Sashe 105
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani irin fitsari ne ya tashi Fatuu dama ta saba tashi fitsari cikin dare sosae, zame jikinta tayi daga nashi ta lalla6a ta saukko kafin ta nufi hanyar toilet d'in da sauri don tana saukkowa taji kaman zai zubo mata, lokacin data duk'a don yin fitsarin wani kalan discharge da bata saba gani ba taga ya zubo mata amman sanin dama tana fitar da shi yasa bata maida kai ba, bayan ta gama fitsarin tayi tsarki ta fito, komawa tayi gado ta kwanta bata fi yan mintuna ba taji cikinta yay wani irin juyawa har saida ta cize baki, wani fitsarin taji ya kamata sosae da sauri ta saukko ta nufi toilet, koda ta duk'a don tayi d'an kad'an ya zubo tare da wani irin ciwo har saida tay d'an sautin rad'ad'i, da k'yar ta yunk'ura ta fito daga cikin toilet d'in ta koma gado, gaba d'aya kwanciyar ta gagareta don ciwon k'aruwa yake mata, wasa wasa tun tana a saman gado har ta kai ta saukko ta duk'e k'asa, duk abunan bata yi tunanin tada Haisam ba don gani take kaman ciwon zai lafa, tun tana juye juye har ta kai ta fara d'an yar fa hannu tana fad'in wash, ganin abun bana k'arewa bane don sai ma cigaba da yake yasa ta gane nak'uda ce take yi a wahalce ta fara kiran sunan Haisam tun dai bata d'aga murya har takai ta d'aga tana ta kiran sunan shi tana ya taimaka mata, ganin yak'i tashi yasa ta fara bubbuga katifa can acikin baccin ya jita a hankali ya fara bud'e idanun shi, daidai ya bud'e ta k'ara kiran sunan nashi tana ya taimaka mata, wata kalar wuntsilowa yay ya sauko da sauri ya zagayo inda take a durk'ushe shima ya duk'a ya shiga tambayar mike damunta hannuwan shi rarruke da ita, cikin ciwo tace mashi tana ganin kaman nakuda ce take a rud'e ya furta Ok bari ya fad'i ma Aunty, mik'ewa yay da sauri ya nufi k'opa har ya bud'e komi ya fad'o mashi a rai sai kuma ya kulle ya dawo cikin d'akin ya nufi wurin side drawer, wayar shi ya d'aukko ya dawo saitin Fatun ya fara k'ok'arin kiran ta, lokacin da wayar ta shiga duk bugu d'aya tare yake da fad'uwar gaban shi, sai faman sintiri yake a wurin saida wayar ta kusa yankewa sannan Aunty ta d'auka cikin muryar bacci ta ambaci sunan shi tare da tambayar lafiya a d'an rud'e yace mata Baby ce ke nak'uda da sauri tace to gata nan zuwa harda ce mata don Allah tayi sauri tana cikin ciwo sosae ta furta Ok gata nan, duk'awa yay ya tallabo Fatun fuskar shi har ta fara hautsinewa cike da tausayi yake ce mata sannu, after few minutes aka turo kopar Aunty ce ta shigo tana sanye da doguwar rigar bacci yana ganin ta ya mik'e yana nuna mata Fatun ta nufo su, a gabanta ta tsaya ta duk'a tana dubata tare da yi mata sannu, d'agowa tay tace ma Haisam nakuda ce da sauri yace to yanzu ya za'ai tace tana zuwa ya taimaka su d'aurata saman gado yace to, bayan sun d'aurata d'aukar abunda ta aje a bakin gado tayi wanda disposal gloves ce ta bud'e yar jakar ta ciro su ta fara k'ok'arin sama hannuwanta, bayan ta gama ta fara duba Fatun dama itama rigar bacci ce iya gwuiwa a jikinta, Haisam na tsaye yana ta kallon abunda take mata fuskar shi a a d'an yamutse sosae yake jin tausayin Fatun, bayan ta gama