← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 211

Sashe 50

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Na'eem ne ya matso shima yace "ni ina ma tunanin k'ilan harda smoke d'in nan duk da ance baida illa amman kasan kowa da kalan yadda jikin shi ke karbar bak'on abu" jinjina kai sukai cike da gamsuwa ba laifi Haisam d'in ya d'an ji fargabar shi ta ragu, after some minutes Likitan ya dawo saida ya d'an d'aga masu hannu sannan ya tura k'opar d'akin ya shige, su Nameer ne suka k'araso bayan Laila ta yi masu kwatancen inda Asibitin yake, gaida su Abbas sukai Mino dai ta kasa cewa komai sai bin su da ido take Fuskar ta sharkaf da hawaye Abbas ne ya shiga kwantar mata da hankali tana jinjina mashi kai, bada jimawa ba Laila ta dawo wurin tare dasu Dad da Mom sai Hajiya da gwaggo, gaidasu su Najeeb suka shiga yi gwaggo dai kai kawai take d'agawa don hankalinta in yayi dubu to ya tashi gaba d'aya jinin ta akan akaifa yake, Dad ne ya tambayi ya ake ciki Abbas ya fad'i mashi bayanin da likitan yayi yace "Ok sai mu jira shi Allah yasa muji Alkhairi" duk suka amsa da Amin, kallon Haisam yay da tunda suka zo bai tanka ma su ba sai ido kawae yake bin su dashi, ganin yanayin fuskar shi yasa shi kai hannu ya dafa Shoulder d'in shi da d'an murmushi yace "Don't worry Son, she will be fine in sha Allah muyi mata Addu'a" jinjina mashi kai yay Dad d'in ya kai hannu ya fara k'ok'arin cire mashi babban rigar yana fad'in bari a cire yasha iska don duk yayi zufa duk da yanayin wurin ba zafi, bayan d'an lokaci da zuwan su Hajiya tace ko dai a yi ma likitan magana aji halin da ake ciki an bar mutane da zullumi Gwaggo tace mata in ba ya gama binciken ba ba abunda zai iya fad'i tunda bai samu sakamako ba Hajiyar ta d'aga kai, Senator ne ya nuna masu waiting seat yace ma su Hajiya su zauna, Mino ma da duk hankalinta a tashe yake yace mata ta zauna ta d'aga mashi kai, basu jima sosae da zuwa ba Doctor d'in ya fito da sauri su Mom suka mik'e haka Hajiya ma da gwaggo, yana ganin Dad ya d'an sunkuyar da kai ya gaishe dashi bayan ya amsa yace ashe patient d'in su ce yace eh matar d'an shi ce, jinjina kai Doctor yay ya d'an yi shiru with confusion on his face Hajiya tace "Dr kai muke saurare, mi binciken naku ya gano yayi silar fad'uwar ta" nannauyar ajiyar zuciya yay idon shi akanta yace "pls zan iya ganin wani daga cikin danginta?" kan kowa ne ya d'aure duk suka zuba mashi ido, Dad ne yay saurin cewa "da wani abu ne?" d'an girgiza kai yay yace "No, kada ku damu yalla6ai inaso zamu d'an yi wata magana ne da d'aya daga cikin danginta wanda suke da kusanci sosae" kwa6e fuska Hajiya tayi tace "to ai nan duk danginta ne tunda alak'ar Aure ta shiga tsakani ai duk an zama d'aya, in ma mafi kusancinta ne ai Mijinta ne gashi sai kuyi Maganar" ajiyar zuciya doctor ya k'ara yi ya kai hannu ya gyara zaman glass d'in shi gaba d'aya jikin kowa yayi sanyi don sun fahimci bai son fad'i masu halin da ake ciki, sosae Doctor ya shiga rud'ani kawai sai ya yanke ya sanar da Mijinta abunda suka gano k'ilan shi yana da masaniya kan ciwon nata, tambayar ina Mijinta yay aka nuna mashi Haisam yace "pls let me see you in my Office" mik'a ma Abbas rigar shi yay wani irin Fad'uwa gaban shi ke yi ya juyo yay ma Dr alamar suje da hannu,

"Shin wai Fateemar ko juna biyu ne da ita??" har likitan ya juya Hajiya ta furta hakan da sauri ya juyo ya kalleta, komawa yay wurinta a d'an fad'ace tace ya fad'i masu abunda ke faruwa duk miye na wani 6oye 6oye, d'an gyaran murya yay ya fara kora mata bayanin cewa abunda suka gano shine stress ne yay mata yawa ta yuwu tayi zurga zurga da yawa ta gaji sosae hakan yasa ta suma sai dai kuma abunda ya assasa suman nata shine sun gano tana d'auke da juna biyu na tsawon wata guda, ai tun kafin ya rufe baki suka hau washe baki su Jidderh da Mino harda sakin k'arar murna gwaggo ma bakinta a washe yake haka Mom dasu Abbas kowa ka gani sai washe bakin murna yake Senator ma fuskar shi d'auke da fara'a yanata fad'in Alhamdulillah nan aka kama anata fad'in Alhamdulillah, bawan Allah ango ai shi gaba d'aya ma ya kasa magana sai murmushi yake kawai sai gani akai ya duk'a yayi sujjadar godiya ga Allah duk aka kalle shi kowa fuskar shi da fara'a, bayan ya mik'e Senator ya dafa Shoulder d'inshi yace "Hankali sai ya kwanta ko Son" kawae sai Haisam d'in ya fad'a jikin shi Dad d'in yasa hannu ya rungume shi anata dariya shima Haisam d'in dariyar farinciki yake don kwata kwata ba abunda yake zato ba Kenan, sosae hakan da suke ya ba Dr mamaki har Fuskar shi ta kasa 6oyewa Dad ne da ya lura still Haisam na jikinshi yace ma likitan kada ya damu ba sabon Aure bane an kwana biyu da yi kawae yanzu ne ake shagalin bikin, wata ajiyar zuciyar samun relieve Dr d'in yayi don da he was completely confused ace ana cikin shagalin biki kuma ga Amarya da ciki hakan ba K'aramin Al'amari bane, shima sai ya shiga taya su murnar yanata murmushi,

