← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 173 OF 211

Sashe 173

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

"Gwaggota lafiya kuwa?" taji muryarshi yana tambaya, kallonshi tayi da ɗan guntun murmushi tace mashi lafiya lou yace amman to ya ya ganta kamar wani abu na damunta ta ɗan yi shiru kafin tace mashi ba komai, shiru ya ɗanyi yanata kallonta can ya sake tambayarta to lafiya Kawu Mani yazo gidansu yaga bai ta6a zuwa ba tunda suke a gidan, shiru Gwaggo tayi tana tunanin mi zata ce mashi ya kawo shin tunda gashi yasan bai ta6a zuwa gidan ba can zuciyarta ta bata kawai ta faɗi mashi abunda ya kawo shi tunda dama ko ba yanzu ba dole zata faɗi mashi, ajiyar zuciya ta sauke tare da kallonshi kaman mai zullumin faɗi mashi shi kuma ya ƙura mata ido alamar ita yake jira tayi magana can dai tayi ƙarfin halin faɗi mashi Hajiya ce ta turo shi wai ya nemi aurenta, ɗan waro ido Amadun yay kafin da sauri yace "to kin amince mashi zaki aure shin???" a hankali ta girgiza kai kafin tace ce mashi tayi sai tayi shawara amman ita....kafin ta ƙarasa abunda take son faɗin kawai sai gani tayi ya kamo hannunta yace "Don Allah Gwaggota ki amince mashi kada ki ƙi kamar yadda kike yi a baya na roƙe ki, wllh ba wuce kiyi aure kikai ba tsofaffi tukuf ma zaki ga suna da aure tunda shi ibada ne, kinga in kika amince mashi muma a ƙalla zai zama muna da Baba a cikin gidan nan" shiru tayi tana kallon shi ta wani bangaren ta ɗan ji mamaki don bai ta6a nuna mata ya damu da tayi aure ba irin yanzu yawanci da anzo neman aurenta ta nuna bata so sai yace shikenan tunda haka take so, tana haka sai gani tayi ya saukko daga saman kujerar ya duƙa a saman guiwowinshi cikin marairaicewa yace "Don Allah Gwaggota ko don ni ki amince mashi nima dai ace inada wanda zan kira da sunan BABA ba tare dana haɗa da sunan shi ba, tun tasowa ta ba wanda nike kira da sunan Baba ba tare da nace Baba wane ba kamar Baba shehu, Baba musa da sauransu kinga yanzu in kika aure shi Baba zan rinƙa kiranshi ba yadda za'ai in haɗa da sunan shi nima a ƙalla in muna hira da wasu zance Babanmu ka za...." kasa ƙarasawa yay saboda ƙwallan da suka tarun mashi suna niyyar zubowa, wani irin tausayinshi ne Gwaggo taji ya kamata tun yana ɗan shekara shidda ya rasa mahaifinshi, girgiza hannunta yay ya furta "Don Allah Gwaggota..." ajiyar zuciya ta sauke tana ƙoƙarin ƙaƙalo murmushi tace "baka tunanin ba lalle ya zama kamar uba a garekan ba kamar yadda yake faruwa sau da yawa wasu ma sai kaga sun raba uwa da ɗanta..." da sauri ya tari hanzarinta,

"A'a Gwaggo ina da yaƙinin bazai yi hakan ba tunda kika ga Hajiya ta turo shi to tasan baida matsala ne, na tabbatar mutumin kirki ne ai ina ganin shi a gidan Hajiyar muna gaisawa, don Allah ki amince?" shiru tay tana kallon shi ƙwallan idon shi har sun zubo mashi can tace shikenan tunda haka yake so zata amince mashi, da sauri ya miƙe ya zauna gefenta tare da ƙanƙameta cikin tsananin farinciki ya shiga yi mata godiya harda su Kiss ya manna mata a gefen fuskarta ita dae sai dariya take zata iya cewa bata ta6a ganinshi cikin farinciki irin wannan ba in ma ta ta6a gani to ta manta, sakinta yay sai faman washe baki yake ya shiga laluban wayarshi yana faɗin bari ya sanar ma Fatuu wannan abun Farinciki, da sauri Gwaggo tace kada ya sanar mata yace a'a yakamata ta sani da zafi zafi, ƙoƙarin amshe wayar Gwaggon tayi ya miƙe yana dariya ya shiga yin safa da marwa a tsakar falon cikin harshen fullanci Gwaggon ke faɗin tana wasa dashi wai sai dariya yake itama yar dariyar take, tana fara yin ringing Fatun ta yanke sai gashi ta kira yana ɗauka ko gaisawa basu yi ba da sauri yace mata Albishirinta a ƙagauce ta amsa da goro fari ƙal yace banda shi ango sun ƙara samun Amarya a gidansu nan ya shiga faɗi mata zancen auren Gwaggo aikuwa wata uwar ƙarar murna ta saki tana faɗin Alhamdulillah abubuwan farinciki sai faruwa suke dasu Amadun yace Wllh kuwa da sauri tace mashi ina Gwaggon ya bata wayar bari ta maida Vedio call taga fuskar amarya yace to, duk Gwaggo na jin su da yake a speaker yasa kiran sai girgiza kai take tana ɗan murmushi, bayan an maida kiran na gani ya miƙa ma Gwaggon saida ta ɗan harareshi sannan ta amsa Fatuu na ganinta ta daddage ta rangaɗa guɗa duk da bama ta wani iya ba sosae Gwaggon tayi yar dariya, cikin washe baki ta gaishe da ita kafin ta shiga yi mata shaƙiyanci tana faɗin ashe dai da rabon za'a mata makeup na amare a ɗaura mata gwaggaro nan take Gwaggon ta tuna da lokacin da Fatun ta faɗi haka can shekarun baya kafin ta girma ta shiga yin dariya, da sauri Amadu ya fita ya kirawo Kamalu suka dawo falon nan suka haɗu suna ta mata iya shege har saida tace in suka isheta zata fasa Allah sannan suka shafa mata lafiya. Washe gari sai ga Kawu Mani ya kirawota wai ya kira yaji yadda suke nan take sanar mashi ta amince ma buƙatar shi, sosae ya nuna jin daɗin shi harda ce mata shi dama yasan zata amince don su jinin sa'a ne tayi murmushi kawai kafin tace mashi amman ko za'a ɗaura masu aure sai anyi na Amadu yace mata amman mi zai hana a riga yin nasu yadda zasu aurar dashi tare tace mashi ita dai tafi son a riga nashi kuma gidan nasu ma Haisam yasa za'a mashi gyara ne tunda anan zata zauna yace duk yadda take so haka za'ayi tunda anan take son zama lafiya lou ya rinƙa zuwa dama yana yawan zuwa katsinar ko can baya saida yayi tunanin yin mata anan yace alabashshi sai ya rinƙa biyanta kuɗin hayar zaman da take, da sauri tace mashi a'a ba sai yayi hakan ba yana murmushi yace to ai saboda ya fita hakkinsu tunda gidan gado ne tace mashi ai itama tana da kaso a ciki lafiya lou kawai dae fatan ta ya ruƙe su amana kada tayi dana sanin yin auren bayan tsawon lokaci, yar dariya mai sauti yayi yace "Kada ki damu Amaryata, Hajjaju tasan zan ruƙe amanarki shiyasa tayi man maganar ki ni kuma ina ganin ki mashin son ki ya soke man zuciya ba shiri na faɗa tarko" Yadda yayi Maganar har saida tayi dariya don ta fahimci ɗan barkwanci ne sai ga Gwaggo an saki jiki ana shan Love😍
Chapter 173 · 0% Book details