ta d'ago tana cire safunan tace mashi haihuwa ce amman da d'an saura, sake tambayar ta ya za'ai yayi tace tana ganin abunda yakamata shine su tafi Asibiti yaje ya d'aukko Mota bari ta shirya yace to ya nufi bedside don ya d'aukko makullai, har zai fita Aunty ta tsaida shi ta hanyar tambayar inda kayan haihuwa suke ya dawo ya bud'e mata wardrobe d'in bangon dake cikin d'akin inda kayan suke shirgi guda don ba abunda babu da ya danganci jariri dama tun kafin Mom taje ta taho da ita tuni an gama siyan komai na haihuwar da yawa ma daga Dubai aka siyo su Haisam ma ya taho da wasu trolley guda wanda shida Fanan suka je suka siyo su had'add'un kayan jarirai ne na gaske unisex wato wanda zasu yi ma mace da namiji komai guda biyu aka siya akwae saura ma da Fanan zata taho da su , bayan ya nuna mata ya juya da sauri ya tafi ita kuma ta fara fiddo abubuwan da za'a buk'ata anan kafin ta bud'e wurin kayan Fatuu nan ma ta d'auki abunda zata d'auka, a wata jaka ta zuba komai lokacin ya dawo yace mata ga Motar nan ya kawo bakin Entry tace to, gadon ta nufa yabi bayanta ta kai hannu ta taimaka ma Fatun ta mik'e kallon Haisam tay tace ya d'aukko mata hijab ko gyale da sauri ya furta Ok tare da juyawa, bayan ya kawo Hijab d'in ta zura mata kafin ta nuna mashi jakar kayan data za6a tace ya d'aukko tana rurruke da Fatun suka nufi hanyar fita yana biye da su, sai cije cijen baki Fatuu ke da nishi Aunty nata mata sannu haka ma Haisam, bayan sun shigo cikin parlon ta tuna da itama tana buk'atar mayafi tace ma Haisam ya aje jakar ya kamata suje Mota bari ta d'aukko mayafi, bata jima ba ta fito ta d'auro after dress a saman kayan baccin jikinta bata yi tunanin fad'i ma Mom ba don tasan ba lalle in tana a d'akinta ba, saida ta d'auki jakar sannan ta nufi k'opa lokacin data fita har ya saka Fatuu a bayan Motar shima yana zaune a wurin yana ta faman yi mata sannu, fitowa yayi ya koma gaba Aunty ta shiga baya ta kwantar da Fatun a jikinta yaja Motar da gudu suka nufi hanyar Gate,
Basu dad'e sosae ba Saboda gudun da yake shararawa suka iso Asibitin wanda babban private hospital ne kuma sananne, bayan sun shiga yana niyyar nufar parking space Aunty tace suje bakin entrance ya furta Ok ya nufi can, bayan ya parker a bakin kopar shiga cikin Aunty tace tana zuwa ta fito da sauri ta nufi shiga cikin Asibitin shi kuma ya fito ya koma bayan ya rungumo Fatuu a jikinshi yana cigaba da yi mata sannu kai kawai take d'aga mashi, bada dad'ewa ba Aunty ta fito Nurses guda biyu musulma da Christian na biye da ita sun turo Wheel chair Haisam na ganin su ya fito yana k'ok'arin fito da Fatun, bayan an d'aurata suka turata Aunty da Haisam suka rufa masu baya, Labour room suka nufa dama Aunty ta fad'a masu Vip zasu kaita suka nufi can da ita, gaba d'aya harda Haisam suka shiga cikin d'akin aka kwantar da Fatun saman gado bayan Aunty ta cire nata Hijab d'inta itama ta cire after dress dinta, daga gefen kanta Haisam ya zauna ya kama hannunta guda yana cigaba da yi mata sannu Fuskar shi a hautsine, ciwon kaman yasan an zo Asibiti nan ya shiga k'aruwa amman yana yi yana lafa mata in ya lafan har d'an