Sashe 43
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"da wa ya buge ki?" taji ya furta, shiru bata bashi amsa ba bata kuma kalle shi ba, ya k'ara furta "am I not asking you?" Sai lokacin ta juyo ta girgiza mashi kai alamar ba kowa, d'age gira yay ya furta "shi wannan d'in na miye?" ta gane kuka yake nufi ta fara motsa baki ta kasa yin magana, ce mata yay kar ta k'ara sa shi ya maimaita mata magana ya k'ara tamke fuska da sauri cikin rawar murya tace mashi yunwa take ji, bin ta yay da wani kallo ganin haka yasa cikin yar in ina tace mashi bata ci Abincin dare ba, ta6e baki ya d'an yi ya janye idanunshi daga barin kallon ta ya koma kallon gaban shi, bin gefen fuskar shi mai d'auke da kwantaccen saje sumar tayi luff tayi da kallo, juyawa yay dama bai datse kopar ba ya fita tana ta kallon shi ya maido kopar ya rufe, maida kanta tayi jikin kujera tay shiru ba abunda take gani sai fuskar shi, bayan wasu yan mintuna taji za'a bud'e Motar da sauri ta kai idonta, shine ya bud'e ya shigo hannun shi ruk'e da abu, bayan ya zauna ya mik'a mata d'an babban cake ne nad'e a leda sai lemu irin na cikin kaman d'an cup da straw manne a jikinshi, a hankali tayi mashi godiya bai ko kalle ta ba ya maida kan shi jikin headrest, ruk'e su tay a hannu bata da niyyar fara sha sai yan kame kame take tana haka taji yace zasu kwana ana ne, abu ta had'iya kafin ta fara k'ok'arin ciro straw d'in jiki, bayan ta saka a cikin lemun ta bud'e cake d'in ta fara ci tana yi tana satar kallon shi, bayan ta d'an ci da yawa ta rage sauran duka a hankali ta juya ta kalle shi ya d'age kan shi idanun shi a rufe, bin fuskar shi tay da kallo Idan tace ga wani abu da bai yi ba a fuskar tashi to kuwa ta shirga babbar k'arya, tana cikin kallon nashi ba tare data ankara ba ya bud'e idanun ya kallo ta, in ina ta kama yi tace mashi ta gama ya kallo sauran data rage a hannunta ba tare da ya d'ago ba kawai sai gani tay ya maida idanun ya rufe, bayan d'an lokaci taji yace "Don't waste my time, else zan barki anan ne" ai tana jin Haka da sauri ta kai lemun baki taci gaba da sha, saida ta cinye komai sannan ta kalle shi tace ta gama shiru kaman bai jita ba ta k'ara d'an d'aga murya ta maimaita ta gama, slowly ya fara bud'e idon ya d'ago daga jikin kujerar ya fara k'ok'arin tashin Motar yana haka yace mata wannan d'in wani zata kai mawa ta d'an girgiza kai kafin tace bata san ina ake aje wa ba ya juyo yay mata wani kallo da sauri ta juya ta bud'e kopar ta wurga ledar da d'an cup d'in, rufe kopar yay daga haka ya fara yin reverse bayan ya fita daga wurin ya shiga juya kan Motar Fauzyn nata kallon wurin har lokacin da mutane kusan ma yafi cika yanzu.
