Sashe 193
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Bayan komawar President Ali kan mulki da shekara ɗaya da wasu watanni ne Hajiya ta kwanta rashin lafiya, farko daga zazza6i ranar wata lahadi ta tashi da shi bayan tasha magani ta ji ta samu sauƙi, da daddare bayan ta kwanta ciwo ya dawo mata zuwa wayewar gari jikinta yayi zafi sosae lokacin da Tk ya dawo daga Masallaci ya je gaisheta kamar yadda yake yi kullum da ƙyar ta amsa mashi sallama, bayan ya shiga a kwance ya isketa saman carpet tana sanye da Hijab da ƙyar tayi ƙarfin hali tayi Salla, jin yadda ta amsa mashi gaisuwar tana nishi dama gashi ya ganta a kwance ƙasa yasa shi tambayarta kamar bata lafiya tace mashi tun jiya take jin zazza6i sama sama tasha magani to da daddare ya idasa rufeta yanzu ma da ƙyar tayi salla yana jin haka da alamun tashin hankali yace bari ya fiddo Mota su tafi asibiti, batare daya jira jin mi zata ce ba ya miƙe da sauri ya nufi ƙopar fita, bayan ya fito saida ya shiga yayi ma Husnah magana kan taje ta taimaka ma Hajiyar ta shirya sai su tafi asibitin tare, itama hankalinta ya ɗan tashi jin Hajiya ba lafiya don da wuya kaji ciwo ya kwantar da ita kaji dai tana cewa bata jin daɗi, bayan zuwan su Asibitin wanda suke zuwa ba 6ata lokaci aka dubata tare da yi mata aune aune bayan an turo result likita ya yi masu bayanin zazza6in malaria da typhoid ne ke damunta har saida Hajiya ta ɗan yi mamakin jin harda typhoid, da likitan yace ko a bata gado don a dubata sosae ta kuma huta tace a'a adai yi mata abunda ya dace yanzu ta koma gida sai taci gaban da shan magani, bayan anyi mata allura an bata maguguna suka tafi, sai bayan da suka dawo Saude tasan da rashin lafiyar nata nan fa suka shiga bata kulawa kowa ya damu Hajiya ba lafiya Tk yace ko ya kira Haisam ya sanar mashi Hajiyar tace a'a kada a tada masu hankali zata samu sauƙi in sha Allah, Amadu ne ya kira Tk kan ya fito su wuce wurin aiki yaga lokaci na niyyar ƙurewa ya sanar mashi da Hajiya ce ba lafiya, Gwaggo na jin Hajiya ba lafiya suka taho harda Haulat da Amadun, gaba ɗaya duk kowa ya shiga damuwa gashi bata cin abinci sai ɗan abu mai ruwa shima daga baya aman abunda tasha ta fara yi ganin haka yasa tk yace ko su koma asibitin tace mashi a'a dama haka zazza6i yake da naci ai zata samu sauki, wasa wasa saiga ciwo nata gaba maimakon a samu sauƙi cikin kwana biyu sai gashi ya kai komai sai su Saude sun yi mata lokacin da Gwaggo tazo taga halin da take ciki ta tambayi Tk yan Abuja sun san bata lafiyar cikin damuwa yace Hajiyar ta hana a sanar masu Gwaggon tace ai ba biye mata za'ai ba, nan take ta buga ma Haisam waya ta sanar dashi da alamun tashin hankali ya tambayi abunda ke damunta ganin ko jiya sunyi waya da ita amman bai gane bata lafiya ba tayi mashi bayani, ana gama sallar Magrib sai ga Haisam ɗin ya iso Tk ne yaje ya ɗaukko shi tun suna kan hanyar zuwa gidan Dad ɗin shi da Hajiya Maryam suka kira suna tambayar ya isa ya jikin Hajiyar yace masu yana hanyar zuwa gidan, lokacin da yaga yanayin jikin Hajiyar bayan ya iso hankalinshi ya ƙara tashi don duk ta faɗa da gani tana jin jiki Haisam ɗin yace ma Tk tun yashe ne bata lafiya cike da damuwa yace kwananta biyu nan ya sanar mashi yadda sukai da likita harda kwantar da itan da akace za'a yi taƙi, bayan Dad ɗinshi ya kirashi ya sanar mashi gaskiya tana ɗan jin jiki Hajiya Maryam harda Vedio call suka yi taga Hajiyar nan fa hankalinta ya ƙara tashi tace ma Haisam gobe da safe zata zo ta ɗauketa, a daren ranar mutanen da suka ji zancen ciwon duk da zullumi suka kwana, washe gari wurin ƙarfe bakwai Hajiya Maryam ta iso nan ta hau su Tk da faɗan ya tana rashin lafiya zasu ƙi kira su sanar tunda ta fara ciwon, bawan Allah harda yar ƙwallan shi yace mata Hajiyar ce ta hana don kada a tada masu hankali aikuwa ta ƙara balbale shi da faɗa harda cewa ko don ba Mahaifiyarshi bace, wannan kalma ta saka shi fashewa da kuka, cikin halin ciwo Hajiya tace mata don me zata faɗi mashi haka bata ji yace ita ta hana ba ko so take yay mata rashin biyayya yaƙi jin Maganarta ganin ran Hajiyar ya 6aci ga kuma halin da take ciki yasa ta ba Tk ɗin haƙuri kan Maganar da tayi, wuraren ƙarfe sha ɗaya suka tafi da Hajiyar Abuja aka bar su Tk da kewa da damuwa sai Addu'ar Allah ya tashi kafaɗun Hajiyar suke, su Gwaggo ma duk sun damu haka yan'unguwa da yawanci duk basu san da Hajiyar bata lafiya ba sai yau da aka tafi da ita duk an damu yara da manya anata mata Addu'o'i.