Sashe 196
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Tun bayan da Hajiya tayi magana dasu Tk game da tafiyarta gaba ɗaya duk sun shiga damuwa gidan ya koma shiru sam basu da wata walwala a haka har ranar tafiyar tata tazo, ranar ta kama Juma'a da safe jirgin Hajiya Maryam ya iso tazo tafiya da ita, bayan zuwan nata nan da nan gidan Hajiyar ya cika da manyan mutane musamman yan siyasa sun zo yi ma Minister sannu da zuwa da kuma yin sallama da Hajiya, da lokacin sallar Juma'a yayi gaba ɗaya a Masallacin gidan duk sukai salla, misalin ƙarfe huɗu na yamma ana gama sallar La'asar aka firfito don raka Hajiya Airport tuni an fito da akwatunan kayanta an saka a Mota don iya su kawai zata tafi dasu ba'a dauki komai na gidan ba, a gaban entrance aka jere motocin lokacin da Hajiya ta fito sanye da rantsatstsiyar lifaya tana dogara sandarta ta alfarma Tk na daga can gefe a tsaye idanunshi sunyi ja don tun da safe yake matsar ƙwalla, har su Gwaggo sun zo suma zasuyi rakiya Amadu ne zai kai su a Motar Fatuu, bayan an fara shiga cikin motoci Amadu ya nufi wurin Tk ya dafa kafaɗarshi yana bashi haƙuri yace mashi yazo suje suyi mata rakiya idanunshi cike da ƙwalla ya girgiza mashi kai yace su je kawai, ganin yanayin shi yana cikin matsananciyar damuwa yasa Amadun ƙyale shi ya juya, a tare Convoy ɗin motocin suka tashi gaba da baya motocin security ne idanun Hajiya na akan Tk dake tsaye har suka isa gate suka ta ɗan girgiza kai tare da rufe idonta, lokacin da suka fito kopar gidan cike yake da mutane yan unguwa tun dazu suke son shiga yin bankwana da Hajiya amman Security sun hana, motocin na fitowa suka shiga daga masu hannu suna faɗin sunan Hajiyar Sanata ganin haka yasa Hajiya tasa a dakata, bayan Jeep ɗin da take ciki ta tsaya ta sauke glass aikuwa mutane na ganinta suka nufo ta da sauri nan fa aka shiga tutsetseniyar kama hannun nata ana kiran sunanta harda masu yin kuka daga baya ma sai ta buɗe Motar ta fito aikuwa matan unguwa da yara aka shiga rungumeta ana kuka cike da ƙarfin hali take basu haƙuri tana kwantar masu da hankali tace ai ba an rabu ba kenan in sha Allahu za'a cigaba da zumunci kuma duk abunda take yi baza'a bari ba tunda ga Tk nan, ganin suna 6ata lokaci yasa Hajiya Maryam tayi ma security magana suka sallami mutanen Hajiyar ta koma cikin Mota, duk yadda ta daure saida ta matse ƙwalla motocin suka tafi anata cigaba da ɗaga ma Hajiyar hannu, mutane rahama ko iya haka za'a iya cewa Hajiya ta dace. Hajiya ta tafi ta bar mutane da kewa ba kamar su Tk don tun bayan tafiyarta yake ta zazza6i bawan Allah don ma Allah yasa yana da mata tanata aikin rarrashin shi duk da itama sosae take kewar Hajiya don ba ƙaramin shaƙuwa sukai ba ita kanta ɗiyar su Hauwa'u duk ta damu ko yaushe cikin tambayar yaushe Hajiyarsu zata dawo take sai an kira mata ita ta waya sunyi magana ko Vedio call take kwantar da hankalinta, ta bangaren Saude ma taso tafiya Daura bayan tafiyar Hajiya Officer ya rarrasheta kan tayi haƙuri tunda Hajiya tace zata nema mashi transfer sai su koma can baki ɗaya da haka ya samu ta haƙura, su Gwaggo ma duk sun yi kewar Hajiyar duk da su bama gida daya suke da ita ba amman da sun zauna suna hira sai sun yi maganarta, sai bayan wani lokaci Tk ya warware amman ko yaushe cikin jin kewar Hajiyar shi yake.
