Sashe 97
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Go and gather all your things!" Kaman daga sama taji ya fad'i haka, d'ago kai tayi da sauri ta kalle shi ya jinginar da kanshi jikin seat fuskar shi na kallon gaba ya d'an lumshe ido, da alamun rashin fahimta ta shiga bin shi da kallo ta kasa gane mi yake nufi da taje ta tattaro kayan ta, mi hakan ke nufi? shine abunda take juyawa a ranta ba dai fushi yayi da Maganar data fad'i mashi ba shiyasa yace haka, kenan ta daina karatun yake nufi ko mi, haka take ta sak'e sak'e a cikin ranta gashi yak'i ko kallonta balle ya bata amsa can da alamun rashin fahimta tace mashi bata gane abunda yake nufi ba da bud'ar bakin shi sai cewa yay bata understanding turanci ne tace a'a ta gane abunda yace amman in ta tattara kayan mi zatai da su, shiru kamar bazai bata amsa ba kafin taji yace ta daina boarding School a tak'aice yayi Maganar still idanun shi na a lumshe, kai ta jinjina kafin ta juya ta kai hannu ta bud'e kopar, Mutumin daya tuk'o shi na tsaye ya jingina da k'opar gaban suna had'a ido yay mata murmushi tare da Fad'in barka da fitowa a hankali tace Yauwa, daidai lokacin data fito akan idon su Zainab da Sa'adatu dake tahowa daga class zasu Hostel gaba d'aya idanun su na akanta har ta fito daga cikin parking space d'in ta nufi hanyar zuwa hostel aikuwa cikin d'aga murya Zainab ta k'wala mata kira, tsayawa tayi har suka k'araso ta d'an k'ak'alo murmushi tana yi masu, tambayarta Zainab d'in tayi bak'o tayi ne taga ta fito daga cikin wanccan galleliyar Motar kai ta d'aga mata alamar eh ta d'an waro ido tace "da sa ranar wani akan ki shine kuma kike saurarar wani ba kyau hakan wllh, kinga don Allah kawai ki had'a ni dashi tunda ke dai kin saida" yar dariya Fauzy tay Sa'adatu ta 6aka ma Zainab d'in bugu tana fad'in ita dai ta shiga ukku da son kudi wllh daga ganin Mota mai kyau shine zata ce a had'a su, a d'an harzuk'e tace a'a to wa zai k'i mai kud'i suma duk tasan inda mai Motar zai ce yana son su da gudu zasu yarda wllh, ganin suna 6ata mata lokaci yasa tace masu bari taje ana jiranta ne da sauri Zainab ta bita tana fad'in yanzu don Allah bak'in ciki zata mata ita tunda Allah ya bata mai kud'i ba sai ta taimake ta ba, tasan in ba fad'i mata wanene tayi ba bazata k'yaleta ba don ta cika nacin magana yasa tace mata ai wanda zata aura d'in ne yazo yanzu ma zuwa yay daukarta zata bar zama a hostel, gaba d'ayan su saida suka ji ba dad'i Zainab tace maimakon tace mashi ya barta taci gaba da zama tunda dai da sauran lokaci bikin nasu Fauzyn tace mata bai so, tare suka je d'akin nasu gaba d'aya don taya ta kwasar kayan, duk wani provisions dinta su ta raba mawa haka wasu daga cikin kayanta duk abunda wani yace mata yana so sai tace ya d'auka ba kamar Zainab duk tafi kwasar abubuwa har su bokitan ta da su robobi da plates duk su ta raba mawa iya trolley d'in kayanta sai wata yar babbar jaka ta saka sauran abubuwan da take so bata bayar ba, tare suka fito su hud'u Zainab tace to bazata yi ma mutane bankwana ba tace kawai sai gobe in Allah ya kaimu tazo har d'akin ma sai taje ta sanar ta saki, dama tunda Fatuu ta bar zama a hostel ita kad'ai take rayuwa a d'akin saidai masu zuwa taya ta zama ko kwana, a tare suka iso parking space d'in har lokacin mutumin ko ace driver d'in yana a tsaye yana ganin su da sauri ya bud'e kopar gaban ya rankwafa don ya bud'e boot d'in, bayan ya bud'e ya nufo wurin ya bud'e boot d'in suna kokarin saka kayan da sauri yace su barshi zai saka, kallon su Sa'adatu tay tana murmushi tace ta gode sai sun had'u in Allah