← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 93 OF 211

Sashe 93

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Allah kuwa Fauziyya a yadda aka fad'i aikin da yake na tabbatar ba k'ananun kud'i yake samu ba ga kuma Baban shi Governor kacokam, da ya turo maki kawai kiyi mashi godiya tunda k'arshe ma shi za'ai ma amfani dasu" murmushi kawai Fauzy tayi kafin tace mata yanzu ta turo mata su gaba d'aya ne tace a'a ta bari sai gobe zasu zauna su tsara abubuwan da za'a yi dasu don har sun gama Magana da baban su Hanif ranar Alhamis zata tafi sai ta bar su sultan d'in a gidan Maman taufiq ranar Friday in ta dawo daga School sai su dawo wurinta Fauzyn tace to,

"Oh ikon Allah ikon gaske, abu dai kinga kamar wasa kuma tabbata zai yi in sha Allah, gaskiya had'uwar ki da Zarah babban Alkhairi ne yo ke wannan ai ko karatun naki ma ba lalle ki amfana da shi ba kamar yadda kika amfana da sanin Zarah kawai dai shi ya zama sila ne",

"Wllh Aunty baki ji yadda nike jin ta ba a raina tamkar yar uwata uwa d'aya uba d'aya, ji yadda ta d'auki uban kud'i ta bada d'azun dama kuma tana man hidima sosae wannan ai ko wani dan'uwan naka mai hali wllh ba lalle yayi maka hakan ba,

"Ai tsakanin mu da ita sai dai Addu'a kawai wllh itace zamu iya saka mata da ita amman duk da hakan ina fatan ace munyi mata wani abu da zata ji dad'i sosae a ranta......" Da sauri Fauzy ta katseta da fad'in "Yauwa Aunty nima wllh ina tunanin haka, amman tunda ga bikin Mino za'ayi mi zai hana muyi kokari muyi masu wani abu da zasu ji dad'i sosae" kai Aunty ta jinjina "tabbas kuwa kin kawo shawara duk da bansan a cikin ku bikin wa za'a fara yi ba amman koma dai nawa aka fara ba abunda zai gagara kinga in ma naki aka fara komai zai zo mana da Sauk'i don lokacin nasan Atm Card d'in Sameer ya riga ya dawo hannun ki" Dariya sosae Fauzy ta saka tana fad'in kai aunty kin jiki da wata magana, bayan sun gama tattaunawa sukai ma juna sai da safe, a ranar kowa kwanan farinciki yay tsakanin Aunty da Fauzy da kuma Fatuu.

