Sashe 185
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Oh ya Allah, shiyasa aka ce maganin kada ayi to kada a fara yanzu ina amfanin haka ace budurwa kamar Farha ta 6ace ai dole a shiga dumuwa da tashin hankalin halin da take ciki, yanzu da ta tafi Kano mi taje yi can in ma acan ɗin ta tsaya, to ko dai yin Film ta tafi ne don naji ance dama wasu yan wasan hausan sanadin auren dole suke tafiyar su su shiga, to in ma dai Film ɗin taje yi ai da sauƙi don tana farawa za'a ganta tsorona ace ba a Kanon ta tsaya ba ta haɗu da wata yar Kano to Jidda ta hure mata kunne kan ta gudo wurinta ta fitar da ita waje....." da sauri Hajiya Maryam ta katseta da faɗin "Don Allah Hajjaju ki daina yin wannan fatan",
"To Maryam na bari Hankalina ne ya tashi na rasa tunanin da zanyi kan inda ta dosa amman in sha Allahu tana a hannu nagari Allah zai tsareta" da sauri Hajiya Maryam ta amsa da Allah yasa kafin a zuciye tace "In dai ba'a ganta ba zuwa gobe ina nan zuwa Katsina zan sa a kama yaron nan da kaf danginshi a tuhume su na tabbatar basu rasa sanin inda take don haka sai sun nemo man yarinyata",
da sauri Hajiya tace "akan me, ke waya faɗi maki su suka ɗauketa, yarinyar da daga gani ita ta shirya ma kanta hakan tunda har da takarda ta aje to ina ruwan yaro da dangin shi anan?" a fusace tace ai zai iya yuwuwa shiya tsara mata,
"Ba wani tsara matan da yayi yaron da tun farko ita ta bayyana mashi so nan fa Kakarshi tazo cikin damuwa kan bata son al'amarin gudun matsala sai kuma suja ma kan su matsalar, don haka ni ban amince kisa ayi masu wani abu ba don na tabbatar basu da sa hannu a 6atan ta in kuma kika ƙi jin maganata kika sa akai ma yaron mutane wani abun ita mai guduwar ta samu labari al'amarin ya ƙara kwa6ewa to ba ruwana kar ma kice zaki kirani dama yanzu ai harda ƙin jin maganata yasa hakan ta faru don haka na dai gaya maki ban amince kisa ayi masu wani abu ba muci gaba da Addu'ar bayyanarta da kasancewarta cikin ƙoshin lafiya" a sanyaye ta amsa mata da Amin kafin sukai sallama, bincike ya tsananta a Kano a gidajen radio da tv da social Media harda Airport anata cigiya harda hotunan Farhar da ranar data zo kano harda kayan jikinta, duk abun nan su Gwaggo basu sani ba kawai dai Kamalu nata kiran layinta bai shiga har ya fara shiga damuwa dama lokacin da tana gida cikin halin damuwa sunyi waya har yake mata magana kan jin muryarta ta canza tace mashi bata jin daɗi ne duk sai tunanin shi ya tafi akan ko ciwon ne yay tsanani yasa ba'a samunta a waya, sai ranar juma'a lokacin kwana ukku da 6acewarta Kamalu yaje School wani abokin shi da suke tare ya nuna mashi hoton Farhar a Facebook yace mashi wai wannan ba itace wannan ɗiyar Minister ɗin ba ƙawarshi da yake ganin hotunanta a wayarshi da sauri Kamalun yace mashi eh itace miya faru nan yake ce mashi wai nemanta ake ta 6ace ai da sauri ya warci wayar yana dubawa nan ya tabbatar da hakan yana bashi wayar ya miƙe sai gida, Lokacin daya dawo a falon Gwaggo ya isketa tare da Amadu da Haulat duk sunyi jugum tun bayan da Amadu ya shigo masu da labarin 6atan Farhar suke haka kowa ya kasa yin ƙwaƙƙwaran motsi, shima zama yay cikin tashin hankali yace masu ko sun samu labarin daya samu yanzu a School wai Farha ta 6ace duk suka ɗaga mashi kai ai shima sai ya nemi wuri ya zauna, bayan wani lokaci Gwaggo ta sauke nannauyar ajiyar zuciya cike da damuwa tace ita dai fatan ta Allah