← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 121 OF 211

Sashe 121

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Not now" shine abunda taji ya fad'a ta gyad'a kai, cigaba da kallon juna sukai tana ta mashi murmushi shima fuskar shi a d'an sake can ya kai hannu ya shafi forehead d'in shi bayan ya ciro hannun ya d'an yi yar hamma, tambayar ta yay har yanzu jin muryar nashi bai isheta bane yana son yayi bacci yadda yay Maganar har saida ya bata dariya cikin wasa tace "ai bata isa na in ina jinta ban k'i ma mu kwana ba inata jinta" d'an wara ido yay ya tambayi is she serious ta d'aga mashi kai kafin tace ko ba zai iya kwana yana hira da ita ba , shiru ya d'an yi yana kallonta kafin yace to mi zai sa su kwana suna magana ai sai Maganan ma ta k'are tana yar dariya tace ba gashi yanzu ma sun d'auki lokaci suna hira ba kuma maganan bata k'are ba ai haka hiran love yake in ana yi ba'a gajiya, wani kalan kallo Yay mata yace waye ke yin love d'in ta nuna shi sannan ta nuna kanta wani irin kallo yay mata ya furta dama ashe bata ji ko tana dariya tace a'a ita tana ji ai ba k'arya tayi ba love d'in suke taga ya d'an girgiza kai slowly yace shi bai yin love da yarinya jin Haka yasa ta tura mashi baki kaman zatayi kuka tace Don Allah ita ya daina ce mata yarinya kawai sai gani tay ya saki yar dariya har dimple d'in shi ya d'an lotsa dama ya fahimci bata son ya kira ta da yarinya, bin shi tayi da kallo ko k'yaftawa bata yi can ta furta mashi dariya yana k'ara mashi kyau sosae kawai sai gani tayi ya d'aure fuskar yace ta fara raina shi ko ganin yadda yayi Maganar ne yasa da sauri ta girgiza mashi kai tace "taya zan raina ka bacin kai mutum ne mai girma da daraja a wurina wanda yay man alfarmar da ban ta6a zaton zan samu irinta ba a rayuwata, kullum ina son in gode maka amman na rasa taya zan hakan don Kalmar Thank you isn't enough, but I promise you I will be a devoted wife to you, I will make sure I give you all the happiness a wife can give to her husband in sha Allah, ina baka hak'uri in Maganar dana yi ka d'auka raini ce ba haka bane wllh kawai ina jin dad'in in ka sake man muna magana tunda ba cika yi kake ba" yadda ta k'arasa Maganar kamar zata saki kuka, murmushi taga yayi tare da lumshe mata ido a hankali ya furta mata thanks tare da Fad'in yana mata wasa ne kawai, sosae taji dad'i tana ta murmushi tace to yayi mata fatan Allah ya bata ikon yi mashi abunda tace ya d'aga kai kafin yace hakan itama tace mashi thanks, sigh yay ya furta "My devoted wife pls allow me to sleep na gaji sosae" Dariya Fauzy ta saka jin abunda yace shima yar dariyar yayi tace mashi to ya kwanta saida safe Allah ya tsare mata shi harda cewa yayi mafarkinta ya d'aga mata kai ta d'an d'aga hannu tana mashi bye bye daga haka yay disconnect, bayan sun gama wayar d'age kanshi yay a jikin kan gado yana d'an murmushi wani irin nishad'i yake ji tunda yake hira irin haka da mata bai ta6a jin dad'in wata ba kamar wannan lokaci guda yaji ya k'osa su zama ma'aurata don ta kasance a kusa da shi, itama bayan sun gama fad'awa tay saman gado tana murmushin jin dad'i wani kalan nishad'i na ratsa dukkan jikinta don tunda take dashi basu ta6a yin hira ba haka, lumshe ido tay suffar shi na dawo mata nan ta fara imagination d'in sun zama ma'aurata can ta bud'e idanun da sauri tana yar dariya a fili ta shiga yin godiya ga Allah da wannan babbar ni'imar da yayi mata don ko a iya haka sanin Sameer d'in da tayi tasan ni'ima ce, tana ta tunane tunanen shi a haka bacci ya kwashe ta.