ya kaimu suma godiyar suka yi mata har zata juya Zainab tace to 6oye masu mijin nata take da bazata had'asu su gaisa ba, d'an jimm Fauzy tay don bata san taya zata aikata hakan ba, ganin sunyi tsaye suna bin ta da ido alamar duk so suke su gaisa da shi d'in yasa tace bari tayi mashi magana, bud'e k'opar bayan tayi yana zaune a inda ta barshi yana latsa waya, rasa mi zata ce mashi tay tana a rankwafe ta bishi da ido, Slowly ya d'ago suka had'a ido tace mashi ga kayan nan ta d'aukko har an saka a boot ya d'aga mata kai kafin yace ta shigo, jimm tay tana d'an kikkafta ido ganin bata shigo ba yasa shi k'ara d'agowa tun kafin yace wani abu cikin yar in ina tace "d...dama wai k'awaye nane zasu gaida ka" shiru kaman bazai tanka mata ba sai kuma ya d'age gira yace mata yace yana son haka ne har saida ta had'iyi abu, d'an girgiza mashi kai tayi tace a'a dama sune suka taimaka mata ta tattaro kayan to sun tambayi miyasa zata bar hostel shine ta fad'a masu shine yazo daukarta, "ni wa?" taji ya jefo mata tambayar ta d'an waro ido don bata tsammaci jin tambayar ba da k'yar ta bashi amsa da wanda zata aura kawai sai gani tay ya d'an ta6e baki ya maida idon shi kan wayar dake hannun shi, tambayar shi tayi tace suzo su gaisan taga ya jinjina mata kai ba tare daya kalleta ba, d'agowa tay tace masu suzo su gaisa duk suka matso bakin Motar Fauzy taja gefe, a tare suka rankwafa suka ce mashi ina wuni a wani slow ya juyo gaba d'ayan su saida gaban su ya fad'i karma Zainab taji wani kallon k'urulla ta shiga bin shi dashi tana k'ok'arin tuna inda ta san shi, jinjina masu kai yayi kamar anyi mashi dole koda yake Kusan hakan ne yace masu ya School a tare suka had'a baki wurin amsa mashi da lafiya lou suka ce anzo lafiya anan dai kai suka samu ya jinjina masu daga haka suka ce sai anjima suka janye kan su, idanu a waje Zainab ke kallon Fauzy dake d'an murmushi tana son yi mata magana amman ba dama sai faman kallon ta take da alamun Al'ajabi, sallama ta k'ara yi masu ta shiga ciki har ta rufe k'opar sai kuma suka ga ta bude, kud'i ta mik'a ma Zainab rafar yan dubu dubu sabbi dal ta dubu d'ari tace gashi ance su raba saidai Sa'adatu ce ta amsa don gaba d'aya Zainab tayi Mutuwar tsaye, har Motar ta bar harabar Makarantar suna tsaye cirko cirko saida ta 6ace ma ganin su sannan suka juya kan Zainab nan fa suka shiga yaba irin kyaun shi har Sa'adatu na fad'in ko ina ta samo shi sai kuma tace ta tuna lokacin da aka raba kayan saka ranarta ance d'an uwan mijin Fateema Ard'o ne ba mamaki don an gan shi haka, Safiya ce tace amman dai da gani ya jik'u da Naira wllh ga mugun aji ji yadda yay masu magana ma, sai lokacin Zainab da still tsananin mamaki ke a kwance akan fuskar ta tace "to ku duk baku ma san wani abu ba, wllh wanccan mutumin da kuke ganin shi d'an Governor ne" zaro ido sukai tare da bud'e baki a tare suka furta "d'an Governor!!!" Kai ta d'aga masu cike da tabbaci tace masu da suka je bikin Fateema Ard'o Abuja a kan idonta suka zo shida Mahaifiyar shi da yan uwan shi a cikin jiniya d'an Governor d'in Nasarawa ne... Nan ta kwashe komai har yadda Sameer d'in ya fito daga cikin Mota ya shiga cikin gidan da dangantakar shi da Mijin Fatuu ta fad'i masu, nan fa duk suka shiga tsananin mamaki ba dai kamar Zainab da kanta ya gama daurewa ta yadda akai har suka san juna shida Fauzy har abun ya kai ga za'ai aure, a fili ta furta ashe shiyasa suna dawowa ta canza waya zuwa latest iPhone, gaba d'aya al'ajabi ma ya hana su yin murnar kud'in da aka basu da alama kuma gobe dole Fauzy tasha tambayoyi a wurin Zainab.