yasa ba dalilin abunda tazo dashi bane tunda dama tace ma Kamalu ita tasan yadda zata sa iyayenta su amince in ko har hakan ne to kuwa akwae babbar matsala, jin Maganar Gwaggo yasa cikin Kamalu juyawa Amadu yace mashi suna waya da ita ne nan ya faɗi masu rabon shi da ita a waya Haulat tace Allah yasa dai ba dalilin hakan yasa ta 6ace ba Allah kuma yasa a ganta duk suka amsa da Amin, Amadu ne yace bari ya kira Fatuu yasan ta bakinta zasu iya jin dalilin 6acewar tata, bayan ta kira sun gaisa yake mata zancen Farhar yace da gaske wai ta 6ace tace mashi eh ya tambayi tasan dalilin 6acewar tata nan ta faɗi mashi guduwa tayi don harda takarda ta aje Mom ɗin su taƙi yarda da Kamalu shine ta yanke yi mata auren dole da Cousin ɗinta da suke yin soyayya a satin data gudun, salati Gwaggo ta saka tare da rufe ido ta dafe goshi shi kuwa Kamalu zumbur ya miƙe yay hanyar ɗakin shi yana zuwa sai toilet, Fatun bata fito ta bayyana masu inda Farhar take ba duk da ta sani saboda Hajiya tace kar a faɗi ma kowa sai dai ta shiga kwantar masu da hankali tace in sha Allahu za'a ganta tunda har an gano ta hau jirgi taje kano Amadu yace to Allah yasa ta amsa tace ina Gwaggo yace gata nan tayi jugum duk tsoro ya kamata tace Kamalu fa yana yar dariya yace shi wannan yana tunanin yana toilet don yana jin bayanin data yi ya miƙe yay hanyar ɗaki Fatun tay yar dariya tace su kwantar da hankalinsu tasa aka ba Gwaggo suka gaisa nan ta shiga kwantar mata da hankali ita dae sai uhmm da to kawai take cewa, suna gama yin wayar Gwaggo ta miƙe tace bari taje tayi ma Hajiya jaje Haulat ma ta miƙe tace bari ta sako Hijab suje, lokacin da suka je Hajiyar na bedroom Farha kuma tana a ɗayan bedroom ɗin Husnah tanata shan bacci abunta dama nan Hajiya tasa ta zauna gudun kada Momynta tayi zuwan bazata, Saude ce ta kirawo masu Hajiyar bayan ta shigo cikin falon tana ɗan murmushi tayi masu sannu da zuwa tare da yi masu barka da Juma'a duk suka amsa suka gaisheta, Gwaggo ce ta fara mata jajen tace su wllh basu san abunda ke faruwa ba sai yau da su Amadu suka ga ana cigiyarta a waya Hajiya na ɗan murmushi tace tsakaninta ne da uwarta taƙi goyon bayan wanda take so ƙarshe ma sai ta yanke yi mata auren dole to dama yaran zamani ana masu dole ne shine ta kaɗa kai tayi gaba abunta, cike da damuwa Gwaggo tace wllh tun farko irin haka take ta gudu don tasan abu ne mai wuya iyayenta su amince Hajiya tace shi mahaifinta ma ya amince uwarce taƙi da yake taurin kai ne da ita sai kuma ta samu yarinya irinta sai suyi ta cakusawa, itama Haulat jajen tayi mata da Addu'ar Allah ya bayyanata ta amsa da Amin ganin yadda Gwaggo tayi gwalau duk ta shiga damuwa yasa Hajiyar yin yar dariya tace "Amaryar Mani ya ya, ko kina tsoron hukuncin da Minister zata yi maku na kun yi silar 6acewar ɗiyarta" ɗan motsa baki Gwaggon tayi kafin tace a'a kawai dai 6acewar mutum bata da daɗi ba'a san a wane hali take ciki ba, Hajiyar tace mata kar su damu za'a ganta ne suka ce Allah ya sa, bayan sun mata sallama sun fito ne Haulat tace ma Gwaggo ita sai taga kamar Hajiya tasan inda Farhar take don taga kamar bata damu ba Gwaggo tace itama ta lura ƙilan kuma kawai ƙarfin zuciya ne Haulat ɗin ta ƙara cewa ko kuma shiri ne akai don Hajiya Maryam ɗin ta saduda Gwaggo tayi shiru tana nazarin Maganar, har aka shiga Weekend shiru Farha bata bayyana ba Kamalu kuwa yana can yana zazza6in zullumi, ranar