Sashe 120
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
.............Bada jimawa ba sai gashi ya kira, bayan tayi picking a hankali ta gaishe shi da tambayar shi ya aiki, har saida ta d'an lumshe ido Jin muryar shi da ya amsa, shiru tayi tama rasa mi zata ce mashi tana hakan taji yace ya Abuja tana d'an murmushi tace lafiya lou yau anyi suna sai kuma tace mashi har ma sun gaisa da Mom d'in shi taji ya furta Ok, shiru sukai can ya k'ara cewa koda wani abu ne ta d'an tura baki shi haka yake duk ta kira shi tana jin shauk'i sai ya wani kama tambayar ta koda wani abu, Ji tayi ya k'ara cewa inda wani abu ta fad'a mashi ta d'an kara tura baki sai kuma a hankali tace "No, babu komai dama kawai na kira ne in ji mur....." Kasa k'arasawa tayi ta d'an waro ido don bata ta6a ce mashi hakan ba,
"ina jin ki" taji ya fad'i hakan, abu ta had'iya kamar ta canza abunda ta fad'an wata zuciyar ta shiga k'arfafa mata gwuiwa ta fad'i mashi hakan, "Dama naji ina son jin voice en ka ne" wani kalan murmushin gefe yay taji yace mi voice en nashi gare shi, d'an Farfar tayi da ido da k'yar ta furta mashi "Yana da dad'in sauraro ne" shiru taji yayi har saida gabanta ya d'an fadi don tasan shi wani lokacin ba'a cika yi mashi gwaninta ba, tambayar ta yay tana ina ne ta bashi amsa da tana a d'akin da suka sauka ya k'ara tambayar ita da waye tace su biyu ne kuma d'ayar bata kaiga shigowa ba taji ya furta Ok suyi Vedio call tace to, lokacin daya maida kiran na gani yana kwance a saman gado yau ma robe ce a jikinshi chest d'in shi a bud'e ya tashi zaune tare da jingina da headboard, bin juna sukai da kallo Fauzy nata mashi d'an murmushi shima yanayin fuskar shi kaman zai murmushin, ganin yanayin idanun shi a lumshe kaman mai jin bacci yasa tace "ko bacci kake ne?" saida ya k'ara lumshe su sannan ya d'an girgiza mata kai,
"Naga kaman har ka kwanta" ta k'ara fad'a idanunta cikin nashi yay d'an shiru can ya bata amsa da ya gaji ne yayi tafiya bai dad'e daya dawo ba ta jinjina mashi kai kafin tace "to bari in bar ka ka huta" wani kallo yay mata ya d'an shigar da lip d'in shi na k'asa kafin taji yace har ta gama sauraron muryan nashi ne, yar dariya tayi ta girgiza mashi kai alamar a'a sai kuma tace "to ai kai baka magana sosae" d'an yamutsa baki yay yace mata bai iya bane ta gyad'a kai ta k'ara cewa "in kana so sai in koya maka" murmushin gefen baki yay tare da girgiza kai yace yafi jin dad'in hakan tunda hakan ya sa6a nan ma kai ta gyad'a mashi suka k'ara yin shiru suna kallon juna,
"A gida kake ne ko hotel?" shiru kaman bazai bata amsa ba taji yace da wani abu ne ta tambaya da sauri ta girgiza mashi kai "hakanan kawai na tambaya" ta bashi amsa, ce mata yay yana a gidan shi ne ta gyad'a kai sai kuma ta k'ara cewa "kuma kai kad'ai kake zaune?",
"Zan zauna da wa?" Ya fad'a, tana murmushi tace "a'a dama ina nufin kai kad'ai ne ba wani wanda ke taya ka zama?" shirun dai yay yana bin ta da ido sai can yace mata yakamata ya samu abokin zama ne tace "kawai naga in kai kad'ai ne kaman kad'aici zai dame ka shiyasa nayi tunanin ko akwai wani da kuke zaune tare" lumshe ido yay tare da d'an girgiza mata kai alamar a'a sai kuma taji yace "akwai wata da zata zo" har saida gaban Fauzy ya fad'i da alamun rashin fahimta tace mashi wata zata zo nan ta zauna ya d'aga mata kai alamar eh, wani irin abu taji ya tokare mata k'irji a zuciyarta ta shiga raya kenan mata suke zuwa suna kwana tare dashi kuma a haka ace bai neman su cab, wani bangaren na zuciyar ta ya raya mata kika san wacece ko yar uwar shi ce, kasa daurewa tayi yana ta kallon ta yanayin fuskarta ya d'an canza tace mashi ita wadda zata zo d'in yar uwar shi ce kawai sai gani tayi ya girgiza mata kai alamar a'a yace kawai zata zo su zauna tare ne ya rage loneliness, abu Fauzy ta had'iya yanayin fuskar ta ya k'ara sauyawa ta koma kallon gefe tana d'an kikkafta idanu, "Any problem?" taji ya fad'i hakan ta juyo suka had'a ido wani irin abu mai zafi take ji a ranta ta bishi da kallo yanayin fuskar ta kaman zata saka kuka, d'age mata gira yay ya k'ara tambayar da