Bayan komawar Hajiya Abuja da yan watanni Allah ya sauki Farha ta haiho san6aleliyar ɗiyarta mace kai kace ɗiyar aljanu ce don kyau gaba ɗaya mamanta da babanta ta biyo, a fuska da Kamalu take kama amman farinta na Farha ne sannan ƙwayar idonta ma ta Farha ce gashin kanta kuma baƙi ne wuluk kalar na babanta, cikin sa'a lokacin da akai haihuwar su Fatuu na hutu hakan ba ƙaramin daɗi yay masu ba, kowa ya ga Babyn sai ya furta ma sha Allah ana ta farinciki Hajiya Maryam ma lokacin data ga Babyn sam kasa rufe bakinta tay sai farin ciki take, bayan sun koma gida daga asibiti da daddare Lokacin da Kamal ya shiga wurin maijegon yana ruƙe da babyn yake sanar mata da sunan da yake son sakamata wato sunan Hajiya Maryam Farhar tace mashi ba gara yasa sunan late Mom ɗin shi ba yace mata tunda Fatuu tasa su bari in ta ƙara haihuwa sai su saka sunan Mom ɗin nashi, harda yar harararshi tayi tace ita wannan wahalar da tasha ta gama haihuwa yana murmushi tare da yi mata kallo mai cike da tsantsar ƙauna yace tayi haƙuri pls ta ƙara mashi yana son su haifi yara tare, itama murmushin tayi ta kai idonta kanshi tana mashi kallon love tace indai irin yaran nan zata rinƙa haifa tare dashi to zata ƙara wasu Amman sai ta huta sosae yay murmushin shi mai burgewa tare da jinjina mata kai alamar amincewa da zancenta tana murmushi ta kwantar da kanta a kan shoulder dinshi tana kallon Kyakkyawar Babyn su tana haka taji ya furta "Thank you my lovely wife for loving me for who i am" ɗago kai tayi ta kalle shi ta kashe mashi ido tare da furta "i will always love u Babe" yadda tayi maganar har sai da ɗumin bakin ta ya bugi fuskarshi saboda kusancin da fuskokin nasu suke dashi, shiru sukai suna kallon juna wani lokacin har mamaki Kamal yake a cikin ranshi irin yadda take nuna mashi ƙauna bata ƙi a ce koda yaushe suna manne da juna ba, a iya zaman da sukai matsayin ma'aurata ba ƙaramar zazzafar soyayya ta nuna mashi ba hakan yasa shima yake ƙokari wurin faranta mata a koda yaushe bai ta6a yin wani abu da zai nuna ta takura mashi ba zaman su suke lafiya sam baida matsala da ita kawai dai tana da zafin kishi wannan kuma tun kafin suyi auren ya sani shiyasa yake taka tsantsan da duk abunda yasan zai haifar masu da matsala, lokacin da Hajiya Maryam taji sunanta aka saka ma jaririyar murnarta ninkuwa tayi jin anyi mata takwara, bayan kwana biyar da yin haihuwar aka maida maijegon Villa don acan za'ayi suna, saida Hajiya Maryam tayi ma jaririyar saitin akwatuna ukku masu guda huɗu haɗaɗɗun gaske shaƙe da kayan jarirai na gani na faɗa da sauran kuma abubuwan da suka danganci jarirai ita kanta mai jegon ita tayi mata kayan da zata fita suna harda shi ma Baban jaririyar tayi mashi ɗinkuna na alfarma abun dai gwanin daɗi, ranar suna ta kama Juma'a suna na gani na faɗa akayi a Villa maijego ta samu iyayen kaya ita da Baby, mai girma shugaban ƙasa kyautar ƙaton fili yay ma jaririyar haka dai aka cika su da abubuwan arzuƙi kowa yayi bajinta su Gwaggo da Haulat harda Kawu Amadu da Tk da matarshi duk sun zo suna, zo kaga farincikin ganin juna wurin Hajiya da Tk harda rungume shi tayi, suna yayi suna abun sai son barka bayan gama sunan anan Villa apartment ɗin da Hajiya Maryam take Farha ta zauna sai ta gama wanka zata koma.
