan Manzon Rahama, shiru suka ɗanyi kafin Gwaggo tace mata ta tashi taje ita dama tazo ne don ta Warware mata abunda take tunani in Allah yasa sun daidaita to suna Farinciki, miƙewa tay ƙasa ƙasa da murya tace ma Gwaggon saida safe ta amsa mata, bayan fitar Haulat yar hira sukai da innar tasu kafin Gwaggo tayi mata Sallama suka miƙe tare, har bakin zaure ta rakota tayi mata Godiya da Addu'ar Allah ya bar zumunci sukai ma juna saida safe, lokacin da ta fito Amadu na zaune bisa ɗan dandamalin gaban gidan dake kallon nasu Haulat yana latsa waya, yana ganinta ya miƙe ya nufo ta, a gabanta ya tsaya yace har ta fito tana murmushi tace eh suje ya ɗan sosa ƙeya yace to ya ake ciki tay mashi wani kallo mai kaman harara tace yadda ake waje yay yar dariya ta ƙara ce mashi suje in sunje gida yaji yadda akai, ɗan ƙara sosa ƙeya yay yace ko taje ya taho daga baya tayi murmushi tare da ɗan girgiza kai tace dama ba rakota yay ba kenan abun shi ya kawo shi, daga haka ta juya yana dariya yace mata a'a yanzu zai taho ƙilan ma ya sameta a hanya, bayan tafiyarta wayar shi ya ɗago ya shiga kiran Haulat bayan tayi ringing ta ɗaga tayi mashi sallama ya amsa ta gaishe dashi nan ma ya amsa daga haka tayi shiru yace mata in ba damuwa yana son ganinta a ƙopar gida tay ɗan jimm jin haka yasa yace mata in bazata samu fitowa ba ba damuwa bari ya tafi, a hankali tace mashi a'a gata nan zuwa, shiru tayi tana tunanin yadda zata fita hakanan sai taji wata irin kunyar shi ta kamata can dai ta miƙe ta nufi wurin kayanta ta curo doguwar Hijab ta daura saman rigar jikinta, tsaye tayi bakin kopar ɗakin tana jin nauyin zuwa ta tambayi innarsu can dai ta nufi ɗakin saida ta ƙara yin jimm kafin ta kai hannu ta ɗaga labulan ta shiga da yar Sallama, innar tasu har ta kwanta ta amsa mata tare da ɗago kanta tana kallonta Haulat ɗin ta sadda kanta ƙasa da ƙyar tace mata dama wai Kawu Amadu ne ke son ganinta a waje, murmushi innar tayi tace mata to taje, har ta juya taji ta kirata ta juyo ta kalleta,
"So nike in tambaye ki kina son Amadun ne ko kuwa?" maida idonta tayi ƙasa sannan ta ɗan jinjina mata kai alamar eh,
"To idan kinje yay maki Maganar Aure ki bashi dama a turo kawai" ɗagowa tay ta kalli innar cikin sanyin murya tace ita gani take kamar yayi wuri da yawa kada aita yin surutu, innar na murmushi tace to miye abun surutu abu kusan shekara da rasuwar Mijin nata wasu ma suna gama takaba da sun samu miji suke yin auren su tunda rashin yin auren ai ba abunda zai canza ko to duk miye na jinkiri tunda Allah ya kawo mai sonta kuma ma Mutum kamar Amadu ta amince mashi kawai ta amsa da to ta juya, yana tsaye gefen ƙopar gidan ta fito ta tsaya a jikin kopar ya juyo yana kallonta da murmushi da yake akwae haske itama ɗan murmushin take mashi ta gaishe shi ya amsa tare da tambayar ina ɗiyar shi tace mashi tayi bacci,
"Allah yasa dai kema ba baccin kike ba na tado ki" a hankali ta girgiza mashi kai alamar a'a suka ɗanyi shiru suna kallon juna can yace "na cika naci ko, kiyi haƙuri kinsan abunda rai ke so ba kamar kuma ga baƙon abun gaba ɗaya na kasa samun natsuwa da aka ƙi amince man" Murmushi tayi kawai bata ce komai ba ya sake cewa "Gwaggota tazo kun yi magana ne?" kai ta daga mashi alamar eh,