Lahadi Dr mijin Hajiya Maryam ya kira Hajiya anan yake sanar mata ba ƙaramin tashi hankalin Hajiya Maryam yayi ba ko isasshshen bacci bata yi taita kuka tana faɗin tayi sanadin 6acewar ɗiyarta waya sani ma ko ta mutu shi yanzu tausayi take bashi sosae gashi sai zuba kuɗi take ana cigiya a gidajen tv da radio yanzu har kuɗi tasa masu yawa na duk wanda ya kawo ta ko ya faɗi inda take zata bashi, murmushi Hajiya tayi tare da ɗan ta6e baki tace mashi ya ƙyaleta ta ɗan ƙara jin jiki tukun su kuma kuɗi da take 6atarwa na cigiya ai tana dasu ne don haka suma kafafen sadarwar ta fitar masu da zakka Dr ya ɗan yi shiru kafin yace shi abunda yake gudu kada wani ciwon kuma ya haye mata Hajiyar tay murmushi mai ɗan sauti jin yanzu kuma ta matar shi yake tace mashi kada ya damu ba ciwon da zai haye mata in ba hakan aka yi mata ba bazata daina taurin kai ba, bayan sun gama yin wayar shiru Hajiya tayi ta ɗan ta6e baki a ranta ta shiga raya in ba don ta kama ba ita kanta ai bazata so ta tada ma ɗiyarta hankali ba, damuwa tasa Hajiya Maryam ƙin komawa Abuja har wata rama tayi daka ganta kasan tana cikin damuwa bayan Hajiya ta warware ma President komai ya kira Hajiya Maryam ɗin sosae yayi mata faɗa yace al'amarin irin wannan ai a hankali ake bi da ta saurari Hajiya duk da hakan bata faru ba yakamata ta daina saurin fushi ta rinƙa bin komai a hankali tana ƙwalla tace mashi in sha Allahu zata rinƙa bin komai a hankali su Mom ma duk sun kirata sunyi mata jaje har suna cewa zasu zo Lagos ɗin suyi mata jaje tace ba sai sun zo ba kawai dai don Allah a tayasu bincikawa ba kamar wurin mutanensu dake Kano suka ce dama duk sunsa anata cigitawa in sha Allahu za'a ganta, Fanan ma ce mata tayi tana son tazo Nigeria ɗin amman ta ɗan ƙara saurarawa ne ko Farhar zata taho wurinta daga Kanon Hajiya Maryam ɗin tace hakan yayi kada ta taho, a ranar Monday da daddare Hajiya ta kira Hajiya Maryam tace mata gobe tazo tana son ganinta tana jin haka da sauri tace mata ko Farhar tazo wurinta ne tace mata a'a tana son yin magana da ita ne...........
"To Maryam na bari Hankalina ne ya tashi na rasa tunanin da zanyi kan inda ta dosa amman in sha Allahu tana a hannu nagari Allah zai tsareta" da sauri Hajiya Maryam ta amsa da Allah yasa kafin a zuciye tace "In dai ba'a ganta ba zuwa gobe ina nan zuwa Katsina zan sa a kama yaron nan da kaf danginshi a tuhume su na tabbatar basu rasa sanin inda take don haka sai sun nemo man yarinyata",
da sauri Hajiya tace "akan me, ke waya faɗi maki su suka ɗauketa, yarinyar da daga gani ita ta shirya ma kanta hakan tunda har da takarda ta aje to ina ruwan yaro da dangin shi anan?" a fusace tace ai zai iya yuwuwa shiya tsara mata,
"Ba wani tsara matan da yayi yaron da tun farko ita ta bayyana mashi so nan fa Kakarshi tazo cikin damuwa kan bata son al'amarin gudun matsala sai kuma suja ma kan su matsalar, don haka ni ban amince kisa ayi masu wani abu ba don na tabbatar basu da sa hannu a 6atan ta in kuma kika ƙi jin maganata kika sa akai ma yaron mutane wani abun ita mai guduwar ta samu labari al'amarin ya ƙara kwa6ewa to ba ruwana kar ma kice zaki kirani dama yanzu ai harda ƙin jin maganata yasa hakan ta faru don haka na dai gaya maki ban amince kisa ayi masu wani abu ba muci gaba da Addu'ar bayyanarta da kasancewarta cikin ƙoshin lafiya" a sanyaye ta amsa mata da Amin kafin sukai sallama, bincike ya tsananta a Kano a