← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 77 OF 211

Sashe 77

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan fitowar shi part d'in Aunty ya nufa lokacin tana cikin d'aki ta koma ta kwanta da yake saida rana zata aiki, tana kishingid'e jikinta sanye da jallabiya kanta a bud'e yasha k'ananun kitso hannunta ruk'e da waya tana amsa kiran da shi ya tashe ta daga bacci ya shigo cikin d'akin da sallama, saida ta cire wayar sannan ta amsa mashi, nufar gadon yay ya zauna ta tashi da sauri tace ma wadda suke wayar tana zuwa, kallon shi tay da murmushi tay mashi barka da shigowa da yake a part d'in shi ta kwana sun gaisa, bayan ya amsa mata ne yay mata Maganar Fatuu yace yana son ta dubata taga in ba wata matsala zasu koma tare da Hajiya, a nutse ta fara mashi bayanin cewa a yanzu dai gaskiya lafiyar Fatun lau don tana duba ta akai akai ba wata matsala a tattare da ita sannan shi miscarriage yana iya faruwa unexpectedly koda ana kiyayewa wani lokacin hakanan ma sai ayi ita abunda take gani a barta ta bita sai a bita da Addu'a kawai tunda barin nata k'arshe zai jefa ta a damuwa ne kuma hakan ma had'ari ne a gareta, sosae tayi mashi bayani tare da nuna mashi duk abunda Allah ya k'addaro sai ya faru duk da kiyayewar nada kyau har ta bashi misali da zuwan su akwae cikin jikinta kuma k'arami ma sosae haka suka hawo jirgi kuma lafiya lou, sosae ya fahimta daga baya ya tafi.

A ranar da daddare lokacin da ya kawo masu Fura Hajiya na zaune tare da Fatuu a parlor tana zaune akan kujera 3 seater ta haye saman ta gaba d'aya ta mik'ar da k'afafu gefenta bowl d'in Fruit ne tana ta sha dama bata dad'e da gama cin Abincin dare na biyu ba, da sallama ya shigo da sauri Fatun ta fara k'ok'arin gyara zama ya d'aga mata hannu yace tayi zaman ta, a kujerar kusa da Hajiya ya zauna bayan ya d'aura ledojin furan kan c-table, gaisawa sukai da Hajiyar Fatuu ma ta gaishe da shi ya amsa yana mata murmushi, juyawa yay kan Hajiya yace mata in Allah ya kaimu ranar Friday zasu tafi ta d'aga mashi kai tace Allah ya kaimu, maido idon shi yay kan Fatuu dake kallon su yace "Daughter sai a shirya in Allah ya kaimu ranar Friday zaku tafi" ba shiri ta washe baki duk dimples d'inta suka lotsa dama ga kumatun sunyi Tubarkallah da sauri takai duka tafukan hannuwanta ta rufe fuska alamar taji kunya duk sukai dariya, Maganar akwatunan ta Hajiya tay ma Senator yace ba matsala zuwa kafin su tafi za'a yi gaba da su. Tun daren Fatuu ta fara had'a kaya a ranar kwanan farinciki tayi.

FRIDAY

Akace komai aka sa ma rana zai zo har ma ya wuce, cike da Nishad'i Fatuu ta tashi har Fuskarta ta kasa 6oye farincikin da take ciki na tafiyar su yau ba kamar da Haisam ya sanar mata da sun koma zai zo, gaba d'aya ta gama shiryawa lokacin tafiya kawai take jira dama tun jiya Alhamis aka tafin mata da dukkan kayanta iya yar jakar kayan da zata yi amfani dasu ce zata d'auka haka Hajiya ma an tafin mata da akwatin ta iya yar jaka ce ta rage mata, da yake Friday ne da wuri yaran gidan suka dawo daga Makaranta bayan an saukko daga Masallaci a tare gaba d'aya suka ci Abincin rana a dining table kowa yaci gayun Juma'a, bayan sun gama cikin parlor suka koma harda Dad aka hau yin hirar bakwana dasu Hajiya har Jidderh na cewa ba don Makaranta ba wllh da bin su zatai taje tayi rainon Baby duk akayi dariya Mom tace da yake yazo duniya ko, Aunty ma cewa tay tana ganin Idan cikin ya kai wata takwas kamata yay ta dawo nan Abuja ta Haihu duk kowa yace haka yakamata ita dae Fatuu murmushi kawai take a k'agare take da su tafi har gani take Lokacin ma bai gudu, sai da akai La'asar sannan duk suka tashi don yin salla daga an gama kuma za'a tafi rakasu Airport..............

_Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268

89

~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~

.........Wuraren k'arfe biyar da rabi jirgin su Fatuu ya sauka a Airport d'in Katsina, Kawu Amadu da Tk da Mino ne suka zo tarbar su, Mino na sanye da riga da skirt na atampa ta yafa gyale a saman kanta sumarta a fake daga bayan kan yayi tudu sosae, gaba d'aya a k'agare take da taga Adda Fatuu din ta, lokacin da suka k'araso cikin Arrivals d'in Fatuu na sanye da Dubai Abaya fara Sol tasha adon stones tayi rolling veil d'in ta hannuwan ta sanye da yan hannunta na diamond da zobe sai k'afafun ta na sanye da takalma brown da suka hau da kalar aikin gaban rigar masu d'an tudu ne don Hajiya ta hanata saka masu tsini, in ka kalleta sai ka rantse bata san hanyar ruga ba balle har ayi zancen acan aka haifeta don gaba d'aya in ka ganta sai kace ba yar Nigeria ba ce ko kuma ace ruwa biyu, Hajiya ma na sanye da doguwar riga mai had'e da mayafi idanunta sanye cikin glasses, akan idon Mino suka shigo aikuwa da sauri ta mik'e ta nufe su da gudu Fatuu na hango su ta fara sakin murmushi, tana zuwa gaba d'aya ta tafi zata fad'a ma Fatun Hajiya tace "a hankali dai Ameenatu" hakan yasa ta dakata a gaban Fatun tana ta washe baki, hannu Fatuu ta kawo ta d'an rungumo ta bayan ta d'ago da ita tay mata sannu da zuwa tana ta murmushi ta amsa mata ta juya kan Hajiya ta gaishe da ita itama da murmushi akan Fuskarta ta amsa mata, lokacin su Kawu Amadu da Tk suka k'araso duk suna sanye da k'ananun kaya, gaishe da Hajiya sukai bayan ta amsa sukai mata an dawo lafiya kafin suka maida idanun su akan Fatuu, Tk na k'ok'arin gaishe da ita da riga shi gaishe dasu duk suka amsa sukai mata an dawo lafiya, bayan sun gama yan gaishe gaishen Tk ya amshi jakar Hajiya ita kuma Mino ta amshi ta Fatuu a tare suka nufi barin wurin sam Mino ta kasa rufe bakinta sai faman juyawa take tana kallon Fatuu da gaba d'aya ta canza mata, inda sukai parking Mota suka nufa daidai lokacin Fauzy ta k'araso cikin Keke Napep, fitowa tay tana sanye da doguwar rigar material tayi rolling bak'in veil a kanta bayan ta biya mai Napep d'in tana juyowa ta hango su Fatun cikin d'an d'aga murya ta k'wala mata kira hakan yasa Fatuu dakatawa ta juyo, nufar su tay gaba d'aya sun dakata suna jiran ta k'araso, tana zuwa ta d'an rungumo Fatuu tace "Welcome back Bestie nah" Fatun tayi mata godiya tana ta murmushi, bayan ta d'ago ta juya ta gaishe da Hajiya tare da yi mata sannu da zuwa, kallon su Kawu Amadu dake d'an murmushi tay suma tay masu sannu da zuwa Mino ma ta gaishe da ita ta amsa da fara'a, maida idon ta tay kan Fatuu da still Murmushi ne akan fuskarta ta kai hannu ta d'an ja kumatunta ta furta "Wannan kumatu haka da kika aje Tubarkallah ko dai ke kike cinye Abincin gidan ne" tana rufe baki Hajiya ta bata amsa da "kamar kin sani" duk sukai dariya, ce masu Hajiya tayi su je a k'arasa gaisawa a gida duk suka juya, ganin Motar kamar bazata ishe su ba yasa Fauzy cewa bari ta samu Napep sai ta bi bayan su Kawu Amadu yace lafiya lou zata isa bari su zauna a gaba shi da Mino, bayan duk sun shiga cikin Motar Hajiya da Fatuu da Fauzy ne a baya suka tafi.

Lokacin da suka iso Unguwar su suna zuwa gab da gida Mino ta kira Gwaggo a waya ta sanar mata gasu sun dawo don da harda ita za'aje tarbar su to sai taga Motar bazata isa ba in aka d'aukko su hakan yasa ta fasa zuwa tace masu in sun dawo sai su sanar mata, A daidai bakin gate Motar ta tsaya su Officer suka taso da sauri suka zo bakin Motar aka zuge glass d'in cikin washe baki suka hau yi masu sannu da zuwa duk suka amsa, bayan an zuge gate d'in suka kutsa cikin gidan, part d'in Hajiya ya tunkara tace mashi ya kaisu cikin parking space kawai yadda ba sai yasha wahalar maido Motar ba tama mik'ar da k'afafunta, lokacin daya parker Motar Officer Jamil mijin Saude ya k'araso da sauri ya bud'e k'opar side d'in da Hajiya take Fauzy ta bud'e ta d'ayan side d'in haka su Kawo Amadu ma duk suka firfito, k'ara gaishe da Hajiya Officer yay cikin washe baki tayi mashi ya aiki ya amsa da Alhamdulillah kafin yace sun yi kewarta sosae cikin Fara'a tace "to ai gani na dawo kewa ta k'are ko" yana yar dariya yace hakane, kallon Fatuu yay ya yi mata ya jiki tace Alhamdulillah, tambayar akwai kaya yayi Hajiya tace mashi ba wasu kaya duk anyo gaba dasu ya je kawai yace to tare da yi masu Allah ya huta gajiya ya nufi komawa gate,
Chapter 77 · 0% Book details