A kwana a tashi ba wuya a wurin Allah, ranar Alhamis tunda safe Aunty ta tafi Funtua, zuwa karfe sha d'aya ta isa gida lokacin data je har anyi ma gidan Fenti mai kyau kamar yadda sukai da Yaya Mubarak d'in su gaba d'aya gidan ya haske layin nasu dama kuma yana d'aya daga cikin gidaje masu d'an kyau a layin nasu, bayan sallar Azahar suka tafi inda za'a siyo furniture da ita da Kishiyar Maman su wadda itama suka d'auketa tamkar uwa a gare su don sam basu taso suka ga suna kishi ba da Mahaifiyarsu in ma suna yi to ba irin na tada fitina ko munafunci ba, wasu daga cikin K'annansu ma sai da suka girma ne suke gane wacece maman su, da yake Funtua akwae wuraren saida had'addun furniture da dama basu wani sha wahalar za6ar inda zasu ba don sun san inda zasu samu irin wanda suke so, bayan sun je wurin wanda katafaren bene ne sama da kasa duk kayan katakon ne iri daban daban, Manager d'in wurin suka buk'aci gani bayan anyi masu jagora wurin shi suka gaisa sannan Ya Mubarak yayi mashi bayanin dama kakara suke son suyi akwae kaya da zasu siya su kuma zasu za6i wasu sai suyi ciko cikin faran faran yace wannan ba matsala bane tunda suna yin hakan ya buk'aci ganin kayan suka sanar dashi suna gida amman akwai hoton su a waya, nuna mashi Vedio d'in kayan mahaifin nasu sukai ya gani kafin yace akwae buk'atar ya tura aje a gansu sai ayi masu kud'i sannan ayi cininkin, Yaya Mubarak ne yace to ba matsala a had'a shi da wanda zasu je d'in sai suje su dawo, ba 6ata lokaci aka had'a shi da Mutum biyu da zasu tafi Aunty Mareeya tace don Allah su kamanta ayi siyan mutunci Manager da suka fito tare da shi cikin show room d'in yana dariya yace karta damu su suna kamantawa sosae, a nan Aunty da Kishiyar Maman tasu da suke kira da gwaggo suka zauna akan kujeru don su jira su. Basu dad'e can sosae ba suka dawo ba laifi kam sun sayi kayan da mutunci don d'aki barin katako ne ba don dole tasa ba daba yadda za'ai Baban nasu ya yarda su siyar mashi da kaya Saboda yana son su ba tun yanzu bama sun so canza mashi kujerun yak'i yarda, za6ar wanda suke so suka shiga yi nan fa suka shiga ruwan idon wanda ya kamata, Manager d'in wurin ne ya basu shawarar d'aukar wasu lumbutsa lumbutsan leather chair yace tunda yaji suna d'akin mahaifin su zasu saka tunda shi Namiji ba'a san shi da k'yale k'yale ba, sosae kujerun sukai masu kyau saidai Aunty Mareeya tace ita abunda ke had'a ta dasu 6an6ara suke Manager yace ba dai irin wannan ba ai ko ita ta kalli leather d'in zata shaida ingancin ta yana mai tabbatar mata da ba abunda suke yi don ko shi irin su ne a parlon shi Aunty na dariya tace kodai abun su na yan kasuwa zai masu yace in yayi haka kuma ai kan shi ya kashe ma kasuwa ko, k'arshe dai su suka za6a harda dining table d'in su mai kujeru shidda, bayan sun gama da nan sama suka hau inda gadaje suke basu wani yi ruwan ido anan ba don sun san wanda ya dace su d'aukar mashi, bayan duk sun gama za6a Manager yace masu harda d'inkakkun labulaye suna dasu da agogunan bango in suna so Aunty tace yauwa bari su duba ya jagorance su nan ma suka za6a, bayan duk sun za6i abubuwan da suke so aka buga lissafi suka yi ciko wanda ya lillinka kud'in da aka Siya kayan nasu sosae, dama shima Ya Mubarak d'in ya bada tashi gudunmawar haka Baban su ma da yake ba K'aramin samu yake da Noma ba Saboda tsohon ma'aikacin Ktarda ne kuma ya kai babban matsayi kafin ya aje aikin banda babbar gonar da yake da ita anan garin yana da wasu k'ananu zasu kai ukku a wasu kauyuka dake kewaye da garin da alama dai Fauzy harda rud'ewa tasa tace ma Sameer mahaifin nasu bai iya biyan shi wayar data fasa mashi, a babbar Motar kamfanin aka zuba kayan su Aunty na gaba a Motar Yaya Mubarak suka tafi, bayan sun isa gidan tuni k'annansu har sun fito dana mahaifin nasu ta kopar shiga sitting room d'in shi ta waje, nan fa aka shiga sauke sabbin kayan yan unguwa suka shiga baza ido suna kallo, bayan angama aka d'aura nashi yan kamfanin suka tafi. Aiki ga mai k'are ka, aifa Aunty Mareeya bata ga ta zama ba dama ita ba mai son jiki bace bare abu kuma irin wannan nan fa suka zage ita da k'annanta maza da mata harda masu Aure guda biyu da suka zo aka shiga shirya parlon dama kuma tiles ne a k'asan kuma sam bai ji jiki ba Saboda ba yawan zirga zirga ake part d'in ba, zuwa bayan sallar La'asar sun gama komai gaba d'aya sashen ya koma kamar na Amarya sosae yay kyau yan gidan sai faman washe baki suke ba kamar yara sai tsallen murna suke, Vedio Aunty tayi ta tura ma Fauzy daga baya ta kirata ta sanar mata ta hau online ta gani, lokacin data yi arba da vedion bud'e baki tay ta waro ido nan ta shiga washe baki tana yarfa hannu sai faman fad'in Wayyo Allah take, da yamma mai gyaran Ac yazo don tuni ta lalace bata yi haka mai gyaran toilet ma, yan unguwa fa kan su ya kulle wasu da basu iya hak'uri sai tambayar ko biki ake gidan saidai ace masu a'a don Mahaifin nasu ya gargad'esu kan su ja baki suyi shiru sai komai ya tabbata. Sai da daddare Mahaifin su ya dawo gidan nan gaba d'aya aka taru a sashen nashi sai farinciki ake shima dai fuskar shi ta kasa daina murmushi Yay Addu'ar Allah ya tabbatar da Alkhairi duk suka amsa daga baya aka watse. Washe gari Friday shirye shiryen Abincin tarbar bak'i aka shiga yi da wuri su Aunty suka shiga kasuwa, a gidan Yaya Mubarak aka shirya za'a yi komai harda Warmers d'in da za'ayi amfani dasu plate duk anan za'a k'aro don Aunty Mareeya ta taho da wasu jigunannun Warmers d'inta dasu plates da sauran su.
Chapter 93 · 0% Book details