Lokacin da suka iso gidan kusan k'arfe d'aya da rabi, a bakin Entry Hall ya parker Motar Fauzy ta bi shi da ido gudun kada tayi wani laifin, shiru kaman ba zai tanka ba can yace "Get out of my car" juyawa tay zata fita sai kuma ta dakata ta juya a d'arare tace mashi don Allah ya bata wayar kawar tata ta kai mata, sai da ya mula sannan ya kai hannu ya bud'e wurin da ya saka ba tare daya kalleta ba yace ta d'aukko, hannunta har d'an rawa yake ta kai shi ta d'aukko ta Fatun kawae a fusace yace waye ta bar ma d'ayar ta sake kai hannu ta d'aukko, d'an kallon shi tay tayi mashi godiya yay banza da ita jiki a sanyaye ta juya zata bud'e k'opar kaman daga sama taji yace ta sani dole zata biya shi damage d'in da tay ma wayar shi, juyowa tay fuska a yamutse tace "Don Allah kayi hakuri...Na fad'i maka wllh Allah ba zan iya biyan ka ba, d'age shoulder yay alamar bai dame shi ba kafin yace ta fita, bud'e k'opar tay bayan ta fita ta juyo idonta a kanshi ta kai hannu ta rufe mashi, nufar shiga cikin gidan tay tana yi tana waiwayen shi har saida ta kusa shigewa sannan taga ya ja Motar,
Lokacin da ta shiga main parlor d'in tsit kowa yayi bacci, kopar baya ta nufa tana waige waige tsoron ta kar wani ya ganta ta dawo a lokacin duk da bata san k'arfe nawa ba amman daga yanayin da ta ga garin ta fahimci dare yayi sosae, har ta fita baya ko motsin mutum bata ji ba ta nufi part d'in da suke, lokacin data shiga cikin parlon kwalam yake da sauri ta nufi d'akin su, sai da tay d'an jimm kafin ta sa hannu a hankali ta d'an tura kopar, d'an lek'awa tay ta hango kowa yayi bacci sannan ta k'arasa tura kopar ta shiga, cikin tafiya mai kaman sand'a don kar tayi sauti wani ya tashi ta nufi cikin d'akin, a bakin gado ta zauna tana kallon su Haulat dake ta shan bacci, maido idon ta tay tana kallon gabanta tayi shiru zuciyarta ta shiga tunano mata dukkan abun da ya faru tsakanin ta da Sameer, tunano lokacin da yake mata magana gab da ita ta shiga yi yadda hucin bakin shi mai had'e da k'amshi ya rink'a bugun fuskarta, kokonton kodai ba giya bace ya sha ta shiga yi wata zuciyar ta raya mata to ita tasan yadda giyar take ne ai k'ilan kala kala ce akwae mai kamshi, tunano lokacin da ya kawo fuskar shi ya had'e da tata tayi har bata san lokacin data rufe ido ba sai kuma ta bud'e da sauri kawae sai ta saki murmushi, wasi wasi ta shiga yi na inda ta amince mashin da gaske zai yi mata wani abu ko kuwa, wata zuciyar ta k'ara raya mata kawai dae k'ilan hakanan yay mata hakan amman ai bata kai yayi hakan da ita ba in ma yana yin, har saida ta d'an ta6e baki, tunanin ko mi yaje yi a wannan wurin ta shiga yi tana raya wurin kaman Club a yadda ta fahimta kuma dai tasan ana cewa ba abun arzik'i ake ba a can, a hankali a fili ta furta "ko ma ina ruwa na" ajiyar zuciya ta sauke ita kanta tasan ba K'aramin firgici ya sata ba, tunanin ko ya yafe mata ko kuwa da gasken yake sai ta biya shin kamar yadda ya fad'a mata yanzu da suka dawo ta shiga yi can ta ta6e baki a fili ta furta "ni dai ai na fad'a mashi gaskiya bansan taya zan biya shi ba kuma" shiru tay tana kallon wuri guda can tay murmushi tunowa da abubuwan daya kawo mata taci ta raya ashe yana da kirki, kunna wayoyin tayi gaba d'aya nan taga ashe a fly mode yasa wayarta ta raya k'ilan ma Aunty Mareeya ta sake kiran ta, ta d'an d'auki lokaci a zaunen can ta tuna da ko sallar isha bata yi ba ta mik'e ta nufi hanyar toilet bayan ta aje wayoyin, saida tayi wanka ta d'auro alwala ta fito d'aure da kallabin ta, wurin akwatin kayanta ta nufa, doguwar rigar bacci ta fiddo bayan ta saka ta d'aukko Hijab ta wuce inda abun salla yake ta d'aukko ta shimfid'a, bayan ta gama sallar tayi Addu'a anan ta kwanta ba tare data cire Hijab d'in ba, gaba d'aya bacci ya k'aurace ma idanunta tay shiru tana kallon wuri guda can ta rufe su nan take zuciyata ta shiga tunano mata sufar Sameer a haka har bacci ya kwashe ta.
