Sashe 53
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan su Laila sun gama salla take ma Fanan Albishir don jiya ta riga tahowa kuma lokacin data dawo tayi bacci, waro ido Fanan tay ta kai hannu ta rufe bakinta alamar mamaki Laila nata Murmushi, cire hannun tayi cike da farinciki tace kenan duk abubuwan nan da ake Zarah is pregnant Laila tace wllh ai Allah ma ya taimaka da ba abunda ya same shi, mik'ewa Fanan tay da sauri ta nufi bakin gado ta kai hannu kan bedside ta d'auki wayarta, Haisam ta kira lokacin ya koma part d'in shi don ya shirya, yana tsaye a gaban dressing mirror kiran ya shigo ya juya ya kallo wayar dake saman bedside kafin ya nufeta, yana ganin mai kiran yay murmushi ya kai hannu yay picking, daga muryarta zaka fahimci tana cikin farinciki tace mashi ashe jiya abunda ya faru kenan bayan ta baro wurin yana ta murmushi yace mata eh, ce mashi tay shine ko ya kirata ya sanar da ita abun farincikin daya same su tama yi fushi dashi, yanayin yadda tay Maganar har saida yayi yar dariya, hak'uri ya bata yace tayi bacci ne yana son ta huta sosae tace to miyasa yanzu da aka tashi bai sanar mata ba ai kamata yay ace shine mutum na farko daya fara sanar mata, hak'uri ya k'ara bata yace mata yana niyyar yazo ne da kan shi sai yay mata Albishir yanzu haka yana gaban mirror yana mata Kwalliyar da zai zo yi mata Albishir d'in, yana jiyo sautin dariyar ta dama ya fad'i ne don ya faranta mata, ce mata yay gashi nan zuwa yi mata Albishir d'in a d'okan ce tace she's waiting for him,
Bayan Jidderh ta gama komai ta had'a mashi a cikin basket part d'in taje ta sanar mashi ta gama yay mata godiya yace ta aje mashi a dining area tace to, har zata juya ya tsaidata, ce mata yay ta d'aukko ma Fatuu kayan da zata canza ta sa towel da brush d'inta sai ta aje mashi a wurin basket d'in tace to kafin ta tafi, bada jimawa ba ya fito yana sanye da k'ananun kaya bak'in jeans da dark blue t-shirt sumar nan ta sha gyara sai baza k'amshi yake, part d'in Laila ya wuce lokacin daya shiga ba kowa cikin parlon hakan yasa ya wuce Bedroom, knocking k'opar yay aka bashi izinin shigowa ya tura ya shiga da yar sallama, Duk suna kwance akan gado Laila tuni ta koma bacci sai Fanan ce idonta biyu ta kasa komawa baccin sai tunane tunane take, sosae taji farincikin samun cikin da Fatuu tay saidai ta wani bangaren zuciyarta ce ta k'ara sarewa ta shiga tunanin anya kuwa tana da rabon haihuwa a duniya ganin tana ta shan Magani kuma ana samun cigaba amman har yanzu ko 6ari bata yi ba tasan ma ko zata iya conceiving, a hankali take kai hannu tana share kwallan dake gangaro mata tana haka taji anyi knocking saida ta goge Fuskarta tass sannan ta bada izinin a shigo, tana ganin shi da sauri ta saukko daga gadon tana sanye da rigar bacci iya gwuiwa kanta ta saka hula gashin ta ya zubo ta gefe da gefe, nufo shi tay da sauri tun kafin ta k'araso ya bud'e mata hannuwan shi tana zuwa ta fad'a jikin shi ya maida hannuwan ya rungumeta sosae ta shiga fad'in she's happy for them bada jimawa ba zasu zama