gidajen radio da tv da social Media harda Airport anata cigiya harda hotunan Farhar da ranar data zo kano harda kayan jikinta, duk abun nan su Gwaggo basu sani ba kawai dai Kamalu nata kiran layinta bai shiga har ya fara shiga damuwa dama lokacin da tana gida cikin halin damuwa sunyi waya har yake mata magana kan jin muryarta ta canza tace mashi bata jin daɗi ne duk sai tunanin shi ya tafi akan ko ciwon ne yay tsanani yasa ba'a samunta a waya, sai ranar juma'a lokacin kwana ukku da 6acewarta Kamalu yaje School wani abokin shi da suke tare ya nuna mashi hoton Farhar a Facebook yace mashi wai wannan ba itace wannan ɗiyar Minister ɗin ba ƙawarshi da yake ganin hotunanta a wayarshi da sauri Kamalun yace mashi eh itace miya faru nan yake ce mashi wai nemanta ake ta 6ace ai da sauri ya warci wayar yana dubawa nan ya tabbatar da hakan yana bashi wayar ya miƙe sai gida, Lokacin daya dawo a falon Gwaggo ya isketa tare da Amadu da Haulat duk sunyi jugum tun bayan da Amadu ya shigo masu da labarin 6atan Farhar suke haka kowa ya kasa yin ƙwaƙƙwaran motsi, shima zama yay cikin tashin hankali yace masu ko sun samu labarin daya samu yanzu a School wai Farha ta 6ace duk suka ɗaga mashi kai ai shima sai ya nemi wuri ya zauna, bayan wani lokaci Gwaggo ta sauke nannauyar ajiyar zuciya cike da damuwa tace ita dai fatan ta Allah yasa ba dalilin abunda tazo dashi bane tunda dama tace ma Kamalu ita tasan yadda zata sa iyayenta su amince in ko har hakan ne to kuwa akwae babbar matsala, jin Maganar Gwaggo yasa cikin Kamalu juyawa Amadu yace mashi suna waya da ita ne nan ya faɗi masu rabon shi da ita a waya Haulat tace Allah yasa dai ba dalilin hakan yasa ta 6ace ba Allah kuma yasa a ganta duk suka amsa da Amin, Amadu ne yace bari ya kira Fatuu yasan ta bakinta zasu iya jin dalilin 6acewar tata, bayan ta kira sun gaisa yake mata zancen Farhar yace da gaske wai ta 6ace tace mashi eh ya tambayi tasan dalilin 6acewar tata nan ta faɗi mashi guduwa tayi don harda takarda ta aje Mom ɗin su taƙi yarda da Kamalu shine ta yanke yi mata auren dole da Cousin ɗinta da suke yin soyayya a satin data gudun, salati Gwaggo ta saka tare da rufe ido ta dafe goshi shi kuwa Kamalu zumbur ya miƙe yay hanyar ɗakin shi yana zuwa sai toilet, Fatun bata fito ta bayyana masu inda Farhar take ba duk da ta sani saboda Hajiya tace kar a faɗi ma kowa sai dai ta shiga kwantar masu da hankali tace in sha Allahu za'a ganta tunda har an gano ta hau jirgi taje kano Amadu yace to Allah yasa ta amsa tace ina Gwaggo yace gata nan tayi jugum duk tsoro ya kamata tace Kamalu fa yana yar dariya yace shi wannan yana tunanin yana toilet don yana jin bayanin data yi ya miƙe yay hanyar ɗaki Fatun tay yar dariya tace su kwantar da hankalinsu tasa aka ba Gwaggo suka gaisa nan ta shiga kwantar mata da hankali ita dae sai uhmm da to kawai take cewa, suna gama yin wayar Gwaggo ta miƙe tace bari taje tayi ma Hajiya jaje Haulat ma ta miƙe tace bari ta sako Hijab suje, lokacin da suka je Hajiyar na bedroom Farha kuma tana a ɗayan bedroom ɗin Husnah tanata shan bacci abunta dama nan Hajiya tasa ta zauna gudun kada Momynta tayi zuwan bazata, Saude ce ta kirawo masu Hajiyar bayan ta shigo cikin falon tana ɗan murmushi tayi masu sannu da zuwa tare da yi masu barka da Juma'a duk suka amsa suka gaisheta, Gwaggo ce ta fara mata jajen tace su wllh basu san abunda ke faruwa ba sai yau da su Amadu