← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 122 OF 211

Sashe 122

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Fatuu na dariya tace "shiyasa nike son ki Auntyn mu" itama dariyar take tace "ai bani da burin daya wuce inga kun kama mazajen ku gam gam wllh kuma ta wannan hanyar ne kawai in kuma aka had'a da biyayya ai magana ta k'are" kai Fatuu ta d'aga ta k'ara cewa "in dai kinga alamun ba nan kusa zaku koma ba to ki man magana sai in aiko maki dasu nan kema kuma sai ki dage da cin abubuwan dana lissafa kinga ma har twins d'in mu sun amfana suma tunda naga kaman kina da kyaun ruwan nono don cikin sati d'aya kinga Tubarkallah sun k'ara girma wllh" amsa mata tayi da to suka d'an k'ara yin hira kafin Aunty ta mik'e tace yadda sukai da Haisam sai ta sanar mata tace to in sha Allah yanzu bada dad'ewa bama zata yi mashi Maganar. Misalin k'arfe goma da rabi duk masu tafiya suka firfito lokacin tuni su Hajiya Zainab sun tafi harda Mahaifiyar su da yan'uwanta yan Ethiopia suka tafi can Nasarawa haka su Hajiya Maryam ma Farha harda musayar lambar waya ita da Fatuu don Hajiya saida ta k'ara masu fad'a da Nasiha kan rashin shirin da suke ta nuna masu duka duniyar nawa take, dama su Yadikko driver da ya kawo su ne zai mayar dasu shi dai Kamalu Katsina zai wuce dama da shirin hakan ya taho don sun gama magana da Kawu Amadu zai koma can shima yaci gaba da karatu Saboda yanata zama ba karatun tun bayan daya gama Secondary, yan d'aura ne suka fara tafiya gaba d'aya su Mom aka fito yi ma su gwaggo rakiya driver su Yadikko nan cikin harabar gidan ya shigo Haisam yaje bayan sun gaisa ya tambayi yadda aka yi dashi zai kawo su ya kuma maida su cikin washe baki driver d'in yace ai shi Abokin Mahaifin ita mai jego d'in ne to yadda sukai ya zuba mashi mai ne zai kawo su ya koma dasu sannan sai ya Sallame shi Haisam d'in ya tambaye shi nawa ne kud'in sallamar yanata washe baki yace mashi ai ko nawa ne aka bashi lafiya lou tunda dai duk abu na gida ne, kud'i masu yawa ya bashi yana ta godiya da sa Albarka sai daga baya ma ya gane shine Mijin inna wuron suma su Yadikkon saida ya basu kud'i wai susha ruwa a hanya su Yaya ana ta washe baki ana godiya, su Gwaggo ma saida ya basu kud'in dama da zasu zo saida ya tura ma Abbas da Tk kud'in mai, Gwaggo da Aunty Mareeya suna ta ya barshi don Allah shida yay hidima yana murmushi yace masu ba wani abu, Nameer na lik'e da Mino sai shagwaba yake mata wai dama ace Shikenan tazo bazata koma ba tana ta murmushi ita kanta ji take kamar kar su rabu ba kamar yanzu da taga ya wani k'ara yin Fresh, sallama suka shiga yi ma juna su Mom da Hajiya nata masu godiya da Addu'ar Allah ya bar zumunci duk suka shishshige cikin Mota Abbas ne ya d'an d'aga murya yace ma Mino in sun gama shan soyayyar ta taho su tafi in kuma su barta anan to su Mom duk sukai dariya Hajiya tace ai in sun bartan daidai kenan kawai sai a d'aura aure ya wuce da ita ba shikenan ba ita kuwa Mino kunya ce ta kamata, daga baya dai duk suka shishshiga ana ta d'aga ma juna hannu a tare Motocin suka tafi sai fatan Allah ya kai su lafiya sai kuma an sake had'uwa bikin su Mino da Aunty Laila.