matsala ne a sanyaye ta d'aga mashi kai yace miye matsalan to, ce mashi tay kawai taga ya zai kawo wata su zauna bayan ba muharramarshi bace ai yasan hakan ba kyau ko, yanayin yadda tay Maganar da yar shagwaba, d'an murmushi taga yayi yace mata ai kawai zata taya shi zama ne ba wani abu ba, yamutsa fuska Fauzy tay yadda take ji kaman ta saki kuka don tasan ko ba wani abun dole k'ilan bai rasa ta6a wadda zai kawo d'in tunda ance yana yin hakan ita yanzu ma ta fara zargin anya bai wuce hakan, ji tayi idanun ta sun ciko da k'walla kawai sai ta sadda kanta k'asa ta daina barin kallonshi shi kuma yanata kallon ta bayan d'an wani lokaci taji ya kira sunan ta shiru ta d'an yi bata amsa ba, a duniya tana jin ba wanda ya iya kiran sunanta kaman yadda yake yi don sosae yake fitar da ko wane harafi,
"ba ki ji na kira ki ba?" Jin ya fad'i hakan yasa ta d'ago ta kalle shi idanunta sun d'an tara k'walla a hakan ma tayi kokarin maida wasu, "baki so tazo ne?" yana mata wani kallo ya tambayi hakan da sauri ta d'aga mashi kai,
"Why?"
"To ai ba kyau fa hakan kuma nasan ka sani taya wata zata zo ta taya ka zama ina laifin ko abokin ka" cikin yar karyayyar murya ta mai son yin kuka tayi Maganar, shiru yay idonshi cikin nata tana ta yan d'aure dauren fuska can taga yay wani d'an murmushi tare da ta6e baki ganin haka yasa ta maida idonta k'asa kawai sai ji tayi k'walla sun zubo mata sharr kiran sunanta ya k'ara yi ta d'ago saida yay mamakin ganin kwallan duk da bai nuna ba, ce mata yay don wata zata zo ta taya shi zama shine yasa take kuka shiru tay bata ce komai ba tana ta yan kyafcen kyafcen idanu,
"In kuma wadda zata zo d'in Wife ena ce shima hakan ba kyau ne?" kaman daga sama taji ya fad'i hakan da sauri ta tsaida idanunta kan shi ya d'age mata gira alamar ta bashi amsa, shiru tayi tana juya abunda ya fad'a a cikin ranta tunanin to wacece Matar tashi ta shiga yi can zuciyarta ta raya mata ita yake nufi ko, sai lokacin ta gane kan Maganar tun daga farko tayi zuru zuru tana kallon shi yana d'an shigar da lip d'inshi na k'asa kafin ya saki yace bata bashi amsa ba, cikin jin yar kunya tace to ai bai fad'i mata hakan yake nufi bane ita tayi tunanin wata ce kawai da ba komai tsakanin su zai kawo, d'an ta6e baki yay kafin yace yar k'arama da ita tasan kishi, Maganar dariya ta bata tasa hannunta daya sha k'unshi ta d'an rufe fuskarta kafin ta cire a d'an shagwabe tace "nifa ba yarinya bace tunda na wuce 20yrs kuma baka ga ba Secondary nike ba, kuma ai ko K'aramin yaro yana kishin abunda yake so" ita kanta ji tayi kawai ta fad'i hakan, hannu ya kai ya d'an shafi beard d'in shi murmushi ya bayyana akan fuskar shi yace mata ashe tana son shi ta d'aga mashi kai yace amman ai bata ta6a fad'i mashi ba tace to ai bata san ko bai son ta fad'i mashi hakan ba yay shiru kawai yana kallonta, tattaro k'warin gwuiwa tayi idonta a cikin nashi ta furta "I love you with all my Heart" gani tayi ya d'an fad'ad'a murmushin da yake tare da d'an ta6e baki yanayin yadda yayin sai taga kaman abunda tace bata yi mashi gwaninta ba, abunda bata sani ba shine sosae yaji dad'in Maganar duk da ba bak'uwa bace a wurin shi kullum mata cikin fad'i mashi Kalmar suke don ko yau an fad'i mashi amman tata sai yaji tayi mashi dad'i shi kanshi yana mamakin kanshi sosae yadda akai Ya fad'a son ta don sosae yake jinta a ran shi (abun daga Allah ne), furta mata Thanks yayi ta d'an yi murmushi sai kuma tace to shi bai ce mata ba still da d'an murmushi a fuskar shi yace ai yayi wannan tun da yazo garin su ta d'an tura mashi baki tace wannan ai dalili ne yasa ya fad'i mata kuma yanzu bata san ya take a wurin shi ba, shiru yay kawai yana kallonta don Maganar tata ta bayyana yarintarta a wurin shi don in bai sonta Maganar auren su zata d'ore ne, d'an yamutsa mashi fuska tayi tace ita bazai fad'i mata ba d'in,
