Sashe 132
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tafiya ce ake me cike da kwanciyar hankali daga baya Fauzyn ta sake bayan Fatuu ta rarrasheta Aunty ta kunna masu kallo suna ta yi abun su, lokacin da suka zo Zaria ne Aunty tace ita dai wllh k'ishi take ji yakamata ace ko wace Mota an aje lemuna da ruwa Fatuu tace ko ta tambaye su k'ilan ba'a rasawa tace to, latsa wurin tayi tace pls suna buk'atar ruwa kawai sai ji tayi an bata amsa da ta duba akwae a cikin Fridge, zaro ido Aunty tay ta d'an kakkali cikin Motar ita dai bata ga wani Fridge ba, tambayar su tayi anan bayan fridge d'in yake yace mata eh mana,
"to gaskiya saidai kuyi hak'uri kun d'aukko yar k'auye nidai wllh ban ganshi ba" ta fad'a tana k'ara kallon wurin, suna jiyo d'an sautin dariyar shi kafin yace Ok bari a bud'e masu daga can yana rufe baki kawai sai gani sukai daga d'an kasan dukkan seats d'in gaban ya bud'e har saida Aunty ta d'an firgita hakan saida yaba Fauzy dariya, d'an karamin fridge ne a jikin dukkan seats d'in kowanne akwae lemuna da ruwa harda snacks a ciki, tambayar Aunty akai yanzu ta gani ko tana dariya tace masu eh sai sunyi hak'uri abun ne ya had'u da yar k'auye suna jiyo dariyar shi, gaba d'ayan su lemu da snack suka d'auka suna sha harda Fauzy Aunty nata washe baki tana fad'in ikon Allah ashe da rabon zata shiga Mota fridge da aketa fad'i, suna cikin ci ne tace to wai yanzu kuma in suka zo suna buk'atar toilet fa tunda sun ci abu, kafin wani ya bata amsa ta sake cewa koda yake k'ilan ma ai baza'a rasa toilet d'in ba acikin Motar, dariya taba Fatuu tace "kai Aunty Mareeya sai kace dai wani jirgi" da sauri tace "ai wannan kaman jirgin ce mai tafiya kan titi kiga fa yadda take da abubuwa kar ki mamakin toilet d'in ma akwai nan da mun tambaya kina iya ganin sun ce akwae" Fatuu dai dariya kawai take cikin disasshiyar murya Fauzy tace don Allah sudai kada ta wani tambayi ko akwai toilet tayi mata wani kallo tace "to your Excellency kada inta bada ku ko " tura mata baki Fauzy tayi ba tare data ce komai ba ta kai hannu ta dafa Shoulder d'inta tace "sai faman wani sha man k'amshi kike ko duk don Mujaheed ne?" Kai ta d'an girgiza mata kawai ba tare data ce komai ba, sai dai tun bayan da suka taho ya tsaya mata a rai sai tunanin halin da yake ciki take da kuma abun da ke damunshi ya hautsine haka.
