← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 85 OF 211

Sashe 85

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Yanzu shi Baba so yake wai aji ta bakin ki don yama rasa yadda zai tafi da Al'amarin" shiru Fauzy tay idonta acikin na Aunty can ta fara girgiza mata kai "Aunty kice mashi kada ya amince su zo ban son Auren shi" waro ido Aunty tay "amman Saboda me Fauziyya, ba abunda dama muke fata ba kenan??" Idanun Fauzy ne suka ciko da k'walla cikin karyayyar murya tace "Haba Aunty ina ake haka fisabilillahi, ko don mu talakawa ne shine zai nuna mana iko haka, bafa soyayya muke dashi ba hasalima bai ta6a nuna man wani alamu na yana so na ba kawai kuma sai ace wai zai aure ni to wane irin aure ne haka zamu yi dashi don Allah?" Shiru Aunty tay tana kallonta k'wallan suka fara zubo mata, ajiyar zuciya Aunty tay tace "amman Fauziyya ba kina son shi ba?" Da sauri tace "ko ina son shi Aunty ni bazan yarda ya nuna man iko haka ba, don ina talaka ai nima inada daraja ba yadda za'ai yayi man wannan ikon, a tunanin shi komai ne ake iya nuna iko, to bazan Aure shi ba gaskiya" ta k'arasa tana girgiza kai harda d'an huci ta kumbura baki, hannu Aunty ta kai ta kama hannunta cikin kwantar da murya ta fara magana "ni ina ganin tunda kinsan halin shi Fauziyya bai kamata ki tada hankalin ki haka ba, k'ilan shi ba da niyyar nuna iko yayi hakan ba...." Katseta tay "iko ne mana Aunty tunda ai yasan ba Soyayya muke da shi ba" d'an cize le6enta na k'asa Aunty tayi kafin tace "watak'il fa shi a wurin shi a hakan soyayya yake dake kinsan Mutane irin shi suna da wuyar fahimta wllh, kiyi tunani tun farko da kuka san juna laifi fa kikai mashi amman kuma ya cigaba da kula ki yana maki abubuwan Alheri kinga ta yuwu kamar yadda nace a wurin shi soyayya yake dake, kuma tabbas yana son ki shiyasa har yasa a zo nema mashi auren ki, tunda kinsan halin shi Fauziyya hakan bai kamata ya dame ki ba har ki fatali da wannan babbar damar da kika samu wadda ko a film da wuya kiga wata ta samu irin damar ace dai d'an Governor zai auri d'iyar talaka " shiru Fauzy tay har lokacin da k'walla a cikin idanunta, still hannun Aunty na a ruk'e da nata,

"Tunda kina son shi ki amince kawai mu taru muyi fatan Allah yasa hakan Alkhairi ne kuma watak'il sakayyar abunda Mujaheed yay maki ne Allah yayi maki dama in dai aka cuci mutum yayi hak'uri ya bar ma Allah tabbas sai ya saka mashi" shiru tay tana ta bin ta da ido Auntyn tace mata tayi magana mana, motsa baki ta fara tana yamutsa fuska tace "to ni Aunty mi kike so in ce, wai ina aka ta6a Aure haka don Allah mutumin nan fa ko halin shi bamu sani ba shin yana da kyakkyawan hali ko mummuna ba wanda ya sani sannan kuma ni wllh ina zargin shi ma, akan ido na fa yasha giya kuma yaje Club taya mutum mai kyaun hali zai aikata hakan, ni dai gaskiya Aunty ina ganin gara mu hak'ura da shi kawai kar azo ayi abunda za'a dawo ana dana sani kema kinsan irin yaran masu kud'i da Mulkin nan sai a Hankali wllh" ta k'arasa tana girgiza kai,

"Amman mijin Zarah haka yake? Kuma ai baki da tabbas din giya d'in ce kika ga yasha ko tunda ai ke ba saninta kikai ba, kuma da ya sha kinga ya bugu ne tunda ai kun d'an jima tare sannan yayi maki wani abu na kaucewar hankali? In da ya bugu kema kinsan yadda kuka kasance ku biyu kawai wllh sai dai Allah ya k'wace ki kuma ko da bai bugu ba inda d'an iska ne na tabbatar da sai ya nuna maki halin shi a wurin, sannan Maganar zuwa Club tare kuka shiga ne? Ina ce a cikin Mota ya bar ki kinga kenan baki da ikon zargin shi tunda ai baki san miya shiga yayi ba duk da ansan ba wurin Arziki bane amma ba kyau ki munana mashi zato" kallonta kawai Fauzy take fuska a kwabe,