"ina jin ki" taji ya fad'i hakan, abu ta had'iya kamar ta canza abunda ta fad'an wata zuciyar ta shiga k'arfafa mata gwuiwa ta fad'i mashi hakan, "Dama naji ina son jin voice en ka ne" wani kalan murmushin gefe yay taji yace mi voice en nashi gare shi, d'an Farfar tayi da ido da k'yar ta furta mashi "Yana da dad'in sauraro ne" shiru taji yayi har saida gabanta ya d'an fadi don tasan shi wani lokacin ba'a cika yi mashi gwaninta ba, tambayar ta yay tana ina ne ta bashi amsa da tana a d'akin da suka sauka ya k'ara tambayar ita da waye tace su biyu ne kuma d'ayar bata kaiga shigowa ba taji ya furta Ok suyi Vedio call tace to, lokacin daya maida kiran na gani yana kwance a saman gado yau ma robe ce a jikinshi chest d'in shi a bud'e ya tashi zaune tare da jingina da headboard, bin juna sukai da kallo Fauzy nata mashi d'an murmushi shima yanayin fuskar shi kaman zai murmushin, ganin yanayin idanun shi a lumshe kaman mai jin bacci yasa tace "ko bacci kake ne?" saida ya k'ara lumshe su sannan ya d'an girgiza mata kai,
"Naga kaman har ka kwanta" ta k'ara fad'a idanunta cikin nashi yay d'an shiru can ya bata amsa da ya gaji ne yayi tafiya bai dad'e daya dawo ba ta jinjina mashi kai kafin tace "to bari in bar ka ka huta" wani kallo yay mata ya d'an shigar da lip d'in shi na k'asa kafin taji yace har ta gama sauraron muryan nashi ne, yar dariya tayi ta girgiza mashi kai alamar a'a sai kuma tace "to ai kai baka magana sosae" d'an yamutsa baki yay yace mata bai iya bane ta gyad'a kai ta k'ara cewa "in kana so sai in koya maka" murmushin gefen baki yay tare da girgiza kai yace yafi jin dad'in hakan tunda hakan ya sa6a nan ma kai ta gyad'a mashi suka k'ara yin shiru suna kallon juna,
"A gida kake ne ko hotel?" shiru kaman bazai bata amsa ba taji yace da wani abu ne ta tambaya da sauri ta girgiza mashi kai "hakanan kawai na tambaya" ta bashi amsa, ce mata yay yana a gidan shi ne ta gyad'a kai sai kuma ta k'ara cewa "kuma kai kad'ai kake zaune?",
"Zan zauna da wa?" Ya fad'a, tana murmushi tace "a'a dama ina nufin kai kad'ai ne ba wani wanda ke taya ka zama?" shirun dai yay yana bin ta da ido sai can yace mata yakamata ya samu abokin zama ne tace "kawai naga in kai kad'ai ne kaman kad'aici zai dame ka shiyasa nayi tunanin ko akwai wani da kuke zaune tare" lumshe ido yay tare da d'an girgiza mata kai alamar a'a sai kuma taji yace "akwai wata da zata zo" har saida gaban Fauzy ya fad'i da alamun rashin fahimta tace mashi wata zata zo nan ta zauna ya d'aga mata kai alamar eh, wani irin abu taji ya tokare mata k'irji a zuciyarta ta shiga raya kenan mata suke zuwa suna kwana tare dashi kuma a haka ace bai neman su cab, wani bangaren na zuciyar ta ya raya mata kika san wacece ko yar uwar shi ce, kasa daurewa tayi yana ta kallon ta yanayin fuskarta ya d'an canza tace mashi ita wadda zata zo d'in yar uwar shi ce kawai sai gani tayi ya girgiza mata kai alamar a'a yace kawai zata zo su zauna tare ne ya rage loneliness, abu Fauzy ta had'iya yanayin fuskar ta ya k'ara sauyawa ta koma kallon gefe tana d'an kikkafta idanu, "Any problem?" taji ya fad'i hakan ta juyo suka had'a ido wani irin abu mai zafi take ji a ranta ta bishi da kallo yanayin fuskar ta kaman zata saka kuka, d'age mata gira yay ya k'ara tambayar da matsala ne a sanyaye ta d'aga mashi kai yace miye matsalan to, ce mashi tay kawai taga ya zai kawo wata su zauna bayan ba muharramarshi bace ai yasan hakan ba kyau ko, yanayin yadda tay Maganar da yar shagwaba, d'an murmushi taga yayi yace mata ai kawai zata taya shi zama ne ba wani abu ba, yamutsa fuska Fauzy tay yadda take ji kaman ta saki kuka don tasan ko ba wani abun dole k'ilan bai rasa ta6a wadda zai kawo d'in tunda ance yana yin hakan ita yanzu ma ta fara zargin anya bai wuce hakan, ji tayi idanun ta sun ciko da k'walla kawai sai ta sadda kanta k'asa ta daina barin kallonshi shi kuma yanata kallon ta bayan d'an wani lokaci taji ya kira sunan ta shiru ta d'an yi bata amsa ba, a duniya tana jin ba wanda ya iya kiran sunanta kaman yadda yake yi don sosae yake fitar da ko wane harafi,
"ba ki ji na kira ki ba?" Jin ya fad'i hakan yasa ta d'ago ta kalle shi idanunta sun d'an tara k'walla a hakan ma tayi kokarin maida wasu, "baki so tazo ne?" yana mata wani kallo ya tambayi hakan da sauri ta d'aga mashi kai,
"Why?"