Alhamdulillah sun iso Kaduna Lafiya, government House d'in nan aka nufa dasu dama an shirya nan za'a tsaya a huta kafin a wuce, bayan sun huta an ci Abinci masu salla sun yi suka d'aura tafiyar. Sai bayan sallar Magrib suka iso garin Abuja, tun a gate d'in gidan da aka nufa dasu suka fara shan kallo Fauzy na ganin cikin gidan ta glass ta gane gidan da Sameer ya ta6a kawo ta ne, gaba d'aya Motocin saida aka shiga dasu cikin gidan, bayan duk an parker aka fara fitowa nan fa kowa ya shiga ba idon shi hakkin shi banda wanda suka san gidan da kuma wanda gidan ba abun kallo bane a wurin su, kowa dai cikin yan kawo Amaryar bai hana idon shi hakkin shi ba ta hanyar bin ko ina na gidan da kallo tare da jinjina ma had'uwar shi a cikin zuciya, Aunty na ruk'e da Fauzy suka nufi hanyar shiga cikin gidan kamar yadda aka basu izini suna cikin tafiyar ne k'asa k'asa da murya Aunty tace ma Fauzy nan ne gidan da Sameer ya ta6a kawo ta ko ta d'aga mata kai tace dama tana gani tayi tunanin hakan don taga yayi kaman yadda ta fasalta mata, saida suka zo bakin entrance d'in gidanne PA din Hajiya Zainab wadda da ita akaje bikon Amarya ta d'an dafa kai tace an samu matsala an manta ba'a bada card d'in da za'a bud'e gidan ba Mom ta tambayi to yanzu ya za'ai da sauri tace bari ta kira Her Excellency d'in, su dai su Aunty jugum sukai kowa na Al'ajabin jin sai da kati za'a bud'e kopar, bayan ta kirata itama nuna rashin jin dad'i tayi tace ta manta ta bada card d'in ne amman bari ta bud'e masu daga nan PA d'in tace Ok, hak'uri taba mutane na an barsu a tsaye bayan sun gama wayar tace gashi nan za'a bud'e, ba'a d'au wani lokaci ba suka ji kopar tayi wani d'an sauti PA din tace yauwa gashi nan an bud'e, ba sai na fad'i mamakin yan kawo Amarya ba, ana bud'ewa aka bada izinin a shiga PA d'in na gaba suka fara shigowa cikin passageway d'in, ita kopar falon dake anan k'asa lafiya lou ta bud'e masu ita kafin a shigar da Fauzy saida ta saci kallon hanyar benen da suka hau da Sameer, Jama'a kuzo kuyi kallon parlor mai sunan falo Aljannar duniya kenan, ashe dai yan kawo Amarya basu ga komai ba sai yanzu, wato wani irin tsararre kuma had'addan Falo ne daya jik'u da tsadaddun kayan alatu masu girgiza mutum, iya luntsuma luntsuman Sofas d'in dake cikin shi abun kallo ne ga wani musulmin Carpet dake malale a cikin shi wanda ya hau da kayan cikin Parlon, a tak'aice dai Idan nace zan tsaya bayyana had'uwar parlon to kuwa saidai in hak'ura da zuwa wurin dinner wadda za'a je da daddaren nan ni kuma gaskiya ina son ba idanuna hakkin su don haka na bar ma kowa ya fassalta had'uwar parlon a cikin zuciyar shi saidai nasan duk hasashen mutum ba lalle ya hasasho ainihin yadda yake ba tunda ba zuwa kai ba, gaba d'aya yan kai Amarya sakin baki sukai suna k'are ma falon kallo wasu na jinjina kai yayin da wasu suka kasa rufe baku nan su, ba anan aka sauke su na wani corridor aka nufa dasu sai gasu sun k'ara shigowa wani parlon, duk da bai kai had'uwar na farkon ba amman dai shima ba k'arya ya jiguna komai na cikin shi navy blue da milk ne sosae shima ya tsaru, anan aka sauke su duk suka zazzauna su Mom suka hau yi masu sannu da zuwa cikin washe baki suke amsawa, nuna masu d'akunan da zasu yi amfani dasu aka yi suna ta godiya duk suka tashi don suyi salla, bayan sun gama ne aka kawo masu lafiyayyen Abinci da lemuna aka sanar dasu in sun gama za'a tafi dinner suyi shiri lokacin Mom ta shigo tayi masu sallama tace zasu je suyi shirin dinner aka shiga k'ara yi mata godiya tanata fara'a take amsawa Fatuu ma sallama tayi masu Saboda kayan da zata saka suna can gidan tace ma Fauzy sai sun had'u wurin dinner d'in, bayan sun huta ne PA tazo da wadda zata yi ma Fauzy kwalliya harda kayan da zata saka ba 6ata lokaci aka fara. K'arfe goma saura aka zo d'aukar su ba'a bar kowa ba Amarya Fauzy ta sha kyau ba k'arya wani rantsattsan