iyaye, murmushin jin dad'i ya shiga saki ya d'aura ha6ar shi a saman kanta tare da lumshe ido, daga lokacin data amince mashi ya cigaba da zama da Zarah ya gane irin son da yake mata, a yadda yake ji he can't live without her, jin tana k'ok'arin d'ago da fuskar ta yasa shi janye ha6ar tashi, d'agowa tay ta kalle shi suka shiga sakar ma juna k'ayataccen murmushi daka kalli fuskokin su zaka fahimci suna cikin farin ciki don cike suke da annuri, suna haka calmly taji ya furta mata "Thank you Sweetheart" d'an bud'a mashi ido tay tace akan me ya lumshe ido yace "For Everything" fad'awa tay jikin shi ta kwantar da kanta a chest d'in shi, yaci gaba da fad'in "har bansan ta yadda zan rink'a gode maki ba, nagode maki da kasance man mafi jin dad'in duniyar nan" wurin kunnanta ya kai bakin shi ya rad'a mata "al'mar'atussaliha" yana jin yadda ta k'ara shige mashi yana ta murmushi,
d'ago kai tay ta kalle shi tace "komai daga wurin ka na koya babe, sadaukarwa halin ka ne, baka da buri sai na kaga kasa mutum farinciki hakan ne yasa kai ma kake kasancewa acikin farinciki koda yaushe, Babe duk yadda na kasance maka kai kaja hakan you're a selfless and just person, da maza zasu yi koyi da halin ka da sun zauna lafiya da matan su koda sunfi d'aya don hakan zai rink'a rage masu radadin kishi, amman da yawa su suke jefa matan su a mawuyacin hali k'arshe suzo suna kauce hanya wanda hakan bashi ne way out ba sai ma mutum ya halaka, Idan ba kayi cuta ba bazaka ga cuta ba all one needs to do shine hak'uri tunda Allah da kan shi yace yana tare da mai shi in mutum yayi sai yaci riba,ina rok'on Allah yasa in ci ribar hak'uri though nama fara cin ribar ga baby nan zamu samu" ta k'arasa tana murmushi, still yay yana kallonta wani irin tausayin ta ne ke ratsa shi, maida kanta yayi jikin shi yace in sha Allah zata samu lafiya itama ta Haifa mashi yara masu irin halinta, tana murmushi tace Allah ya amince amman in ya kaddaro mata bazata haihun ba ba komai tasan daga cikin hikimar sa ne ya kawo Zarah ta Haifa masu, murmushi kawai yake wani lokacin sai yay ta ganin kaman ba ita ba don da kuruciyarta bata da hak'uri ga kukan banza, sigh yay ya d'agota yace bari yaje, tambayar shi tay inda zashi ya fad'i mata da sauri tace to bari ta shirya sai su tafi tare, ba tare da ya sake ta ba gently yace mata yana son yaje da wuri ne Saboda grandma d'inta ta dawo gida jiya ta kwana ba shiri ko blanket babu yasan bata yi bacci cikin dad'i ba ta bari ta shirya a nutse sai suzo da Laila in ma ita bazata zo ba in ta shirya tay mashi magana zaisa a kawo mata makullin Mota sai ya bata address na Hospital d'in, kai ta jinjina mashi ya d'an sunkuyo yay pecking goshinta had'i da furta "I love u" farfar tay da ido ta furta mashi tana son shi da kowane bugu na zuciyar ta, yar dariya yay ya saketa tace in yaje yay kissing baby d'in su dariya Maganar ta bashi yace mata har ya zama baby kenan tace eh ai zai zama ne in sha Allah, bayan ya fito dining area ya nufa ya d'auki basket d'in da yar jakar kayan sannan ya tafi.