"To yanzu kin yarda ba tursasa man akai in aure ki ba ni ke son hakan?" kai ta ƙara ɗaga mashi,
"To yanzu an yanke shawara game da buƙatar tawa ko sai na ƙara jira?" shiru tayi tana ɗan yi murmushi kafin a hankali tace an yanke yace to yana saurarenta Allah yasa yaji Alkhairi ya tsareta da ido yana mata wani kallo gaba ɗaya duk sai taji nauyin shi take ji ganin abun take kamar a Mafarki wai ita da Kawu Amadu ne suke soyayya har ma da zancen aure abunda bata ta6a kawo wa a ranta ba, cikin kwantar da murya yace mata pls a tausaya mashi kada aja mashi aji, kallon shi tayi tana murmushi a hankali ta furta "an amince maka" ɗan buɗa ido yay yace "You Mean kin amince zaki aure ni?" kai ta ɗaga mashi ya wani lumshe ido tare da kai hannu ya dafe saitin zuciyarshi ya furta "Alhamdulillah, har bansan yadda zan bayyana daɗin dana ji ba yau dai ɗan Gwaggo zai yi bacci hada munshari da ana niyyar a zautar mata da yaro" Dariya Haulat tayi har haƙoranta suka bayyana tace "Kai Kawu Amadu" buɗe idon shi yay sosae yace "Allah kuwa kullum da tunanin amsar da zaki ban nike kwana kinsan ni ba sanin kan abun nayi ba gaba ɗaya na zurma har na fara tunanin ko ban shiga fagen Soyayyar ba a sa'a da naga kamar ba'a so na",
"Ai kai da wuya ace ba'a son ka kawai don baka cewa kana son ne" ɗage gira yay yace Why ta faɗi Hakan,
"Saboda kana da duk wani abu da mace zata so a wurin Namiji" da ƙyar ta ƙarasa Maganar yana murmushi yace a hakan shi da baida kuɗi abunda yanzu kusan mata saboda su suke son Mutum,
"Ko akwai wanda kike so ne?" innar su ta jefa mata tambaya ta girgiza mata kai ba tare data ɗago ba Gwaggo tace to in dai har taji tana son Amadun ta bashi dama tunda ba haramun bane wai don yana saurayi sau nawa akai ga misali nan ma akan Manzon Rahama, shiru suka ɗanyi kafin Gwaggo tace mata ta tashi taje ita dama tazo ne don ta Warware mata abunda take tunani in Allah yasa sun daidaita to suna Farinciki, miƙewa tay ƙasa ƙasa da murya tace ma Gwaggon saida safe ta amsa mata, bayan fitar Haulat yar hira sukai da innar tasu kafin Gwaggo tayi mata Sallama suka miƙe tare, har bakin zaure ta rakota tayi mata Godiya da Addu'ar Allah ya bar zumunci sukai ma juna saida safe, lokacin da ta fito Amadu na zaune bisa ɗan dandamalin gaban gidan dake kallon nasu Haulat yana latsa waya, yana ganinta ya miƙe ya nufo ta, a gabanta ya tsaya yace har ta fito tana murmushi tace eh suje ya ɗan sosa ƙeya yace to ya ake ciki tay mashi wani kallo mai kaman harara tace yadda ake waje yay yar dariya ta ƙara ce mashi suje in sunje gida yaji yadda akai, ɗan ƙara sosa ƙeya yay yace ko taje ya taho daga baya tayi murmushi tare da ɗan girgiza kai tace dama ba rakota yay ba kenan abun shi ya kawo shi, daga haka ta juya yana dariya yace mata a'a yanzu zai taho ƙilan ma ya sameta a hanya, bayan tafiyarta wayar shi ya ɗago ya shiga kiran Haulat bayan tayi ringing ta ɗaga tayi mashi sallama ya amsa ta gaishe dashi nan ma ya amsa daga haka tayi shiru yace mata in ba damuwa yana son ganinta a ƙopar gida tay ɗan jimm jin haka yasa yace mata in bazata samu fitowa ba ba damuwa bari ya tafi, a hankali tace mashi a'a gata nan zuwa, shiru tayi tana tunanin yadda zata fita hakanan sai taji wata irin kunyar shi ta kamata can dai ta miƙe