material ne golden brown aka yi mata fitted gown data hau jikinta sosae, lokacin da suka isa wurin dinner d'in shima dai ya had'u over da gani Naira ta sha kuka wurin tsara Hall d'in, tunda aka fara hidiman bikin Fauzy bata ga Sameer ba sai yanzu a wurin dinner d'in shima dai ya had'u sosae yana sanye da bugaggun Suit da suka hau da shigar Fauzyn, zuwa k'arfe goma da rabi kowa ya hallara har da uwar ango wato Hajiya Zainab tazo wurin, manyan mutane aka had'a a wurin hakan yasa ko ina ka juya jami'an tsaro ne mata da maza sosae aka zo kasantuwar wannan ce hidimar su ta farko, ba'a yi tak'amaimai anko guda ba gaba d'aya kowa da kalar wanda sukai saidae gaba d'aya lace ne aka saka kamar yan gidan su Haisam kalar lace din su d'aya haka ta bangaren su Sameer suma kalar nasu daban har kakar su ta zo da sauran dangin su yan Ethiopia haka yan Qatar ma sun zo, su Aunty Mareeya da sauran yan gidansu suma lace d'in su daban haka dai duk akayi ankon wasu kuma lace d'in su ne suka saka daban kamar su gwaggo da Aunty Feenah da Haulat dasu Zainab kowa lace d'in shi ya saka amman ita Mino irin nasu Fatuu ta saka ita ta d'inka mata Nameer dai bai samu zuwa ba don yana gab da fara yin Final Exams d'in shi, sosae kowa yayi kyau angwaye ma su Haisam duk wankan Suit sukai, ba 6ata lokaci aka shiga aiwatar da activities d'in dinner d'in abun gwanin k'ayatarwa. Gab da za'a tashi ne aka rarraba wata k'atuwar jaka mai d'auke da hoton Fauzy da Sameer cikinta uban souvenirs ne iri iri Aunty Mareeya aka ba na dangin su ta rarraba masu sauran da suka rage ta yanke aika ma Mamar su, Sai wurin k'arfe d'aya saura aka tashi abun sai godiyar Allah don an ci an sha an nishadantu yadda yakamata dinner ce da zata tsaya ma mutane a rai Aunty Mareeya dai taci uwar sabada kamar yadda ta ci alwashi kowa ka gani san barka yake dangin su Fauzy sai k'ara tayata murnar samun Sameer a matsayin miji suke ana ta fad'in ta dace ba kamar k'awayenta kowa jinjina irin rabon da take da shi suke, daga baya aka kwashe kowa aka maida su gida su Hajiya Zainab wani gidan nasu daban suka sauka wanda aka sauke su Fauzy kuma aka bar masu sai masu kula dasu.
"to gaskiya saidai kuyi hak'uri kun d'aukko yar k'auye nidai wllh ban ganshi ba" ta fad'a tana k'ara kallon wurin, suna jiyo d'an sautin dariyar shi kafin yace Ok bari a bud'e masu daga can yana rufe baki kawai sai gani sukai daga d'an kasan dukkan seats d'in gaban ya bud'e har saida Aunty ta d'an firgita hakan saida yaba Fauzy dariya, d'an karamin fridge ne a jikin dukkan seats d'in kowanne akwae lemuna da ruwa harda snacks a ciki, tambayar Aunty akai yanzu ta gani ko tana dariya tace masu eh sai sunyi hak'uri abun ne ya had'u da yar k'auye suna jiyo dariyar shi, gaba d'ayan su lemu da snack suka d'auka suna sha harda Fauzy Aunty nata washe baki tana fad'in ikon Allah ashe da rabon zata shiga Mota fridge da aketa fad'i, suna cikin ci ne tace to wai yanzu kuma in suka zo suna buk'atar toilet fa tunda sun ci abu, kafin wani ya bata amsa ta sake cewa koda yake k'ilan ma ai baza'a rasa toilet d'in ba acikin Motar, dariya taba Fatuu tace "kai Aunty Mareeya sai kace dai wani jirgi" da sauri tace "ai wannan kaman jirgin ce mai tafiya kan titi kiga fa yadda take da abubuwa kar ki mamakin toilet d'in ma akwai nan da mun tambaya kina iya ganin sun ce akwae" Fatuu dai dariya kawai take cikin disasshiyar murya Fauzy tace don Allah sudai kada ta wani tambayi ko akwai toilet tayi mata wani kallo tace "to your Excellency kada inta bada ku ko " tura mata baki Fauzy tayi ba tare data ce komai ba ta kai hannu ta dafa Shoulder d'inta tace "sai faman wani sha man k'amshi kike ko duk don Mujaheed ne?" Kai ta d'an girgiza mata kawai ba tare data ce komai ba, sai dai tun bayan da suka taho ya tsaya mata a rai sai tunanin halin da yake ciki take da kuma abun da ke damunshi ya hautsine haka.