Bakin gado ta koma cike da zumud'i ta d'auki wayarta ta fara k'ok'arin kiran Mom d'inta, saida kiran ya kusa katsewa sannan tayi picking, gaishe da ita Fanan tayi muryarta ciki ciki ta amsa, cike da Farinciki tace mata dama ta kira tayi mata Albishir Hajiya Maryam d'in tace mata miya faru ne, cikin washe baki ta hau bata labarin cikin da Zarah ta samu tana jiyo sautin d'an tsoki data buga kafin a hasale tace to shine zata tashe ta a bacci kaman dole kuma tasan a lokacin bacci take, hak'uri ta bata tace farinciki ne yayi mata yawa shiyasa ta kira don ta taya su murna, bata ce mata komai ba tay shiru can ta tambayi ina Noor ta bata amsa da tana a wurin su twins ta furta Ok, jin zata katse kiran yasa da sauri tace bata taya ta murna ba a dak'ile tace Allah yasa Alkhairi daga haka ta katse kiran sam Fanan bata ji komai ba, kiran Farha ta shiga yi bayan tayi ringing tay picking, gaishe da Fanan d'in tayi ta amsa ta tambayi ko bacci take ta bata amsa da No tana yin Assignment ne, ce mata tay ta tayata murna bride d'in su is pregnant Farhar tay d'an jimm sai kuma tace ta taya ta murna Fanan d'in tay mata godiya, tambayar ta tay yaushe zata dawo tace msta cikin week d'in da za'a shiga tay mata sai ta dawo daga haka sukai sallama.
Bayan Jidderh ta gama komai ta had'a mashi a cikin basket part d'in taje ta sanar mashi ta gama yay mata godiya yace ta aje mashi a dining area tace to, har zata juya ya tsaidata, ce mata yay ta d'aukko ma Fatuu kayan da zata canza ta sa towel da brush d'inta sai ta aje mashi a wurin basket d'in tace to kafin ta tafi, bada jimawa ba ya fito yana sanye da k'ananun kaya bak'in jeans da dark blue t-shirt sumar nan ta sha gyara sai baza k'amshi yake, part d'in Laila ya wuce lokacin daya shiga ba kowa cikin parlon hakan yasa ya wuce Bedroom, knocking k'opar yay aka bashi izinin shigowa ya tura ya shiga da yar sallama, Duk suna kwance akan gado Laila tuni ta koma bacci sai Fanan ce idonta biyu ta kasa komawa baccin sai tunane tunane take, sosae taji farincikin samun cikin da Fatuu tay saidai ta wani bangaren zuciyarta ce ta k'ara sarewa ta shiga tunanin anya kuwa tana da rabon haihuwa a duniya ganin tana ta shan Magani kuma ana samun cigaba amman har yanzu ko 6ari bata yi ba tasan ma ko zata iya conceiving, a hankali take kai hannu tana share kwallan dake gangaro mata tana haka taji anyi knocking saida ta goge Fuskarta tass sannan ta bada izinin a shigo, tana ganin shi da sauri ta saukko daga gadon tana sanye da rigar bacci iya gwuiwa kanta ta saka hula gashin ta ya zubo ta gefe da gefe, nufo shi tay da sauri tun kafin ta k'araso ya bud'e mata hannuwan shi tana zuwa ta fad'a jikin shi ya maida hannuwan ya rungumeta sosae ta shiga fad'in she's happy for them bada jimawa ba zasu zama iyaye, murmushin jin dad'i ya shiga saki ya d'aura ha6ar shi a saman kanta tare da lumshe ido, daga lokacin data amince mashi ya cigaba da zama da Zarah ya gane irin son da yake mata, a yadda yake ji he can't live without her, jin tana k'ok'arin d'ago da fuskar ta yasa shi janye ha6ar tashi, d'agowa tay ta kalle shi suka shiga sakar ma juna k'ayataccen murmushi daka kalli fuskokin su zaka fahimci suna cikin farin ciki don cike suke da annuri, suna haka calmly taji ya furta mata "Thank you Sweetheart" d'an bud'a mashi ido tay tace akan me ya lumshe ido yace "For Everything" fad'awa tay jikin shi ta kwantar da kanta a chest d'in shi, yaci gaba da fad'in "har bansan ta yadda zan rink'a gode maki ba, nagode maki da kasance man mafi jin dad'in duniyar nan" wurin kunnanta ya kai bakin shi ya rad'a mata "al'mar'atussaliha" yana jin yadda ta k'ara shige mashi yana ta murmushi,