gyangyad'i take, gaba daya Aunty da Nurses d'in biyu na a kanta suma suna ta yi mata sannu sai faman d'aga kai take tana yarfa hannu, in ciwon ya taso sosae hankalin Haisam ke tashi har sai ya lafa sannan hankalin shi ke d'an kwanciya, a haka saida aka shafe Kusan awa bata Haihun ba Haisam sai tambayar Aunty yake ya tak'i haihuwan tace mashi lokacin bai yi bane, sai bayan kamar awa d'aya da rabi sannan ciwon ya taso gaba d'aya daka kalli Fatuu kasan tana cikin Azabar ciwo don a lokacin ko anyi mata sannu bata iya amsawa gaba d'aya ta rurruke Haisam sai murkususu take tana kukan da ba hawaye cikin fitar hayyaci take fad'in "Ya Haisam bazan iya ba....kilan ma Mutuwa zan yi" sosae wannan Maganar tata ta k'ara rud'a shi tsantsar tashin hankali ne bayyane akan fuskar shi tayi wani irin ja fuskar yana ta ce ma Fadin "Pls Baby stop saying that....im here for you ba abunda zai faru in sha Allah zaki haihu lafiya" ganin abun yayi yawa a wurin shi yasa shi mik'ewa tsaye daga bakin gadon still yana ruk'e da hannunta guda, kallon Aunty dake tsaye a gefenta tana k'arfafa mata gwuiwa yayi yace "Aunty this is too much gaskiya, pls kiyi wani abu tana shan wahala da yawa" fuska a yamutse yayi Maganar, idon Aunty na akan Fatun tana mata kallon tausayi tace "bai yi yawa ba Son haka ake yi dama kuma duk abunda yakamata ayi mata an yi so sai mu jira Allah ya sauketa lafiya" wani kalan waro ido yay yace yanzu duk wannan Azabar ciwon da take sha ne da Sauk'i, kai Aunty ta jinjina mashi tace wasu suna spending whole day haka wasu ma 2 days ita kuwa bai fi awa d'aya da rabi da suka zo ba kuma in sha Allahu tana gab da haihuwan, girgiza kai yay idon shi akan Fatuu dake cigaba da murkususun azaba yace gaskiya to in haka ne ayi mata Cs kawai taya Mutum zai jure wannan wahalar, d'an guntun murmushi Aunty tay tare da d'an girgiza kai ta fahimci a wurin shi gani yake hakan sauki ne duk da tabbas in anyi nasarar yin shi lafiya lou yafi sauk'in, kara maimaita mata Maganar ayi mata Cs yayi ta kalle shi cike da jan hankali ta furta "ba sai an mata shi ba zata iya haihuwa da kanta, pls Son You should encourage her instead, wannan Maganganun da kake kana sata tana sarewa and kana anan ne don ka k'arfafa mata gwuiwa so is better if you do dat" d'an yamutsa baki yay jiki a mace yaja k'afa ya koma bakin gadon Aunty tace yayi mata Addu'a ya d'aga mata kai gaba daya rud'ewa tasa ya manta da yayi hakan, lokacin Aunty ta buk'aci amfani da wayarta ta tuna ta baro ta a gida tambayar Haisam tayi wayar shi ya girgiza mata kai alamar bai tare da ita,
Basu dad'e sosae ba Saboda gudun da yake shararawa suka iso Asibitin wanda babban private hospital ne kuma sananne, bayan sun shiga yana niyyar nufar parking space Aunty tace suje bakin entrance ya furta Ok ya nufi can, bayan ya parker a bakin kopar shiga cikin Aunty tace tana zuwa ta fito da sauri ta nufi shiga cikin Asibitin shi kuma ya fito ya koma bayan ya rungumo Fatuu a jikinshi yana cigaba da yi mata sannu kai kawai take d'aga mashi, bada dad'ewa ba Aunty ta fito Nurses guda biyu musulma da Christian na biye da ita sun turo Wheel chair Haisam na