Alhamdulillah sun iso Kaduna Lafiya, government House d'in nan aka nufa dasu dama an shirya nan za'a tsaya a huta kafin a wuce, bayan sun huta an ci Abinci masu salla sun yi suka d'aura tafiyar. Sai bayan sallar Magrib suka iso garin Abuja, tun a gate d'in gidan da aka nufa dasu suka fara shan kallo Fauzy na ganin cikin gidan ta glass ta gane gidan da Sameer ya ta6a kawo ta ne, gaba d'aya Motocin saida aka shiga dasu cikin gidan, bayan duk an parker aka fara fitowa nan fa kowa ya shiga ba idon shi hakkin shi banda wanda suka san gidan da kuma wanda gidan ba abun kallo bane a wurin su, kowa dai cikin yan kawo Amaryar bai hana idon shi hakkin shi ba ta hanyar bin ko ina na gidan da kallo tare da jinjina ma had'uwar shi a cikin zuciya, Aunty na ruk'e da Fauzy suka nufi hanyar shiga cikin gidan kamar yadda aka basu izini suna cikin tafiyar ne k'asa k'asa da murya Aunty tace ma Fauzy nan ne gidan da Sameer ya ta6a kawo ta ko ta d'aga mata kai tace dama tana gani tayi tunanin hakan don taga yayi kaman yadda ta fasalta mata, saida suka zo bakin entrance d'in gidanne PA din Hajiya Zainab wadda da ita akaje bikon Amarya ta d'an dafa kai tace an samu matsala an manta ba'a bada card d'in da za'a bud'e gidan ba Mom ta tambayi to yanzu ya za'ai da sauri tace bari ta kira Her Excellency d'in, su dai su Aunty jugum sukai kowa na Al'ajabin jin sai da kati za'a bud'e kopar, bayan ta kirata itama nuna rashin jin dad'i tayi tace ta manta ta bada card d'in ne amman bari ta bud'e masu daga nan PA d'in tace Ok, hak'uri taba mutane na an barsu a tsaye bayan sun gama wayar tace gashi nan za'a bud'e, ba'a d'au wani lokaci ba suka ji kopar tayi wani d'an sauti PA din tace yauwa gashi nan an bud'e, ba sai na fad'i mamakin yan kawo Amarya ba, ana bud'ewa aka bada izinin a shiga PA d'in na gaba suka fara shigowa cikin passageway d'in, ita kopar falon dake anan k'asa lafiya lou ta bud'e masu ita kafin a shigar da Fauzy saida ta saci kallon hanyar benen da suka hau da Sameer, Jama'a kuzo kuyi kallon parlor mai sunan falo Aljannar duniya kenan, ashe dai yan kawo Amarya basu ga komai ba sai yanzu, wato wani irin tsararre kuma had'addan Falo ne daya jik'u da tsadaddun kayan alatu masu girgiza mutum, iya luntsuma luntsuman Sofas d'in dake cikin shi abun kallo ne ga wani musulmin Carpet dake malale a cikin shi wanda ya hau da kayan cikin Parlon, a tak'aice dai Idan nace zan tsaya bayyana had'uwar parlon to kuwa saidai in hak'ura da zuwa wurin dinner wadda za'a je da daddaren nan ni kuma gaskiya ina son ba idanuna hakkin su don haka na bar ma kowa ya fassalta had'uwar parlon a cikin zuciyar shi saidai nasan duk hasashen mutum ba lalle ya hasasho ainihin yadda yake ba tunda ba zuwa kai ba, gaba d'aya yan kai Amarya sakin baki sukai suna k'are ma falon kallo wasu na jinjina kai yayin da wasu suka kasa rufe baku nan su, ba anan aka sauke su na wani corridor aka nufa dasu sai gasu sun k'ara shigowa wani parlon, duk da bai kai had'uwar na farkon ba amman dai shima ba