Lokacin da suka iso gidan kusan k'arfe d'aya da rabi, a bakin Entry Hall ya parker Motar Fauzy ta bi shi da ido gudun kada tayi wani laifin, shiru kaman ba zai tanka ba can yace "Get out of my car" juyawa tay zata fita sai kuma ta dakata ta juya a d'arare tace mashi don Allah ya bata wayar kawar tata ta kai mata, sai da ya mula sannan ya kai hannu ya bud'e wurin da ya saka ba tare daya kalleta ba yace ta d'aukko, hannunta har d'an rawa yake ta kai shi ta d'aukko ta Fatun kawae a fusace yace waye ta bar ma d'ayar ta sake kai hannu ta d'aukko, d'an kallon shi tay tayi mashi godiya yay banza da ita jiki a sanyaye ta juya zata bud'e k'opar kaman daga sama taji yace ta sani dole zata biya shi damage d'in da tay ma wayar shi, juyowa tay fuska a yamutse tace "Don Allah kayi hakuri...Na fad'i maka wllh Allah ba zan iya biyan ka ba, d'age shoulder yay alamar bai dame shi ba kafin yace ta fita, bud'e k'opar tay bayan ta fita ta juyo idonta a kanshi ta kai hannu ta rufe mashi, nufar shiga cikin gidan tay tana yi tana waiwayen shi har saida ta kusa shigewa sannan taga ya ja Motar,
Lokacin da ta shiga main parlor d'in tsit kowa yayi bacci, kopar baya ta nufa tana waige waige tsoron ta kar wani ya ganta ta dawo a lokacin duk da bata san k'arfe nawa ba amman daga yanayin da ta ga garin ta fahimci dare yayi sosae, har ta fita baya ko motsin mutum bata ji ba ta nufi part d'in da suke, lokacin data shiga cikin parlon kwalam yake da sauri ta nufi d'akin su, sai da tay d'an jimm kafin ta sa hannu a hankali ta d'an tura kopar, d'an lek'awa tay ta hango kowa yayi bacci sannan ta k'arasa tura kopar ta shiga, cikin tafiya mai kaman sand'a don kar tayi sauti wani ya tashi ta nufi cikin d'akin, a bakin gado ta zauna tana kallon su Haulat dake ta shan bacci, maido idon ta tay tana kallon gabanta tayi shiru zuciyarta ta shiga tunano mata dukkan abun da ya faru tsakanin ta da Sameer, tunano lokacin da yake mata magana gab da ita ta shiga yi yadda hucin bakin shi mai had'e da k'amshi ya rink'a bugun fuskarta, kokonton kodai ba giya bace ya sha ta shiga yi wata zuciyar ta raya mata to ita tasan yadda giyar take ne ai k'ilan kala kala ce akwae mai kamshi, tunano lokacin da ya kawo fuskar shi ya had'e da tata tayi har bata san lokacin data rufe ido ba sai kuma ta bud'e da sauri kawae sai ta saki murmushi, wasi wasi ta shiga yi na inda ta amince mashin da gaske zai yi mata wani abu ko kuwa, wata zuciyar ta k'ara raya mata kawai dae k'ilan hakanan yay mata hakan amman ai bata kai yayi hakan da ita ba in ma yana yin, har saida ta d'an ta6e baki, tunanin ko mi yaje yi a wannan wurin ta shiga yi tana raya wurin kaman Club a yadda ta fahimta kuma dai tasan ana cewa ba abun arzik'i ake ba a can, a hankali a fili ta furta "ko ma ina ruwa na" ajiyar zuciya ta sauke ita kanta tasan ba K'aramin firgici ya sata ba, tunanin ko ya yafe mata ko kuwa da gasken yake sai ta biya shin kamar yadda ya fad'a mata yanzu da suka dawo ta shiga yi can ta ta6e baki a fili ta furta "ni dai ai na fad'a mashi gaskiya bansan taya zan biya shi ba kuma" shiru tay tana kallon wuri guda can tay murmushi tunowa da abubuwan daya kawo mata taci ta raya ashe yana da kirki, kunna wayoyin tayi gaba d'aya nan taga ashe a fly mode yasa wayarta ta raya k'ilan ma Aunty Mareeya ta sake kiran ta, ta d'an d'auki lokaci a zaunen can ta tuna da ko sallar isha bata yi ba ta mik'e ta nufi hanyar toilet bayan ta aje wayoyin, saida tayi wanka ta d'auro alwala ta fito d'aure da kallabin ta, wurin akwatin kayanta ta nufa, doguwar rigar bacci ta fiddo bayan ta saka ta d'aukko Hijab ta wuce inda abun salla yake ta d'aukko ta shimfid'a, bayan ta gama sallar tayi Addu'a anan ta kwanta ba tare data cire Hijab d'in ba, gaba d'aya bacci ya k'aurace ma idanunta tay shiru tana kallon wuri guda can ta rufe su nan take zuciyata ta shiga tunano mata sufar Sameer a haka har bacci ya kwashe ta.