Washe gari Misalin k'arfe goma saura masu tafiya nata shiri, bayan Aunty Mareeya ta gama shiryawa ta nufi part d'in su Fatuu, lokacin data je har sunyi wankan safe ta koma ta kwanta saidai ba bacci take ba hira suke da Mino sai Aysha kanwarsu, da sallama ta shigo cikin Bedroom d'in Fatuu na ganinta ta yunk'ura ta tashi zaune tana fad'in sunanta ita kuma tana amsawa tana karasowa wurin gadon, a baki ta zauna Fuskar kowannen su da Murmushi su Mino suka gaishe da ita ta amsa tare da Fad'in har an shirya tace mata eh, gaishe da ita Fatuu tayi ta maido idonta kanta ta amsa tace har anyi wankan safe tace mata eh, kallon su Twins tayi dake cikin gadon su tace suma sun sha wanka suna ta bacci Fatuu tace eh sun sha wankan Kakar su Yadikko Aunty tace ah lalle dole suyi bacci ashe mata ce ta sulle su duk akai yar dariya, tunani Fatuu tay k'ilan ko Maganar da sukai ne tazo fad'i mata tunda dama tace sai tazo Abuja hakan yasa ta kalli Mino da fulatanci tace su d'an basu wuri tace to ta kamo hannun Aysha suka nufi hanyar fita, bayan fitar su ne Aunty Mareeya tace "Yauwa dama kamar kinsan magana nike son muyi duk da dai ma ba wata ta sirri bane ai kan Maganar da muka yi ta gidane, na kira Yayan mu yaje ya samu Baban mu sun tattauna, abunda ke faruwa Zarah gaskiya samun irin gidan da shi Sameer d'in zai so zai yi wuya a garin namu yawancin manyan gidaje duk masu su ne a ciki saidai za'a iya samun sabo wanda ba'a kammala ba sai a ida ginawa to amman irin wannan gaskiya sai a wajen gari haka, to yanzu dai shawarar da aka yanke itace wai ko kawai ayi renovating namu gidan tunda ba laifi d'an babba ne kuma gaskiya ginin shi mai kyau ne don da asali ginin k'asa ne irin na da d'in nan to a hankali lokacin Babanmu na aiki ya fara maida shi na bulon siminti zuwa lokacin daya aje aiki aka gama maida shi gaba d'aya na siminti kinga sai kawai a gyara a yi mashi dai irin adon zamani, kai Fatuu ta jinjina bayan ta gama tace "kuma hakan yayi Aunty Mareeya tunda kun saba da Unguwar gaskiya bazaku ji dad'in barinta ba kuma sai ma a maida shi na bene kawai" d'an zaro ido Aunty tay "na bene kuma Zarah, a'a ba sai anyi wannan uwar dawainiyar ba kar ma aga mun zaqe ki dai fad'a ma mijin naki yadda nace kar ai zancen benen nan" ta k'arasa tana yar dariya Fatun ma ita take yi tace ai da ta bari an fad'i hakan tunda dai yana da halin Aunty Mareeyar ta ce "ke dai kada ayi Maganar benen nan tawajena kinga sun duba mana sosae ban ma fad'i maki ba jiya fa Her Excellency tayi magana dani tace ba sai anyi ma Fauziyya komai ba na aure iya ita suke buk'ata" waro ido tay tace don Allah Aunty tace mata Allah kuwa, sosae Fatuu taji dad'i ta shiga washe baki tana fad'in kamar irin yadda akai mata itama ba'ayi mata komai ba Aunty tace ai yawanci Kusan duk kaddarar su daya da Fauziyya shiyasa Allah ya had'a su Fatuu tace hakane tay fatan Allah ya nuna masu bikin Aunty tace "Amin ya Rabbi, ai wllh a k'agare nike da inga anyi bikin nan ai dole ma ne muci uwar sabada bayan mun yi godiya ga ubangiji" dariya sosae Fatuu ke yi, bayan ta tsagaita tace "wai Aunty ina wannan mayaudarin daya yaudari Fauzy ya kuwa san da Maganar zata yi aure?"

"Oho, wama yasan duniyar da yake nasan gaskiya bai san da Maganar ba don kinsan fa Babanmu ya hana a bud'e Maganar yace a bari sai komai ya tabbata amman yanzu nasan da an fara aikin gidan zaki ga abun ya bayyana" jinjina kai Fatuu tay tace zata so taga fuskar shi ranar daya ji Maganar Aunty tay dariya tace shegen k'ilan har ciwon zuciya sai ya kama shi,

"Yauwa ina son dama in yi maki magana kan gyaran jiki kinsan fa jinin haihuwa na lalata duk wani shiri na jiki don haka dole sai kin k'ara yin sabon gyara" da sauri Fatuu tace eh dama tana son yi mata magana akan hakan, tambayar ta Aunty tay ai har yanzu jinin na zuwa ko tace mata eh ta sake tambayar ta yaushe zasu dawo Katsina ne tunda gama jarabawar su ta k'arshe ta taho tace sunyi magana da Ya Haisam kan hakan bada jimawa ba zata dawo Aunty tace "to abunda za'ai yanzu da mun koma zan tanadar maki masu kyau dama akwai wanda nasa za'a kawo ma Fauziyya daga Nijar don har yanzu ban fara bata komai ba Saboda kinsan in akwae k'ananun shekaru to ba buk'atar asha abubuwa sosae k'arshe yazo ya damu mutum shiyasa na bari sai gab da bikin amman dai ina bata nama mai romo sosae haka su fruit da fresh milk sosae nike sata tana ci Mino ma yakamata ace zuwa yanzu ana bata su sosae duk da dai bansan ko ana hakan ba amman dai zan ma gwaggo magana zuwa lokacin da za'a fara basu magungunan, shiri na musamman za'a yi masu in sha Allah",
Chapter 121 · 0% Book details