suka ga ana cigiyarta a waya Hajiya na ɗan murmushi tace tsakaninta ne da uwarta taƙi goyon bayan wanda take so ƙarshe ma sai ta yanke yi mata auren dole to dama yaran zamani ana masu dole ne shine ta kaɗa kai tayi gaba abunta, cike da damuwa Gwaggo tace wllh tun farko irin haka take ta gudu don tasan abu ne mai wuya iyayenta su amince Hajiya tace shi mahaifinta ma ya amince uwarce taƙi da yake taurin kai ne da ita sai kuma ta samu yarinya irinta sai suyi ta cakusawa, itama Haulat jajen tayi mata da Addu'ar Allah ya bayyanata ta amsa da Amin ganin yadda Gwaggo tayi gwalau duk ta shiga damuwa yasa Hajiyar yin yar dariya tace "Amaryar Mani ya ya, ko kina tsoron hukuncin da Minister zata yi maku na kun yi silar 6acewar ɗiyarta" ɗan motsa baki Gwaggon tayi kafin tace a'a kawai dai 6acewar mutum bata da daɗi ba'a san a wane hali take ciki ba, Hajiyar tace mata kar su damu za'a ganta ne suka ce Allah ya sa, bayan sun mata sallama sun fito ne Haulat tace ma Gwaggo ita sai taga kamar Hajiya tasan inda Farhar take don taga kamar bata damu ba Gwaggo tace itama ta lura ƙilan kuma kawai ƙarfin zuciya ne Haulat ɗin ta ƙara cewa ko kuma shiri ne akai don Hajiya Maryam ɗin ta saduda Gwaggo tayi shiru tana nazarin Maganar, har aka shiga Weekend shiru Farha bata bayyana ba Kamalu kuwa yana can yana zazza6in zullumi, ranar Lahadi Dr mijin Hajiya Maryam ya kira Hajiya anan yake sanar mata ba ƙaramin tashi hankalin Hajiya Maryam yayi ba ko isasshshen bacci bata yi taita kuka tana faɗin tayi sanadin 6acewar ɗiyarta waya sani ma ko ta mutu shi yanzu tausayi take bashi sosae gashi sai zuba kuɗi take ana cigiya a gidajen tv da radio yanzu har kuɗi tasa masu yawa na duk wanda ya kawo ta ko ya faɗi inda take zata bashi, murmushi Hajiya tayi tare da ɗan ta6e baki tace mashi ya ƙyaleta ta ɗan ƙara jin jiki tukun su kuma kuɗi da take 6atarwa na cigiya ai tana dasu ne don haka suma kafafen sadarwar ta fitar masu da zakka Dr ya ɗan yi shiru kafin yace shi abunda yake gudu kada wani ciwon kuma ya haye mata Hajiyar tay murmushi mai ɗan sauti jin yanzu kuma ta matar shi yake tace mashi kada ya damu ba ciwon da zai haye mata in ba hakan aka yi mata ba bazata daina taurin kai ba, bayan sun gama yin wayar shiru Hajiya tayi ta ɗan ta6e baki a ranta ta shiga raya in ba don ta kama ba ita kanta ai bazata so ta tada ma ɗiyarta hankali ba, damuwa tasa Hajiya Maryam ƙin komawa Abuja har wata rama tayi daka ganta kasan tana cikin damuwa bayan Hajiya ta warware ma President komai ya kira Hajiya Maryam ɗin sosae yayi mata faɗa yace al'amarin irin wannan ai a hankali ake bi da ta saurari Hajiya duk da hakan bata faru ba yakamata ta daina saurin fushi ta rinƙa bin komai a hankali tana ƙwalla tace mashi in sha Allahu zata rinƙa bin komai a hankali su Mom ma duk sun kirata sunyi mata jaje har suna cewa zasu zo Lagos ɗin suyi mata jaje tace ba sai sun zo ba kawai dai don Allah a tayasu bincikawa ba kamar wurin mutanensu dake Kano suka ce dama duk sunsa anata cigitawa in sha Allahu za'a ganta, Fanan ma ce mata tayi tana son tazo Nigeria ɗin amman ta ɗan ƙara saurarawa ne ko Farhar zata taho wurinta daga Kanon Hajiya Maryam ɗin tace hakan yayi kada ta taho, a ranar Monday da daddare Hajiya ta kira Hajiya Maryam tace mata gobe tazo tana son ganinta tana jin haka da sauri tace mata ko Farhar tazo wurinta ne tace mata a'a tana son yin magana da ita ne...........