Sashe 153
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ƙarfe sha biyu na yi sun gama ayyukan da suke su Aunty mareeya da Feenah suka tafi don su shiryo zuwa kai amarya Fatuu ma ta wuce gida don ta shirya zuwa lokacin tuni gidan ya cika da mutane ƙawayen gwaggo da yan'uwanta harda iyalin Kawu shibaɗo da shi kan shi yazo daurin auren, Jirage kawai keta kai da komowa yan ɗaurin aure sai zuwa suke zuwa lokacin Mutane sosae sun taru a gidan su Haisam na G.r.a yan uwa da abokan arzuƙi da abokan siyasa na Senator duk sun hallara har Sameer ma ya iso haka ma 6angaren Angon Laila duk sun dawo nan gidan don a tafi tare , lokacin sallar Juma'a na masallacin da za'a ɗaura auren wato Masallacin Banu Commassie na gabatowa aka shirya convoy na Motoci masu sunan Motoci aka tafi Magana ake ta harkar masu arzuƙi daya amsa sunan Arzuƙi abun sai wanda ya gani don alƙalami bazai iya zayyana ainihin ƙayatuwar ba, suma can 6angaren iyayen Mino Maza Tk da Kawu Amadu ne suka ɗaukko su a Motoci, Massallaci fa ya cika dankam da mutane ga tsaro ta ko ina don ma yana da girma da ba lalle ya isa ba, ana gama salla ɗaurin Auren su aka fara yi bayan waliyyai na kowanne 6angare sun hallara aka fara ɗaura na Dr Bashir da Dr Laila bayan an gama aka ɗaura na Engr Nameer da Ameenatu kowanne akan sadaki Naira 500 dubban mutane suka shaida, bayan angama kowa fuskar shi ɗauke take da farinciki aka shiga gaishe gaishe da fatan alkhairi ga ma'auratan yan jarida muna ta aikin ɗaukar rahoto, bayan an gama mutanen 6angaren Angon Laila Hotel ɗin da suka sauka can suka koma don yin reception bangaren su Senator kuwa G.r.a suka koma acan zasu yi nasu a Masallacin ma an raba ma mutane uban Abinci da lemuna sai Addu'oi ake ma ma'auratan da kuma Senator Ali Zakee ana faɗin Allah yayi mashi President sai murmushi yake yana gaisawa da mutane har saida jami'ai suka dakatar dasu, acan 6angaren gidan su amarya duk sun sha ankon atampa mai kyau da suka yi kowa ka gani yayi kyau cikin atampar har Hajiya da Saude duk suma ita suka saka anata hotuna da wayoyi, yan G.r.a na gama yin reception ɗin gidan Hajiya suka nufo harda Senator nan fa unguwa ta cika ango Nameer yasha babbar rigar bugaggar shadda light blue haka hular shi da agogon shi zuwa takalmanshi duk sun hau da kalar shigar da yayi sam ya kasa rufe baki hakanan ma yayi murmushi balle yanzu da dalili Allah ya mallaka mashi Babynshi yar fillo, su Kawu Amadu abokan ango duk sun sha shaddoji kowa dai yayi kyau Hajiya na ganin Nameer ta rungume shi tana faɗin duk da tana kishi tana farinciki kuma da Allah ya nuna mata wannan rana su Senator dasu Kawu Mani yan Daura nata dariya, bangaren amarya Mino kuwa tana a part ɗin Fatuu ƙwararriyar mai makeup dake a Katsina wato Munah Beauty tana tsantsara mata kwalliya, fitted gown din rantsattsan lace Navy blue da ratsin light da kuma fari mai kaman silver tasa sai net light blue an ci bakin shi da bakin lace ɗin jikinta aka yafa mata sai head ɗinta shima light blue ne clutch da takalmanta kuma silver sai sarƙarta da yan kunnanta na Diamond, Wow Ma sha Allah shine abunda aketa faɗi, bayan Munah Glam ta gama tsantsara mata kwalliya ta naɗa mata head su Aunty Mareeya suka shiga tambayar ina aka samo mai makeup ɗin nan Fatuu ta bata amsa da Babbar ƙawar Mino wato Safnah ta kawo masu ita tace da Sunan Yayarta ita tayi masu Makeup harda ma ƙunshi na zane dana salataf duk tana yi Feenah tace kenan har ƙunshin ita tayi masu Safnah dake zaune gefen Mino itama tana jira ayi mata make up ɗin ta bata amsa da eh har itama nata duk ita tayi masu, sosae suka yaba da ƙunshin shima Aunty Mareeya tace ansha da ita da ta sani itama tare dasu akai mata ya zanu raɗam haka ta ɗan harari Fatuu tace duk laifinta ne da bata sanar masu ƙwararrar mai ƙunshi zata masu ba suma ayi masu Fatuu na dariya ta bata haƙuri tace itama bata santa ba saida Safna ta kawo ta, dafa shoulder ɗin mai makeup