← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 110 OF 211

Sashe 110

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Bayan Aunty ta taimaka mata ta gyara jikinta sun fito ta d'aukko mata doguwar rigar da ta sako mata cikin kayan ta saka ta d'aura gyalenta, Aunty da kanta ta shirya mata pad a jikin pant d'in da zata saka ta bata ta sa kafin ta bata turare ta fesa bayan ta gama kimtsawa ta haye saman gadon da aka canza mata acan wani bangaren d'akin, juyawa tayi tana kallon babies d'in dake kwance a gefe da murmushi Aunty ma zama tay daga bakin gadon tana kallon su bada jimawa ba Nurse Haleema ta shigo ruk'e da d'an babban tray an d'auro kayan tea da bread a leda da yake a Vip d'in har Abinci ake badawa ta d'aura akan drawer tace ma Aunty gashi nan dama ita tasata taje ta amso bayan ta ajen ta juya ta fita, Aunty ce ta had'a mata kakkauran tea ta bata ta fara sha sosae taji dad'in tea d'in biredin ne take ci kad'an tana cikin sha Aunty tace bari ta amso mata magunguna da in ta gama zata sha tace to, bayan fitar ta juyawa tay tana kallon yaran nata tana sakin k'ayataccen murmushi gaba d'aya har yanzu ganin abun take kamar wasa wai ita ta haife su ita kanta sosae take ganin kyaun yaran sai kace larabawa duk da dai akwai jinin larabawan a jikin su, lips d'in su sak kalar na Haisam wato peach saidai nasu yafi cizawa gashin girar su ma a tsare yake kwance lub gashi bak'i ne sosae komai dai nasu mai ban sha'awa ne, bada jimawa ba Aunty ta dawo lokacin ta gama shan tea din ta bata magungunan tana cikin sha Hassan d'in ya farka yana motsi can ya kai hannun shi dake cikin mitten ya fara tsotsa Aunty dake kallon shi tace "da alama dai grandpa acici ne, tun ana goge shi ya fara mamulan hannu" Fatuu dake yar dariya tace d'azun ma da ta d'aura mata shi saida ya tsotsi hannun har ta fad'i mata abunda Haisam yace na siyo mashi Madara tana dariya tace ina ruwan sabon Baba, ce ma Fatun tay ta fiddo breast d'in aga in milk d'in ya zo tace to, bayan ta fiddo tasata ta matsa ba ruwan sai yellow d'in farko tace ta bashi ya sha ruwan zai zo, koya mata yadda ake ruk'on babyn in za'ai feeding ta shiga yi Fatun nata murmushi yayin da take jin wani iri daya kama sosae yake sha Aunty na mashi tsiya tana fad'in duk da suruki ne ta wani bangaren, suna haka aka tura kopar a tare suka kai idanun su wajen Jidderh ce ta fad'o cikin d'akin da sauri su twins na biye da ita suna ganin su Fatun suka nufo su da d'an gudu gudu daga baya Mom ta shigo Dad da Haisam na biye da ita duk suka nufo gadon, tsaye duk sukai a gaban gadon da sauri Fatuu ta maida breast d'in nata ganin su Dad tuni Jidderh ta d'aukko Hussein su Yasmeen da twins duk suka mik'a ma Fatuu hannu suna yar rige rigen wanda zai amshe shi sai dariya ake ganin d'aya yak'i hak'ura a ba d'aya yasa Aunty saka baki tace su bi a hankali kowa zai d'auka, gaishe da Dad Fatuu tayi yana ta faffad'an murmushi ya amsa tare da Fad'in "Sannu, sannu da kokari Daughter" kai ta jinjina mashi tana ta murmushi Mom ma tayi mata sannu da tambayar jikinta tace lafiya lou, had'a ido sukai da Haisam suka shiga yi ma juna murmushi Mom data k'agara ta d'auki jaririn ta mik'a ma Jidderh hannu tana fad'in tunda ta gani ta kawo,
"Ma sha Allah lakuwwata illa billah, Yanzu Daughter da kanki kikai wannan aiki?" Mom ta tambaya idanunta akan Fatuu tay murmushi kawai Aunty tace "ai gaskiya tayi kokari wllh" jinjina kai Mom tayi ta furta sosae kafin tace amman saida aka k'arata wannan ko Aunty tace a'a har saida fuskarta ta nuna mamaki ta shiga k'ara yi ma Fatuu sannu fuskarta d'auke da murmushin farinciki haka Dad ma sannun yake ta ma Fatuu, gaba d'aya kowa tsantsar farinciki ne akan fuskokin su kai kace ba'a ta6a yi masu haihuwa ba duk da dai an d'auki lokaci ba'ayi ba gashi wad'annan ne jikokin Farko, sai faman k'arba k'arba ake tsakanin yaran Jidderh ma sai sannu take ma Fatun, Dad ne ya tambayi an saka masu suna Aunty tace eh ta fad'i mashi har saida ya d'an waro ido alamar mamaki,
Chapter 110 · 0% Book details