d'ago kai tay ta kalle shi tace "komai daga wurin ka na koya babe, sadaukarwa halin ka ne, baka da buri sai na kaga kasa mutum farinciki hakan ne yasa kai ma kake kasancewa acikin farinciki koda yaushe, Babe duk yadda na kasance maka kai kaja hakan you're a selfless and just person, da maza zasu yi koyi da halin ka da sun zauna lafiya da matan su koda sunfi d'aya don hakan zai rink'a rage masu radadin kishi, amman da yawa su suke jefa matan su a mawuyacin hali k'arshe suzo suna kauce hanya wanda hakan bashi ne way out ba sai ma mutum ya halaka, Idan ba kayi cuta ba bazaka ga cuta ba all one needs to do shine hak'uri tunda Allah da kan shi yace yana tare da mai shi in mutum yayi sai yaci riba,ina rok'on Allah yasa in ci ribar hak'uri though nama fara cin ribar ga baby nan zamu samu" ta k'arasa tana murmushi, still yay yana kallonta wani irin tausayin ta ne ke ratsa shi, maida kanta yayi jikin shi yace in sha Allah zata samu lafiya itama ta Haifa mashi yara masu irin halinta, tana murmushi tace Allah ya amince amman in ya kaddaro mata bazata haihun ba ba komai tasan daga cikin hikimar sa ne ya kawo Zarah ta Haifa masu, murmushi kawai yake wani lokacin sai yay ta ganin kaman ba ita ba don da kuruciyarta bata da hak'uri ga kukan banza, sigh yay ya d'agota yace bari yaje, tambayar shi tay inda zashi ya fad'i mata da sauri tace to bari ta shirya sai su tafi tare, ba tare da ya sake ta ba gently yace mata yana son yaje da wuri ne Saboda grandma d'inta ta dawo gida jiya ta kwana ba shiri ko blanket babu yasan bata yi bacci cikin dad'i ba ta bari ta shirya a nutse sai suzo da Laila in ma ita bazata zo ba in ta shirya tay mashi magana zaisa a kawo mata makullin Mota sai ya bata address na Hospital d'in, kai ta jinjina mashi ya d'an sunkuyo yay pecking goshinta had'i da furta "I love u" farfar tay da ido ta furta mashi tana son shi da kowane bugu na zuciyar ta, yar dariya yay ya saketa tace in yaje yay kissing baby d'in su dariya Maganar ta bashi yace mata har ya zama baby kenan tace eh ai zai zama ne in sha Allah, bayan ya fito dining area ya nufa ya d'auki basket d'in da yar jakar kayan sannan ya tafi.
Bakin gado ta koma cike da zumud'i ta d'auki wayarta ta fara k'ok'arin kiran Mom d'inta, saida kiran ya kusa katsewa sannan tayi picking, gaishe da ita Fanan tayi muryarta ciki ciki ta amsa, cike da Farinciki tace mata dama ta kira tayi mata Albishir Hajiya Maryam d'in tace mata miya faru ne, cikin washe baki ta hau bata labarin cikin da Zarah ta samu tana jiyo sautin d'an tsoki data buga kafin a hasale tace to shine zata tashe ta a bacci kaman dole kuma tasan a lokacin bacci take, hak'uri ta bata tace farinciki ne yayi mata yawa shiyasa ta kira don ta taya su murna, bata ce mata komai ba tay shiru can ta tambayi ina Noor ta bata amsa da tana a wurin su twins ta furta Ok, jin zata katse kiran yasa da sauri tace bata taya ta murna ba a dak'ile tace Allah yasa Alkhairi daga haka ta katse kiran sam Fanan bata ji komai ba, kiran Farha ta shiga yi bayan tayi ringing tay picking, gaishe da Fanan d'in tayi ta amsa ta tambayi ko bacci take ta bata amsa da No tana yin Assignment ne, ce mata tay ta tayata murna bride d'in su is pregnant Farhar tay d'an jimm sai kuma tace ta taya ta murna Fanan d'in tay mata godiya, tambayar ta tay yaushe zata dawo tace msta cikin week d'in da za'a shiga tay mata sai ta dawo daga haka sukai sallama.