← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 211

Sashe 40

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

bayan ya haye a cikin wani Corridor ya tsaya cikin shi akwae flower vases masu kyau d'auke da kayatattun Flowers haka saman wurin akwae fitila mai kyau da tsari, kopopi ukku ne a wurin a gaban d'aya daga ciki ta bangaren hagu ya tsaya, hannu ya kai jikin kopar ya ta6a wani d'an circle na glass nan take k'opar tay wani d'an sauti alamar ta bud'e, tura ta yay ya shiga ya tsaya daga bakin kopar yana kallon Fauzy da tay fiki fiki duk ta firgice gata daga ita sai rigar jikinta ko gyale babu, "Come in" ya fad'a tare da yi mata nuni da kai, yamutsa fuska ta fara yi k'walla suka cigaba da zubowa ba tare data matsa daga inda take ba, hak'uri ta fara bashi kawae sai ya saki kopar yace mata ta bari ta rufe, a rud'e ta kutsa kai ciki bayan ta shiga kopar ta maida kanta ta rufe, Ya Allah kai mana Arziki mai Amfani shine abunda na furta, had'add'an parlor ne daya amsa sunan parlon masu Arziki sosae, komai na cikin shi fari da golden ne tun daga kan kujerun, labulaye, carpet, hatta fitilun cikin shi fari da golden ne kai kace da gold akai adon wasu abubuwan, sam parlon baida hayaniya komae tsaf tsaf sai ni'imtaccen sanyi mai had'e da daddad'an k'amshi ke tashi, a yanayin parlon kai kace mutane basu rayuwa a cikin shi yadda fararen abubuwan suke K'al da su, tsaye tay a bakin kopar duk da halin da take ciki sai da ta bi parlon da kallo fuskarta duk hawaye, cikin parlon ya shiga a saman farin c-table shima da adon golden ya d'aura wallet da wayar shi, hannu ya kai ya cire glass d'in Fuskar shi shima ya aje a wurin, saida ya d'an juyo ya kalleta suka had'a ido kafin ya juya walking majestically ya nufi hanyar wani Corridor ta bi bayan shi da kallo har ya shige, lokacin ta samu damar k'ara bin ko'ina na cikin Parlon da kallo baki a d'an bud'e, bai d'auki lokaci sosae ba ya fito ya cire yellow rigar ta sama sai farar ta ciki da ta kama jikin shi kirar k'arfin shi ta bayyana ya cire takalman k'afafun shi ya sanyo wasu bak'ak'en slippers masu d'an tudu, da sauri Fauzy ta maida idanunta cikin Corridor d'in jin sautin tafiya, yana fitowa suka had'a ido ya wani k'ara tamke fuskar da sauri ta maida idon gefe gabanta na bugawa da k'arfi da k'arfi, cikin parlon ya shigo ya nufi inda fridge yake a can gefe, bud'ewa yay bayan yaje gaban shi Fauzy ta kai idon ta wurin, hannu ya kai ciki ya fiddo wata k'atuwar bak'ar kwalba an nad'e saman marfinta da wata leda mai k'yalli haka ma a jikinta akwae takarda mai d'auke da rubutu zagaye da ita, d'aurata yay a saman fridge d'in ya k'ara kai hannu ciki ya d'aukko tumbler, bayan ya rufe fridge d'in ya kai d'ayan hannun shi ya d'aukko kwalbar tana ganin zai juyo da sauri ta kauda idonta daga barin kallon shi, cikin parlon ya dawo ya nufi kujera ya d'aura abunda ya d'aukko kafin ya kai hannu ya jawo c-table d'in gab da kujerar, d'aukar kwalbar da cup d'in yay ya d'aura su a saman table d'in kafin ya zauna ya kai hannu ya d'aukko kwalbar ya kaita baki yana cizge ledar da aka nad'e bakin ta, sakin baki Fauzy tay tana kallon shi cike da Al'ajabi don ita a saninta irin wannan kwalbar ta giya ce, lokacin daya gama bud'ewa ya fara tsiyayawa a cikin cup d'in wani irin harbawa zuciyar Fauzy ta shiga yin don kuwa ganin kalar abunda ya zuba a cikin cup d'in ta tabbatar ma kanta da giya ce, kaman rabi ya zuba bayan ya rufe kwalbar ya d'auka ya kai baki ya fara sipping a hankali, yana cikin sha yayi mata kallon k'asan ido da sauri ta sunnar da kanta k'asa gaban ta na cigaba da fad'uwa, yana cikin sha ya kai hannu kan table d'in ya d'aukko remote da ke a saman shi daga d'an can gefe ya kunna Tv, bayan ta kama ya shiga caccanza channel ya kamo wadda yake so sannan yaci gaba da shan lemun d'ayan hannunshi ruk'e da remote d'in ya d'aura kafa d'aya akan d'aya idon shi akan Tv yana kallo, fara gajiya da tsayuwar Fauzy tay daurewa kawai take don k'afafunta har sun fara mata zafi sai wuwwurga ido take sai ta kalle shi sai kuma ta kalli Tv shi kam gaba d'aya ya maida hankalin shi akan Tv ko kallonta bai yi sai kace ma ya manta da ita a wurin, sun d'auki lokaci a haka gaba d'aya Fauzy ta gaji da tsayuwar har k'afafunta sun fara mata zunga sai kallon shi take tana yamutsa fuska tare da kikkafta idanunta da suka cika da kwalla, matsawa ta d'an k'ara yi gaba kad'an cikin rawar murya tace "Don girman Allah kayi hak'uri ka k'yale ni in tafi, nasan ana can anata nema na wllh" da alama dae bango take ma magana don kuwa sipping d'in lemun shi da ya k'ara zubawa kawai yake, kuka Fauzy tasa sosae mai sauti sai lokacin ya juyo yana mata wani kallo, cigaba da magiya tay mashi tana nuni da hannuwan ta, janye idon shi yay daga kan ta ya ci gaba da kallon shi, bayan ya gama shanye abun cikin cup d'in d'aura cup d'in yayi saman table, tsam ya mik'e ya nufo cikin parlon ganin inda take yake nufowa yasa ta zaro ido ta fara ja da baya gabanta na wani irin bugu tamkar ana mata luguden ta6are, cigaba da tunkararta yay tana ja da baya can ta juya a rud'e ta kama k'opa ta fara jijjiga handle d'in a K'ok'arin ta nata bud'e tana yi tana waiwayen shi duk ta gigice ba kamar da take ganin giya ce ya gama sha, tana haka ya cimmata kokarin bi ta gefe ta ruga tay ya kai duka hannuwan shi ya dafe kopar ta yadda ya sakata a tsakiyar su yay mata rumfa, gaba d'aya jikinta 6ari yake har bakinta sai numfashi take da k'arfi tunda take a rayuwarta bata taba shiga firgici irin wannan ba, ko lokacin da aka sanar Mata Mujaheed yayi Aure batai irin wannan firgicewar ba Saboda sumewa tay lokacin yanzu kuwa bata fatan ma ta sume d'in, gaba d'aya ganin shi take a buge yake hakan yake k'ara tada mata hankali, kafeta da ido yay yana mata wani matsiyacin kallo sai kerma bakinta ke yi tama kasa cewa komai, wayarta ce da har lokacin tana ruk'e a hannunta tare da ta Fatuu ta fara ringing da sauri ta kai idonta kan screen d'in ganin Aunty Mareeya ce me kiran yasa a kid'ime ta fara k'ok'arin d'auka don ta sanar mata halin da take ciki kwatsam taji ya kawo hannu ya buge wayar ta fad'i k'asa ta daki tiles, daga jin sautin fad'uwar ba sai an fada ba glass d'in ya fashe, cikin rawar murya ta fara fad'in "D...don girman Allah, don son ka da Manzo SAW kayi hak'uri, wllh bada sani na na buge ka ba har wayan ta fad'i kaji na rantse..." abun ka da fara fuskarta har tayi jajur tunda take a rayuwarta bata ta6a kasancewa da Namiji haka ba don kusancin yayi yawa, bin ta kawae yay da ido da suke a d'an lumshe wanda suna daga cikin abun da ke tafiya da mata a tattare da shi, komai nasu da Haisam iri d'aya sai kace suma yan biyun ne don shima ya iya lumshe ido, kaman daga sama taji yace,