Misalin k'arfe biyun rana lokacin Aunty ta dawo daga aiki don bata nan yan tafiya suka tafi bayan ta kimtsa ta nufi part d'in su Fatuu don duk su Aunty Laila na can harda Fanan anan ma suka ci abincin rana gaba dayansu don yaran gidan k'in zuwa School sukai wai gajiyar suna bata sake su ba, tana shiga duk suka yi mata Welcome kowa yana murmushi haka itama shi take masu ta nufi kujera tana ruk'e da wasu Manyan fararen ledoji masu d'auke da tambari ta zauna Jidderh ce ta tambayeta ta zubo mata Abinci tace eh ba da yawa ba ta d'an ci wani a wurin aiki tace to ta fita, bayan ta gama cin Abincin an saka su Yasmeen sun gyara d'akin Aunty ta d'ago jakar ta mik'a ma Fatuu tace gashi nan tayi amfani dasu ta d'ago d'ayar itama m'ika ma Fanan tace d'ayar Momyn twins itama gashi a tare duk suka bud'e, wasu had'addun laces ne kowa guda d'aya sai kuma manyan atamfofi na Fatuu guda biyu ita kuma Fanan guda d'aya, nan fa aka shiga yi ma Aunty godiya sosae Fanan taji dad'in hakan da tayi mata itama tayi mata godiya ta mik'e da sauri tana ruk'e da jaririn ta nufi hanyar fita tana fad'in bari ta je ta gwado ma Hajiya anata mata dariya don kowa ya fahimci taji dad'in kyautar, bata dad'e sosae ba ta dawo tana ruk'e da ledar cikin washe baki tace Hajiya tace ayi mata godiya sai ta shigo zata k'ara mata Aunty dake dariya tace sai kace wani abu Fanan d'in tace aikuwa wani abu ne don babbar kyauta ce nan suka cigaba da yin fira har aka yi La'asar, bayan sallar ne Fatuu tace ma Aunty Laila don Allah ta tayata su duba kayan da aka samu tace to nan aka shiga fiddo kayayyakin kili guda harda Fanan aka shiga bubbud'awa ana shirya su, Kusan raba kayan Fatuu tay wanda nata ne taba Fanan wai ta bata aikuwa tace wllh bazata amsa ba sai kace ita tayi mata nak'udar, K'arshe da k'yar ta amshi wata doguwar riga cikin wanda kakar su Haisam ta kawo mata daga Qatar tare da kayan jarirai had'add'un gaske duk da haka saida Fatuu ta k'ara mata da wata babbar atamfa ta rok'e ta kan ta amsa sannan ta amsa tayi mata godiya sosae, wasu masu yawa ta k'ara warewa tace ma Aunty Laila gashi ta kai ma Mom suyi amfani da su itama harda rok'onta Laila d'in ta d'an waro ido tace don me zata basu kaya haka ta marairaice mata, yar dariya tayi ta gyad'a kai tace tunda sak'o ne ta bata bari ta kai ma Mom d'in amman ashawarce ma da ta bar kayanta Fatuun ta girgiza mata kai tace Don Allah ta saka Mom d'in ta amsa, Bayan sun gama shirya kayan ta d'aukko jakar da kud'i suke suma ta fara kokarin fiddo su Laila dake kallonta tace mi kuma za'ai dasu tace mata wai su k'irga wani kallo tay mata tace har tama saka zata harareta tana matsayin Yayarta to shima k'irga kud'in aiki ne da bazata k'irga abunta ba, dole Laila tayi mata ta maida kud'in data fiddo bayan sun gama komai ta d'auki wanda ta basu ta tafi.

Bayan Sallar la'asar Fatuu na cikin yin chat saman gado Fanan ma na daga gefenta ta tasa su twins gaba saiga Mom ta shigo Laila na biye da ita d'auke da kayan da ta kai mata tana yar dariya, a saman gado Mom ta sakata ta d'aura kayan kafin ta zauna a sanyaye Fatuu ta gaishe da ita ta masa kafin tace ga kayanta nan ta maido mata a ina ake haka kawai ta kwashi uban kaya ta basu sai kace su aka ba, marairaicewa Fatuu tay ta shiga yi mata Magiya Mom d'in tace bafa za'a amsa ba gara ma kar ta wahalar da kanta, suna haka Aunty ta shigo ganin drama d'in da suke yasa ta zauna tana dariya Mom na cema Fatuu ko tayi Kuka ba za'a amshi kayan ba, tambayar abunda ke faruwa Aunty tayi Mom ta fad'i mata tare da nuna mata kayan ta kalli Fatun tace "to daughter taya za'ai hakan ai kayan ki ne ko kiyi amfani da abun ki" murya kamar zata yi kuka tace to ai kayan da yawa ya zatayi da su Mom ce tace ba tana da yan'uwa ba sai ta babbasu suma suci albarkacin twins suyi masu Addu'a,

"Amman Mom kuma ai yan'uwan nawa ne ko",

tana yin Maganar k'walla suka zubo mata Mom ta d'an bud'e ido tace miye abun kuka anan, Aunty ce tace yanzu dai tunda hakane Shikenan a d'an d'auka suma suci albarkacin twins d'in tunda haka take so, ba wasu kaya masu yawa ba suka d'auka duk da haka Fatun taji dad'i hannu ta kai ta d'aukko jakar da kud'i suke Laila na ganin haka tace "Mom see, wai kud'in ma sai an gani" wani kallo mai kaman harara Mom d'in tayi mata Fatun ta marairaice fuska tana niyyar yin Magana Mom tace "Daughter yaushe muka fara wasa irin wannan ne?" abu Fatuu ta had'iya ta d'an girgiza mata kai kamar zatayi kuka ta bata hak'uri tace dama tana son nuna masu ne Mom d'in tace mata ba buk'ata komai ta gani nata ne tayi duk abunda take so da su ta d'aga mata kai, abunda Mom ta ruk'o a hannunta ta mik'a ma Fatun tace to itama ga nata tunda ta kar6i nata Fatuu tabi yan kunnan zinari da take Mik'o mata da kallo Mom tace mata ta amsa mana ta mik'a hannu ta amsa gudun kada ta k'ara cewa ta raina ta, kallon Fanan tayi itama ta mik'a mata zoben zinarin tace itama ga nata ta waro ido tare da d'an bud'e baki cike da mamaki tace itama harda ita ta d'aga mata kai kawai sai ta matso ta rungume Mom d'in tana mata godiya su Aunty ma da Fatuu sukai mata godiya, bayan Fanan ta saketa ta saukko daga saman gadon ta nufi hanyar fita tace shima bari ta nuno ma Hajiya.
Chapter 122 · 0% Book details