"To ai ba kyau fa hakan kuma nasan ka sani taya wata zata zo ta taya ka zama ina laifin ko abokin ka" cikin yar karyayyar murya ta mai son yin kuka tayi Maganar, shiru yay idonshi cikin nata tana ta yan d'aure dauren fuska can taga yay wani d'an murmushi tare da ta6e baki ganin haka yasa ta maida idonta k'asa kawai sai ji tayi k'walla sun zubo mata sharr kiran sunanta ya k'ara yi ta d'ago saida yay mamakin ganin kwallan duk da bai nuna ba, ce mata yay don wata zata zo ta taya shi zama shine yasa take kuka shiru tay bata ce komai ba tana ta yan kyafcen kyafcen idanu,
"In kuma wadda zata zo d'in Wife ena ce shima hakan ba kyau ne?" kaman daga sama taji ya fad'i hakan da sauri ta tsaida idanunta kan shi ya d'age mata gira alamar ta bashi amsa, shiru tayi tana juya abunda ya fad'a a cikin ranta tunanin to wacece Matar tashi ta shiga yi can zuciyarta ta raya mata ita yake nufi ko, sai lokacin ta gane kan Maganar tun daga farko tayi zuru zuru tana kallon shi yana d'an shigar da lip d'inshi na k'asa kafin ya saki yace bata bashi amsa ba, cikin jin yar kunya tace to ai bai fad'i mata hakan yake nufi bane ita tayi tunanin wata ce kawai da ba komai tsakanin su zai kawo, d'an ta6e baki yay kafin yace yar k'arama da ita tasan kishi, Maganar dariya ta bata tasa hannunta daya sha k'unshi ta d'an rufe fuskarta kafin ta cire a d'an shagwabe tace "nifa ba yarinya bace tunda na wuce 20yrs kuma baka ga ba Secondary nike ba, kuma ai ko K'aramin yaro yana kishin abunda yake so" ita kanta ji tayi kawai ta fad'i hakan, hannu ya kai ya d'an shafi beard d'in shi murmushi ya bayyana akan fuskar shi yace mata ashe tana son shi ta d'aga mashi kai yace amman ai bata ta6a fad'i mashi ba tace to ai bata san ko bai son ta fad'i mashi hakan ba yay shiru kawai yana kallonta, tattaro k'warin gwuiwa tayi idonta a cikin nashi ta furta "I love you with all my Heart" gani tayi ya d'an fad'ad'a murmushin da yake tare da d'an ta6e baki yanayin yadda yayin sai taga kaman abunda tace bata yi mashi gwaninta ba, abunda bata sani ba shine sosae yaji dad'in Maganar duk da ba bak'uwa bace a wurin shi kullum mata cikin fad'i mashi Kalmar suke don ko yau an fad'i mashi amman tata sai yaji tayi mashi dad'i shi kanshi yana mamakin kanshi sosae yadda akai Ya fad'a son ta don sosae yake jinta a ran shi (abun daga Allah ne), furta mata Thanks yayi ta d'an yi murmushi sai kuma tace to shi bai ce mata ba still da d'an murmushi a fuskar shi yace ai yayi wannan tun da yazo garin su ta d'an tura mashi baki tace wannan ai dalili ne yasa ya fad'i mata kuma yanzu bata san ya take a wurin shi ba, shiru yay kawai yana kallonta don Maganar tata ta bayyana yarintarta a wurin shi don in bai sonta Maganar auren su zata d'ore ne, d'an yamutsa mashi fuska tayi tace ita bazai fad'i mata ba d'in,