"What is ur name" idanu waje cikin rawar murya tace "n..ni suna...na...Fauziyya" shiru yayi kafin ya k'ara cewa "What's your relationship with the bride?" har saida ta had'iyi abu kafin tace "Ni..Best Friend din ta ce tare muke karatu" da k'yar take bashi amsa don har lokacin a firgice take, tambayar ta ya k'ara yi a wani Makaranta suke karatu ta bashi amsa da School of nursing Katsina, "A nan kike?" da alamun rashin fahimta tace ina, kaman bazai bata amsa ba sai kuma taji ya furta sunan Katsina nan ta gane yana nufin a Katsina d'in take, ce mashi tayi ita yar Funtua ce, hannu ya kai ya shafi beard din shi bayan ya janye hannun yace mata ina ne Funtua, duk da halin da take ciki saida taji Maganar kaman ta rainin wayau don sai taga ya za'ai yace bai san garin ba, amsa ta bashi da babbar local Government d'in Katsina ce, dan ta6e baki yay ya juyar da Fuskar shi gefe,

maido fuskar yay ya kalleta yace "Kinsan abunda kika fasa man yana da kud'i sosae?" da sauri ta jinjina mashi kai alamar eh, yace "Ok ina son ki biya shi" yamutsa fuska ta fara yi zata cigaba da kuka yay mata wani kallo ba shiri ta saki fuskar tace "Wallahi, tallahi kaji na rantse maka bazan iya biyan ka ba" still yay yana kallonta kaman bazai ce komai ba can yace "Ok sai ki sanar ma Dad d'in ki ya biya" girgiza kai ta hau yi "Wllh shima nasan bazai iya biyan ka ba....." Katseta yay ya d'age gira yace tasan kud'in shi ne, da sauri tace "a'a ban sani ba amman dai nasan zata yi kud'i sosae kuma mu wllh talakawa ne kawai dai muna da rufin asiri amman nasan baza'a iya biyan ka ba" tana rufe baki yace ai yasan basu rasa wani abu da za'a saida a biya shi, idanunta ne suka k'ara cikowa da k'walla suka zubo mata sharr ta kai hannu tana gogewa tace "saidae gidanmu kuma a ciki muke sai kuma gonar Baban mu ita kuma anan ake noma Abincin da muke ci wani kuma a saida ayi wasu hidindimun tunda baban namu ya aje aiki pension ake biyan shi kuma basu isa" shiru yay bayan ta gama kora mashi bayanin can yay sigh yace "Ok naji, but you must compensate me for the damage" yana rufe baki ta fashe mashi da kuka ya kai dogon yatsan shi jikin bakin shi yay mata alamar tay shiru, gunji ta koma yi tana yi tana kai hannu tana goge kwallan dake zubo mata ya kafeta da ido,
Chapter 40 · 0% Book details