← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 206 OF 211

Sashe 206

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Bayan sati biyu da haihuwar Mino ranar Alhamis lokacin hutun su Fatuu na gab da ƙarewa tana kwance saman gado da safe wurin ƙarfe sha biyu na rana jikinta sanye da turkish dress riga da wando kalar Yellow gyalen kayan na daga can gefe hakan ya bayyanar da kanta da akai ma kitson sunan Mino sati ɗaya daya wuce, tana cikin yin baccin Esha ta shigo ɗakin da gudu koda ta hangota kwance sai ta nufi gadon, hayewa tay ta fara bubbuga jikin Fatuu tana faɗin "Aunty, wake up!, wake up pls!! ki tashi" yanayin yadda take Maganar kamar zata saka kuka, buɗe ido Fatun tayi ganin Esha ce ke tashinta yasa ta tamke fuska da alamun 6acin rai ta furta "Esha! Why do you always disturb my sleep for God's sake! Banda dama in kwanta sai kin tashe ni kuma bada wani dalili ba kawai baki so ki ganni a kwance!" yamutsa fuska Esha ɗin ta shiga yi idanunta suka ciko da ƙwalla, a fusace Fatun ta ƙara cewa "yanzu da kika zo kina buguna haka miye zan maki??" cikin karyayyar murya Esha ɗin tace "Ba Momy ne bata lafiya ba kuma tayi amai da kuka" waro ido Fatun tay ta maimaita "amai da kuka!" da sauri ta jinjina mata kai aikuwa ba shiri ta wuntsilo daga saman gadon ko ta kan gyalen kayan bata bi ba ta nufi hanyar ƙopa Esha data saukko itama tabi bayanta da sauri, lokacin data shiga Bedroom ɗin Fanan kwance ta sameta a saman gado rabin jikinta lullu6e da duvet sai nishi take su twins sun sakata tsakiya fuskokinsu duk ƙwalla, a ruɗe Fatuu ta nufi bakin gadon ta zauna tare da kai hannu ta ta6a fuskarta tana tambayarta mike damunta haka, cikin nishi tace mata tunda ta tashi bata jin daɗin jikinta haka ta rinƙa daurewa har sukai breakfast to bayan sun gama ta dawo ɗaki taji zuciyanta ta fara tashi daga baya kuma sai amai yazo mata bayan tayi ne zazza6i da ciwon kai suka rufeta tana haka su twins suka zo yanzu ma bata daɗe data ƙara yin aman ba gashi harda juwa take ji shiyasa tasa a kira mata ita ganin ciwon na gaba, cike da damuwa Fatuu tace ai da tun da taji bata lafiya tasa aka kirata, wayar Fanan ɗin ta ɗauka ta kira Haisam bayan ya ɗauka cikin tashin hankali ta sanar mashi da halin da Fanan take ciki Shima hankalinshi ya tashi ba kamar daya ga lafiya lou suka yi breakfast, ce mata yay ko ta kaita Asibitin Villa tunda yafi Kusa zai iskesu yayi wasu baƙi ne daga Lagos amman bada jimawa ba zai sallamesu yazo duk yadda ake ciki pls ta sanar mashi da sauri tace to, suna gama wayar Mom ɗin shi ya kira ya sanar mata tace bari ta kirasu, bayan ta kira wayar Fanan ɗin Fatuu ta ɗauka ta tambayi yanayin jikin Fanan ɗin da damuwa Fatun tace to gata nan da gani dai tana jin jiki tana tunanin fever ce ke damunta Mom ɗin tace Ok su taho nan sai a dubata, dama Fanan ɗin a shirye take don duk sunyi wankan safe gyale Fatuu ta ɗaukko mata itama ta ɗauki wani cikin nata ta yafa, a tare harda su twins suka kamo Fanan ɗin yaran duk sun shiga damuwa gwanin tausayi, a Motar Fanan suka tafi, bayan sun isa Mom ta tarbesu aka wuce da ita Asibitin, suna zuwa kwantar da ita akai a ɗaya daga cikin lafiyayyun dakunan da ake kwantar da marasa lafiya da suka danganci gidan gwamnatin tarayyar, tambayoyi likitan daya kar6eta ya shiga yi mata tana bashi amsa ciki harda rabonta da period ta bashi amsa da tayi last Month sai wannan watan ne bata kaiga yi ba amman dama wani lokacin tana fita daga wata sannan har tsallaken wata ma tana yi nan tayi mashi bayanin lalurar data yi a baya amman tace mashi ta samu sauƙi, lokacin da ake mata tambayoyin Mom ta kira Hajiya Maryam ta sanar mata ga Fanan an kawo ba lafiya nan take hankalinta ya tashi ta shiga tambayar abunda ya sameta Mom ɗin tace ba'asan taƙamaimai ba amman gashi nan likita na bincikawa tace to gata nan zuwa, jininta aka ɗiba aka tafi yi mata gwaje gwaje, ba'a jima ba Hajiya Maryam ta ƙaraso tana ganin yanayin jikin Fanan ɗin a ruɗe ta hau tambayarta abunda ke damunta Fatuu dake zaune a wurin kanta tayi mata bayanin yadda ciwon ya fara sam ba wanda ya kawo komai a ranshi Mom tace su jira likita yazo ya faɗi sakamakon gwaje gwajen, bayan wani ɗan lokaci Hajiya Maryam ɗin ta miƙe tace bari dai tabi bayan likitan don ta ƙagara taji mike damunta haka, tana niyyar fita likitan ya sako kai da sallama taja gefe, yana shigowa ta hau tambayar shi mike damunta ne fuskarshi ɗauke da murmushi yace ta kwantar da hankalinta abun farinciki ne, su Mom na jin haka duk suka miƙe suka nufo shi, tambayarshi Hajiya Maryam ta sake yi miye abun farincikin yace sakamakon gwajin ciki da akai mata ya bayyana tana ɗauke da ciki na tsawon sati ukku, yadda kasan wutar jikinsu ta ɗauke gaba ɗaya bin shi sukai da ido ba mai ko ƙwakkwaran motsi shi kuma likitan sai murmushi yake,
Chapter 206 · 0% Book details