D'ago Haisam Dad yay suka had'a ido ya d'an bud'a ido yace "Son da alama ma har kuka kayi ko, halan kana tsoron kada Amarya ta tafi ana tsaka da shan Amarci ne" Yar dariya Haisam d'in yay sauran ma duk aka sa dariya, hannu ya kai suka gaisa ya furta "Congratulations my man, soon you will become a Father" cikin cool voice d'in shi ya furta mashi "Thank you Dad" Laila ce itama ta matso tana washe baki ta taya shi murna yay mata side hug ya amsa Jidderh ma ta matso tana washe baki tace "Congrats bro" jinjina mata kai yayi haka ma su Fauzy duk suka matso suna taya shi murna Nameer ma wurin shi yazo yana murmushi ya rungume shi yana taya shi murna, Abbas na tsaye tare da su Najeeb suma duk farinciki ne akan fuskokin su don ba K'aramin tashi hankulan su sukai ba, Abbas na dariya idon shi akan Najeeb da yake yasan da zancen wanccan cikin ya furta mashi "gaskiya Mom Zarah Sharp shooter ce ta gaske kaga fa har ta maida wani" kafin Najeeb d'in yace wani abu kaman daga sama suka ji ance "Shi kuma abokin naku jarababbe ko" gaba d'aya waro ido sukai suka sauke su akan Hajiya data yi Maganar kuma ko kallon su bata yi ba gwaggo dake gefenta sadda kai tay cike da jin kunya, gumtse dariya su Abbas d'in sukai ba wanda yace wani abu, Hajiya ce tace ma likitan zasu iya shiga su ganta da sauri yay mata alama da hannu ya furta "Yes you can" nufar d'akin sukai gaba d'aya harda Mom da Dad da gwaggo dasu Fauzy, su Haisam d'in suka tsaya jiran su gama shiga Najeeb da Na'eem suka matso wurin shi suna taya shi murna, Abbas na zuwa ya kamo hannun shi guda yay mashi side hug yace "Mom Zarah ta biya mu bashi da wuri kuma da alama dai a G.r.a d'in aka sake samo mana" washe baki Haisam d'in yay wanda shi rabon da yayi irin dariyar ma ya manta, tabbas a yadda aka fad'i lokacin shi da alama a G.r.a d'in ta same shi nan ya gane k'ilan harda shi yasa ta jin jiri da suka sauka Abuja Allah yasa ma bata samu wata matsala ba, daga baya suka shiga cikin d'akin, duk a tsattsaye suka iske su an zagaye gadon da take kwance har lokacin head dinta na a saman kanta fuskar ta sanye da Oxygen mask haka hannunta guda na sanye da drip, Addu'oin Allah ya bata lafiya aka shiga yi daga baya Doctor yace masu akwae buk'atar a d'aura ta kan Bed rest don akwai chance na zata iya miscarrying cikin in ta cika zirga zirga dole ta samu hutu sosae har ya zauna duk aka jinjina kai, Dad ne yace yakamata su tafi don dare yayi sosae sai wasu su tsaya, Aunty Laila ce tace a barta Hajiya tace a'a shi Mijin nata ya tsaya gwaggo dake murmushi tace a'a abar shi yaje ya huta ai an sha hidima Abbas yace kada shima ya fad'i duk aka sa dariya, shi da za'a barshin ma daya fi son hakan don zai so ace yana a kusa da ita ta farka, sallama Dad yayi masu ya juya Mom ma haka Nameer yayi ma su Mino magana suma suka tafi Fauzy sai faman sakin murmushi take ji take inama tana nan Fatun zata farka, kallon gwaggo Hajiya tayi tace suje ko tana d'an murmushi tace ba komai Laila taje don itama tasha hidima da yawa ita ta zauna, murmushi Hajiya tayi tace kawai dai K'aunar ta motsa bata son barin autar tata, kunya ce ta kama gwaggo tay yar dariya Hajiya tace ma Laila d'in suje kawai, har zasu juya Hajiya ta dakata tana kallon gwaggo tace bari suje sai a kawo mata abun shimfid'a da na lullu6a an taho hankali ba kwance ba, da sauri tace a'a tunda ga Hijab d'inta kuma doguwa ce lafiya lau zata yi mata ba sai an kawo komai ba abari sai zuwa gobe tunda ma dare yayi sosae tace to Shikenan suka juya suka tafi,
Chapter 50 · 0% Book details