da ƙunshin Aunty Mareeya tayi ta tambayeta irin abubuwan da take yi ta fara lissafo mata bangaren kwalliya tace suna yin ta Amare da masu Jego ko ta Birthday ko simple da za'a ma mutum don zuwa biki ko suna sannan tana koya ma mutum in yana so a bangaren ƙunshi kuma tana yin baƙi na zane da kuma ja na zane dana salataf irin wanda ke yin maroon ko kuma baƙi sannan suna yin kitso iri iri sai wanda mutum keso sannan kuma suna yin Home service wato in mutum naso a iske shi a gida ayi mashi kowanne cikin abubuwan data lissafa, tambayarta Feenah tay ya yanayin price ɗin aikin nata yake ta shiga faɗi mata ai tun kafin ta ƙarasa Aunty Mareeya ta miƙa mata waya da sauri tana faɗin yar albarka saka man lambar wayarki aikuwa su Fatuu da Aunty Feenah suka kwashe da dariya Feenah na faɗin su Maman Hanif an ji sauƙi tana dariya tace to yanzu a rayuwar nan ai sauƙin ake nema harda tsawwalawar da wasu masu makeup ɗin ke yi yasa da yawa wasu suke haƙura da yin gayun duk da suna so amman ba hali Feenah tace gaskiya kam wasu kuma sai hidima ta kama sannan suyi duk da mace da gayu aka santa amman in dai mutum zai samu Munah Glam saidai in shi ke bai son gyara kanshi, Aunty Mareeya tace ta bari kawai ai ita yanzu kakarta ta yanke saƙa gayu sai in ba'a yi yanzu ta ƙara samun tarkon da zata ƙara damƙe zuciyar Abban su hanif dama shi ɗan son gayu ne shiyasa bata wasa yanzu kuma zata ƙara ƙaimi da Munah Glam, bayan ta saka mata lambar ta miƙa mata tana cikin yin saving Feenah tace itama ta karanto mata tace to ta fara karanto mata lambar kamar haka 08169856268, Bayan an gama shirya amarya Mino Fatuu akai mawa da yake wadda za'a mata ba irin ta Mino bace hakan yasa ba'a ɗauki lokaci sosae ba aka gama aka ɗaura mata kallabi abun sai wanda ya gani Babyn Haisam itama ta fito kamar Amarya, Safnah aka shiga yi mawa bayan Fatuu ana gama mata Aunty mareeya tace itama duk da tayo kwalliyar daga gida a gyara mata ita ana cikin yi mata Haisam ya kira Fatuu yace mata ta kawo Mino part ɗin Hajiya yanzu tace to, ita da Safnah suka tafi kai Minon, lokacin da suka shiga parlon Hajiya gaba ɗaya idanu suka dawo kan su da sauri Mino ta sadda kanta ƙasa a haka suka nufi cikin parlon ango Nameer sai sakin ƙayataccen murmushi yake yaga yar fillon shi ta zama tamkar tauraruwa gashi yanayin shigarsu ta haɗu don head ɗin da aka ɗaura mata da mayafinta da kuma fulawoyin lace ɗinta sun yi kala ɗaya da shaddar shi da gani dai tsara hakan sukai, idon Haisam na akan Babyn shi Fatuu da yaga ta ƙara mashi kyau sosai wurin Hajiya suka nufa da ita tana ta murmushi ta miƙo hannu ta kamo na Mino ta zaunar da ita a gefenta tana yaba kwalliyarta harda cewa wato shine aka ƙi kawo mai yin kwalliyar tayi mata don ansan in aka yi mata sai tafi Amaryar kyau duk akai dariya su Fatuu da suka zuƙunna akan Carpet suka shiga gaishe da mutanen ciki suna ta amsawa harda Senator sukai mata ya hidima, Mino sarkin kunya gaba ɗaya ta kasa ɗagowa balle ta gaisa da mutane hakan yasa Hajiya tace ma Fatuu ta kamata ta kai ta wurin su Senator, a gaban shi suka tsugunna da ƙyar Mino ta ɗago ta gaishe shi yana ruƙe da Adam ya kai ɗayan hannun shi ya dafa shoulder ɗinta yana murmushi ya tayata murna tare dasa ma Auren nasu Albarka yace yana farinciki da shigowarta Family ɗin tare da yin Addu'o'i ya juya kan Fatuu yace ita Daughter yanzu ta zama yar gida sai dai ta tarbi wasu Fatun tay yar dariya ta ɗaga mashi kai tare da faɗin hakane saida tayi magana sannan Adam ya gane itace ya fara miƙo mata hannu yana faɗin Momy duk akai dariya don sun fahimci bai ganeta ba farko saboda Makeup da aka mata, Hotuna aka shiga yi anan cikin parlon Hajiyar lokacin da Mino ta jera da Nameer za'a yi masu har saida na furta Ma sha Allah wato kyau ya haɗu da kyau sai ya bada Madarar kyau.......
99
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~
99
~_*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*_~