"Yanzu in don sanin halin shi ne ai Mijin Zarah na nan ko zan kirata in sa ta tambayar mana shi komai da muke son sani na tabbatar bazai 6oye mana komai ba, ni kuma na maki Alkawarin indai aka tabbatar yana da wani mugun hali da ya kamata a guje ma auran shi to zan goya maki bayan hakan" ganin bata ce komai ba yasa tace mata hakan yayi mata, d'an yamutsa fuska tay a raunane tace "to amman Aunty yanzu misali ace baida wata illa haka zan aure shi ko fa sona bai ta6a cewa yana yi ba, ni nafi tunanin ma Saboda labarin dana bashi na Mujaheed ne yasa ya yanke aure na matsayin ya taimaka man" d'an murmushi Aunty tay tace "in ma don hakan ne ai ba laifi bane sau nawa dama ake aure ba soyayya duk yawancin iyayenmu ba haka sukai auren ba kuma suka zauna lafiya, yanzu aure nawa ne akai a turbar soyayyar yazo ya lalace mudai fatan mu ai ya ruk'e mana ke da kyau ne kiji dad'in Auren, wani Maganar soyayya in kunyi auren kun yi in ma bai iya ba sai ki koya mashi abun ai duk mai sauki ne balle ma wllh irin wad'annan mutanen sun mugun iya love ki bari ayi Auren zaki ban labari dama yanzu ai bazai sake maki ba tunda yana ji da shegiyar izzar tsiya, ke ni ki bari indai damuwar ki ya furta yana son ki ne nayi maki Alkawarin sai furta wannan Kalmar ya zame mashi tamkar cin Abincin shi, yadda zai ci Abinci safe da rana da dare to ina mai tabbatar maki haka zai rink'a fad'in I love you Fauziyya",

duk da yanayin da take ciki saida ta d'an yi dariya Aunty ta k'ara cewa "Allah kuwa, ke baki ga yadda mijin Zarah ba ya shigo hannu sai faman rawar k'afa yake akanta ko ba'a fad'a ba daka gani kasan ta kama shi gamm to shima hakan zamu kama shi wuyarta dai ayi Auren hakan ba wani abun wahala bane wllh" d'an ta6e baki Fauzy tay tana d'an murmushi,

"Yanzu ya kika ce Your Excellency, a kira Zarah d'in ko mu fad'i mata abubuwan da muke so mu sani game dashi d'in?" wani kallo Fauzy tay mata tana yar dariya kafin a hankali ta d'aga mata kai alamar eh, da sauri Aunty ta kai hannu ta 6akar mata shoulder tace "su Excellency ana so ana kaiwa market" dariya Fauzy ta saka tana fad'in Allah ita ba wani son shi da take.

Fatuu zaune a parlor tana kallo tana sanye da doguwar riga Boubou ta lace cikin kayan data ba Kb ya d'inka mata daga baya akai mata d'inkunan da Hajiya tace , bata dad'e da fitowa daga Kitchen ba tayi ma Haisam Abinci da yake tunda yazo ita ke mashi Abinci har ce mata yay ta bari a rink'a yi acan part d'in Hajiya ita ta huta amman tak'i, wayarta dake a gefenta ce ta fara ringing ta kai hannu ta d'aukko, ganin mai kiran nata yasa tay d'an murmushi ta kai hannu tay picking,

"Aunty Mareeya ina wuni, barka da juma'a" ta fad'a bayan data yi sallama, amsa mata tayi ta tambayi ya suke harda unborn tana yar dariya tace mata duk lafiya lou suke ga unborn d'in ma yaji suna waya yace/tace a gaishe ta, dariya Maganar ta bata tace to tana amsawa ai in Allah ya yarda biyun ne duka ita dai Fatuu murmushi kawai tayi,

"Yauwa Zarah nace don Allah ko mijin ki na nan?" Fatun tace "a'a Aunty yau da safe ya tafi Kano yin wani aiki amman dai a yau zai dawo yace man in sha Allahu da Magrib jirgin su zai sauka" jinjina kai tay tace to Allah ya dawo dashi lafiya bayan ta amsa tace "Amman Aunty lafiya dai ko?"

"lafiya lou yar gidana sai ma Alkhairi in sha Allahu...." nan ta kwashe komai game da zuwa neman Auren Fauzy da za'ai da kuma yadda sukai da Fauzyn, tsananin mamaki ne ya bayyana akan fuskar Fatun gaba d'aya ta washe baki tana dariyar farinciki tace "Amman Aunty wllh naji dad'in wannan labarin wayyo Allah na, muna ta jiran ya furta yana son ta ko sun fara soyayya suyi aure ashe mai gaba d'aya zai yi.." Aunty ta amshe "Wllh haihuwa da hanji ba" dariya Fatuu tasaka nan ta fad'i mata abubuwan da take so ta tambayar mata Haisam a d'okance tace to in sha Allahu yana dawowa zasu yi Maganar Allah dai yasa suji Alkhairi Aunty tace "Amin ya Rabbi yar gidana shine abun da zamu yi fata kam" bayan sun gama wayar ta tambayi ina amarya Fauzy,
yar dariya Aunty tay tace "ga abu nan tayi wuri wuri Sameer yayi mata bazata" Fatun nata dariya tace a bata, bayan ta amshi wayar tsokanarta Fatuu ta shiga yi ita dai sai uhhm take daga baya ta hau yin Addu'ar Allah ya tabbatar masu da Alkhairi.
Chapter 85 · 0% Book details