ganin su ya fito yana k'ok'arin fito da Fatun, bayan an d'aurata suka turata Aunty da Haisam suka rufa masu baya, Labour room suka nufa dama Aunty ta fad'a masu Vip zasu kaita suka nufi can da ita, gaba d'aya harda Haisam suka shiga cikin d'akin aka kwantar da Fatun saman gado bayan Aunty ta cire nata Hijab d'inta itama ta cire after dress dinta, daga gefen kanta Haisam ya zauna ya kama hannunta guda yana cigaba da yi mata sannu Fuskar shi a hautsine, ciwon kaman yasan an zo Asibiti nan ya shiga k'aruwa amman yana yi yana lafa mata in ya lafan har d'an gyangyad'i take, gaba daya Aunty da Nurses d'in biyu na a kanta suma suna ta yi mata sannu sai faman d'aga kai take tana yarfa hannu, in ciwon ya taso sosae hankalin Haisam ke tashi har sai ya lafa sannan hankalin shi ke d'an kwanciya, a haka saida aka shafe Kusan awa bata Haihun ba Haisam sai tambayar Aunty yake ya tak'i haihuwan tace mashi lokacin bai yi bane, sai bayan kamar awa d'aya da rabi sannan ciwon ya taso gaba d'aya daka kalli Fatuu kasan tana cikin Azabar ciwo don a lokacin ko anyi mata sannu bata iya amsawa gaba d'aya ta rurruke Haisam sai murkususu take tana kukan da ba hawaye cikin fitar hayyaci take fad'in "Ya Haisam bazan iya ba....kilan ma Mutuwa zan yi" sosae wannan Maganar tata ta k'ara rud'a shi tsantsar tashin hankali ne bayyane akan fuskar shi tayi wani irin ja fuskar yana ta ce ma Fadin "Pls Baby stop saying that....im here for you ba abunda zai faru in sha Allah zaki haihu lafiya" ganin abun yayi yawa a wurin shi yasa shi mik'ewa tsaye daga bakin gadon still yana ruk'e da hannunta guda, kallon Aunty dake tsaye a gefenta tana k'arfafa mata gwuiwa yayi yace "Aunty this is too much gaskiya, pls kiyi wani abu tana shan wahala da yawa" fuska a yamutse yayi Maganar, idon Aunty na akan Fatun tana mata kallon tausayi tace "bai yi yawa ba Son haka ake yi dama kuma duk abunda yakamata ayi mata an yi so sai mu jira Allah ya sauketa lafiya" wani kalan waro ido yay yace yanzu duk wannan Azabar ciwon da take sha ne da Sauk'i, kai Aunty ta jinjina mashi tace wasu suna spending whole day haka wasu ma 2 days ita kuwa bai fi awa d'aya da rabi da suka zo ba kuma in sha Allahu tana gab da haihuwan, girgiza kai yay idon shi akan Fatuu dake cigaba da murkususun azaba yace gaskiya to in haka ne ayi mata Cs kawai taya Mutum zai jure wannan wahalar, d'an guntun murmushi Aunty tay tare da d'an girgiza kai ta fahimci a wurin shi gani yake hakan sauki ne duk da tabbas in anyi nasarar yin shi lafiya lou yafi sauk'in, kara maimaita mata Maganar ayi mata Cs yayi ta kalle shi cike da jan hankali ta furta "ba sai an mata shi ba zata iya haihuwa da kanta, pls Son You should encourage her instead, wannan Maganganun da kake kana sata tana sarewa and kana anan ne don ka k'arfafa mata gwuiwa so is better if you do dat" d'an yamutsa baki yay jiki a mace yaja k'afa ya koma bakin gadon Aunty tace yayi mata Addu'a ya d'aga mata kai gaba daya rud'ewa tasa ya manta da yayi hakan, lokacin Aunty ta buk'aci amfani da wayarta ta tuna ta baro ta a gida tambayar Haisam tayi wayar shi ya girgiza mata kai alamar bai tare da ita,