Bayan komawar Hajiya Abuja da yan watanni Allah ya sauki Farha ta haiho san6aleliyar ɗiyarta mace kai kace ɗiyar aljanu ce don kyau gaba ɗaya mamanta da babanta ta biyo, a fuska da Kamalu take kama amman farinta na Farha ne sannan ƙwayar idonta ma ta Farha ce gashin kanta kuma baƙi ne wuluk kalar na babanta, cikin sa'a lokacin da akai haihuwar su Fatuu na hutu hakan ba ƙaramin daɗi yay masu ba, kowa ya ga Babyn sai ya furta ma sha Allah ana ta farinciki Hajiya Maryam ma lokacin data ga Babyn sam kasa rufe bakinta tay sai farin ciki take, bayan sun koma gida daga asibiti da daddare Lokacin da Kamal ya shiga wurin maijegon yana ruƙe da babyn yake sanar mata da sunan da yake son sakamata wato sunan Hajiya Maryam Farhar tace mashi ba gara yasa sunan late Mom ɗin shi ba yace mata tunda Fatuu tasa su bari in ta ƙara haihuwa sai su saka sunan Mom ɗin nashi, harda yar harararshi tayi tace ita wannan wahalar da tasha ta gama haihuwa yana murmushi tare da yi mata kallo mai cike da tsantsar ƙauna yace tayi haƙuri pls ta ƙara mashi yana son su haifi yara tare, itama murmushin tayi ta kai idonta kanshi tana mashi kallon love tace indai irin yaran nan zata rinƙa haifa tare dashi to zata ƙara wasu Amman sai ta huta sosae yay murmushin shi mai burgewa tare da jinjina mata kai alamar amincewa da zancenta tana murmushi ta kwantar da kanta a kan shoulder dinshi tana kallon Kyakkyawar Babyn su tana haka taji ya furta "Thank you my lovely wife for loving me for who i am" ɗago kai tayi ta kalle shi ta kashe mashi ido tare da furta "i will always love u Babe" yadda tayi maganar har sai da ɗumin bakin ta ya bugi fuskarshi saboda kusancin da fuskokin nasu suke dashi, shiru sukai suna kallon juna wani lokacin har mamaki Kamal yake a cikin ranshi irin yadda take nuna mashi ƙauna bata ƙi a ce koda yaushe suna manne da juna ba, a iya zaman da sukai matsayin ma'aurata ba ƙaramar zazzafar soyayya ta nuna mashi ba hakan yasa shima yake ƙokari wurin faranta mata a koda yaushe bai ta6a yin wani abu da zai nuna ta takura mashi ba zaman su suke lafiya sam baida matsala da ita kawai dai tana da zafin kishi wannan kuma tun kafin suyi auren ya sani shiyasa yake taka tsantsan da duk abunda yasan zai haifar masu da matsala, lokacin da Hajiya Maryam taji sunanta aka saka ma jaririyar murnarta ninkuwa tayi jin anyi mata takwara, bayan kwana biyar da yin haihuwar aka maida maijegon Villa don acan za'ayi suna, saida Hajiya Maryam tayi ma jaririyar saitin akwatuna ukku masu guda huɗu haɗaɗɗun gaske shaƙe da kayan jarirai na gani na faɗa da sauran kuma abubuwan da suka danganci jarirai ita kanta mai jegon ita tayi mata kayan da zata fita suna harda shi ma Baban jaririyar tayi mashi ɗinkuna na alfarma abun dai gwanin daɗi, ranar suna ta kama Juma'a suna na gani na faɗa akayi a Villa maijego ta samu iyayen kaya ita da Baby, mai girma shugaban ƙasa kyautar ƙaton fili yay ma jaririyar haka dai aka cika su da abubuwan arzuƙi kowa yayi bajinta su Gwaggo da Haulat harda Kawu Amadu da Tk da matarshi duk sun zo suna, zo kaga farincikin ganin juna wurin Hajiya da Tk harda rungume shi tayi, suna yayi suna abun sai son barka bayan gama sunan anan Villa apartment ɗin da Hajiya Maryam take Farha ta zauna sai ta gama wanka zata koma.