ta nufi wurin kayanta ta curo doguwar Hijab ta daura saman rigar jikinta, tsaye tayi bakin kopar ɗakin tana jin nauyin zuwa ta tambayi innarsu can dai ta nufi ɗakin saida ta ƙara yin jimm kafin ta kai hannu ta ɗaga labulan ta shiga da yar Sallama, innar tasu har ta kwanta ta amsa mata tare da ɗago kanta tana kallonta Haulat ɗin ta sadda kanta ƙasa da ƙyar tace mata dama wai Kawu Amadu ne ke son ganinta a waje, murmushi innar tayi tace mata to taje, har ta juya taji ta kirata ta juyo ta kalleta,
"So nike in tambaye ki kina son Amadun ne ko kuwa?" maida idonta tayi ƙasa sannan ta ɗan jinjina mata kai alamar eh,
"To idan kinje yay maki Maganar Aure ki bashi dama a turo kawai" ɗagowa tay ta kalli innar cikin sanyin murya tace ita gani take kamar yayi wuri da yawa kada aita yin surutu, innar na murmushi tace to miye abun surutu abu kusan shekara da rasuwar Mijin nata wasu ma suna gama takaba da sun samu miji suke yin auren su tunda rashin yin auren ai ba abunda zai canza ko to duk miye na jinkiri tunda Allah ya kawo mai sonta kuma ma Mutum kamar Amadu ta amince mashi kawai ta amsa da to ta juya, yana tsaye gefen ƙopar gidan ta fito ta tsaya a jikin kopar ya juyo yana kallonta da murmushi da yake akwae haske itama ɗan murmushin take mashi ta gaishe shi ya amsa tare da tambayar ina ɗiyar shi tace mashi tayi bacci,
"Allah yasa dai kema ba baccin kike ba na tado ki" a hankali ta girgiza mashi kai alamar a'a suka ɗanyi shiru suna kallon juna can yace "na cika naci ko, kiyi haƙuri kinsan abunda rai ke so ba kamar kuma ga baƙon abun gaba ɗaya na kasa samun natsuwa da aka ƙi amince man" Murmushi tayi kawai bata ce komai ba ya sake cewa "Gwaggota tazo kun yi magana ne?" kai ta daga mashi alamar eh,
"To yanzu kin yarda ba tursasa man akai in aure ki ba ni ke son hakan?" kai ta ƙara ɗaga mashi,
"To yanzu an yanke shawara game da buƙatar tawa ko sai na ƙara jira?" shiru tayi tana ɗan yi murmushi kafin a hankali tace an yanke yace to yana saurarenta Allah yasa yaji Alkhairi ya tsareta da ido yana mata wani kallo gaba ɗaya duk sai taji nauyin shi take ji ganin abun take kamar a Mafarki wai ita da Kawu Amadu ne suke soyayya har ma da zancen aure abunda bata ta6a kawo wa a ranta ba, cikin kwantar da murya yace mata pls a tausaya mashi kada aja mashi aji, kallon shi tayi tana murmushi a hankali ta furta "an amince maka" ɗan buɗa ido yay yace "You Mean kin amince zaki aure ni?" kai ta ɗaga mashi ya wani lumshe ido tare da kai hannu ya dafe saitin zuciyarshi ya furta "Alhamdulillah, har bansan yadda zan bayyana daɗin dana ji ba yau dai ɗan Gwaggo zai yi bacci hada munshari da ana niyyar a zautar mata da yaro" Dariya Haulat tayi har haƙoranta suka bayyana tace "Kai Kawu Amadu" buɗe idon shi yay sosae yace "Allah kuwa kullum da tunanin amsar da zaki ban nike kwana kinsan ni ba sanin kan abun nayi ba gaba ɗaya na zurma har na fara tunanin ko ban shiga fagen Soyayyar ba a sa'a da naga kamar ba'a so na",
"Ai kai da wuya ace ba'a son ka kawai don baka cewa kana son ne" ɗage gira yay yace Why ta faɗi Hakan,
"Saboda kana da duk wani abu da mace zata so a wurin Namiji" da ƙyar ta ƙarasa Maganar yana murmushi yace a hakan shi da baida kuɗi abunda yanzu kusan mata saboda su suke son Mutum,