Suna fitowa daga cikin Makarantar cikin girmamawa driver d'in ya d'an juyo ba tare daya kalli Sameer d'in ba ya tambayi ina zasu, kallon Fauzy yayi da tayi zuru yace ta bashi address d'in gidan Sister d'in ta tace to, basu wani d'auki lokaci ba suka karaso Unguwar don kusa take da Makarantar tasu, kallon shi tay bayan sun tsaya ya d'an d'age kanshi jikin seat idanunshi a lumshe, ce mashi tay sun iso ya d'an d'aga mata kai ta k'ara cewa suje, shiru kaman bazai tanka ba can ya juyo suka had'a ido yace taje ta sanar ta d'aga mashi kai, lokacin data fito Driver d'in na tsaye yana ganinta cikin girmamawa ya tambayi kayan boot fito da su za'ai tace mashi eh, yana k'ok'arin d'aukar mata bayan ya fito dasu tace mashi ya bashshi zata d'auka yace to bari ya kai mata ko bakin gate tayi gaba yana biye da ita a baya, lokacin data shiga cikin parlon tsaye tay tana bin shi da kallo yasha uban gyara sai uban k'amshi ke tashi har labulaye an canza haka kujerun ma da gani har goge su akai don sunyi haske a ranta ta raya lalle Aunty tayi kokari, d'akin Aunty ta nufa lokacin data shiga a zaune ta isketa gaban mirror tana yin shafa, jin sallamar Fauzyn yasa ta juyo suka had'a ido, d'an waro ido tay tace to lafiya ta ganta da kaya nik'i nik'i tana murmushi tace sabon mai iko da ita ne yace ta dawo ta gama yin boarding, k'ara waro ido Aunty tay sai kuma tayi dariya, tambayar ina yake ta yi ta bata amsa da yana waje,
Suna fitowa daga cikin Makarantar cikin girmamawa driver d'in ya d'an juyo ba tare daya kalli Sameer d'in ba ya tambayi ina zasu, kallon Fauzy yayi da tayi zuru yace ta bashi address d'in gidan Sister d'in ta tace to, basu wani d'auki lokaci ba suka karaso Unguwar don kusa take da Makarantar tasu, kallon shi tay bayan sun tsaya ya d'an d'age kanshi jikin seat idanunshi a lumshe, ce mashi tay sun iso ya d'an d'aga mata kai ta k'ara cewa suje, shiru kaman bazai tanka ba can ya juyo suka had'a ido yace taje ta sanar ta d'aga mashi kai, lokacin data fito Driver d'in na tsaye yana ganinta cikin girmamawa ya tambayi kayan boot fito da su za'ai tace mashi eh, yana k'ok'arin d'aukar mata bayan ya fito dasu tace mashi ya bashshi zata d'auka yace to bari ya kai mata ko bakin gate tayi gaba yana biye da ita a baya, lokacin data shiga cikin parlon tsaye tay tana bin shi da kallo yasha uban gyara sai uban k'amshi ke tashi har labulaye an canza haka kujerun ma da gani har goge su akai don sunyi haske a ranta ta raya lalle Aunty tayi kokari, d'akin Aunty ta nufa lokacin data shiga a zaune ta isketa gaban mirror tana yin shafa, jin sallamar Fauzyn yasa ta juyo suka had'a ido, d'an waro ido tay tace to lafiya ta ganta da kaya nik'i nik'i tana murmushi tace sabon mai iko da ita ne yace ta dawo ta gama yin boarding, k'ara waro ido Aunty tay sai kuma tayi dariya, tambayar ina yake ta yi ta bata amsa da yana waje,