k'arya ya jiguna komai na cikin shi navy blue da milk ne sosae shima ya tsaru, anan aka sauke su duk suka zazzauna su Mom suka hau yi masu sannu da zuwa cikin washe baki suke amsawa, nuna masu d'akunan da zasu yi amfani dasu aka yi suna ta godiya duk suka tashi don suyi salla, bayan sun gama ne aka kawo masu lafiyayyen Abinci da lemuna aka sanar dasu in sun gama za'a tafi dinner suyi shiri lokacin Mom ta shigo tayi masu sallama tace zasu je suyi shirin dinner aka shiga k'ara yi mata godiya tanata fara'a take amsawa Fatuu ma sallama tayi masu Saboda kayan da zata saka suna can gidan tace ma Fauzy sai sun had'u wurin dinner d'in, bayan sun huta ne PA tazo da wadda zata yi ma Fauzy kwalliya harda kayan da zata saka ba 6ata lokaci aka fara. K'arfe goma saura aka zo d'aukar su ba'a bar kowa ba Amarya Fauzy ta sha kyau ba k'arya wani rantsattsan material ne golden brown aka yi mata fitted gown data hau jikinta sosae, lokacin da suka isa wurin dinner d'in shima dai ya had'u over da gani Naira ta sha kuka wurin tsara Hall d'in, tunda aka fara hidiman bikin Fauzy bata ga Sameer ba sai yanzu a wurin dinner d'in shima dai ya had'u sosae yana sanye da bugaggun Suit da suka hau da shigar Fauzyn, zuwa k'arfe goma da rabi kowa ya hallara har da uwar ango wato Hajiya Zainab tazo wurin, manyan mutane aka had'a a wurin hakan yasa ko ina ka juya jami'an tsaro ne mata da maza sosae aka zo kasantuwar wannan ce hidimar su ta farko, ba'a yi tak'amaimai anko guda ba gaba d'aya kowa da kalar wanda sukai saidae gaba d'aya lace ne aka saka kamar yan gidan su Haisam kalar lace din su d'aya haka ta bangaren su Sameer suma kalar nasu daban har kakar su ta zo da sauran dangin su yan Ethiopia haka yan Qatar ma sun zo, su Aunty Mareeya da sauran yan gidansu suma lace d'in su daban haka dai duk akayi ankon wasu kuma lace d'in su ne suka saka daban kamar su gwaggo da Aunty Feenah da Haulat dasu Zainab kowa lace d'in shi ya saka amman ita Mino irin nasu Fatuu ta saka ita ta d'inka mata Nameer dai bai samu zuwa ba don yana gab da fara yin Final Exams d'in shi, sosae kowa yayi kyau angwaye ma su Haisam duk wankan Suit sukai, ba 6ata lokaci aka shiga aiwatar da activities d'in dinner d'in abun gwanin k'ayatarwa. Gab da za'a tashi ne aka rarraba wata k'atuwar jaka mai d'auke da hoton Fauzy da Sameer cikinta uban souvenirs ne iri iri Aunty Mareeya aka ba na dangin su ta rarraba masu sauran da suka rage ta yanke aika ma Mamar su, Sai wurin k'arfe d'aya saura aka tashi abun sai godiyar Allah don an ci an sha an nishadantu yadda yakamata dinner ce da zata tsaya ma mutane a rai Aunty Mareeya dai taci uwar sabada kamar yadda ta ci alwashi kowa ka gani san barka yake dangin su Fauzy sai k'ara tayata murnar samun Sameer a matsayin miji suke ana ta fad'in ta dace ba kamar k'awayenta kowa jinjina irin rabon da take da shi suke, daga baya aka kwashe kowa aka maida su gida su Hajiya Zainab wani gidan nasu daban suka sauka wanda aka sauke su Fauzy kuma aka bar masu sai masu kula dasu.