← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 123 OF 211

Sashe 123

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

A Ranar da daddare duk suna a part d'in Fatun harda Hajiya da Haisam da Nameer gaba d'aya yan gidan anata hira ana cin naman suna ana korawa da lemu Aunty na ta cema su Jidderh wllh su bi a hankali ganin yadda suke ta d'irka kamar sun samu Abinci wai naman dad'i yafi wanda aka saba soya masu Hajiya tace ai haka naman suna yake, suna anan Dad ya dawo shima ya nufo nan part d'in su twins suka mik'e da gudu suna mashi oyoyo ya ruk'e su ganin bakin su jage jage da mai yace miye suke ci haka a tare suka ce naman suna ne ya d'an waro ido yace shine ko a tuna dashi suka ce ai akwai da yawa sosae ya d'aga kai suka nufo ciki, sannu da zuwa aka shiga yi mashi yana amsawa bayan ya zauna ya gaishe da Hajiya tayi mashi an dawo lafiya ya amsa Jidderh tace a zubo mashi naman shima yace anya dare ne fa suma suci a hankali in mutum yaci ya kwanta yana iya samun matsala Aunty Laila dake taunar naman tace ai zasu sha flagyl kafin su kwanta duk aka saka dariya, shima d'an kad'an yasa aka bashi ya fara ci abun gwanin sha'awa k'arshe dai saida Aunty tasa aka d'auke naman daga falon, Bayan Dad ya gama ne aka bashi tissue ya goge hannun shi ya kai hannu cikin aljihun rigar yar cikin shi dama saida yaje part d'in shi ya cire babbar rigar sannan ya nufo nan, wasu takardu ya fiddo guda biyu ya mik'a ma Mom yace taba Daughter gashi nan takardun gidaje ne guda biyu a cikin na Estate d'in shi yaba Abokanshi su daga yanzu kud'in hayar su nasu ne a bud'a masu Account a rink'a saka masu, wata irin shewar farinciki su Aunty Laila da Jidderh sukai su Mom da Aunty ma sai dariyar farinciki suke suna yi ma Dad d'in godiya da Allah ya kara girma da Arzuki, bayan an mik'a ma Fatuu takardun a sanyaye tayi mashi godiya da Addu'ar Allah ya k'ara girma da daukaka yanata amsawa, Hajiya ce tace wato salon sabon Angonta yaga bata yi farinciki da shi ba shiyasa zai masu wannan babbar kyauta haka to itama baza'a barta a baya ba ta basu d'aya daga cikin filayenta na Katsina wannan karon ihun murna Aunty Laila ta saka tana fad'in kaga yara masu k'ashin arzuki daga zuwan su duniya har sun zama masu arzuki,

"Wai to sai ba yaran kyauta kuke ita Mom d'in tasu fa?" Jidderh ce ta fad'a tana tura baki idonta akan Dad d'in su yana yar dariya yace yana sane da ita in sha Allah ita da yar'uwarta zasu je Hajjin bana amman tunda da sauran lokaci zasu fara zuwa Umra gaba d'aya gidan zo kaga farinciki su twins harda rawa suna fad'in dama an dad'e ba'a je dasu ba, Mom ce tace Shikenan ma in suka je sai a biya Qatar a gaido Abie Dad yace ba matsala ya kalli Fatuu yafe ta fad'i daga nan in akwai wata k'asa da take son zuwa Albarkacin su twins sai a wuce tayi shiru tana ta murmushi tama rasa mi zata ce don gaba d'aya bakin ta ya mutu su Aunty Laila na ta fad'i don Allah, Haisam ne yace sun kusa fara Final Exams d'in su ne bai fi nan da 2 Months ba Dad na jin hakan yace to a tsaya daga Qatar d'in, kallon Hajiya Jidderh tayi tace to itama bata ba Aunty Fanan da Fatuu kyautar ba ta d'an kwa6e fuska tace dole sai ta basu suma Aunty Laila tace eh gaskiya tace to ta basu kowa kaza da zakara suyi kiwo gaba d'aya aka saka dariya Fanan tace ta gode zata tafi US dasu tayi kiwon acan Aunty Laila tace gaskiya kyautar tayi kad'an Hajiya ta d'an harareta tace to ina laifi tasan Arzikin da zasu iya janyo masu Jidderh tace duk da haka dai gaskiya sunyi kad'an,

"To tunda had'in kai za'a nuna man Shikenan na basu kowa tunkiya da rago daga haka bazan k'ara ba" dariya aka fashe da ita Dad yace ai wannan ma ta basu mai yawa don tushen garke ne gaba d'aya sukai godiya,

"to wai shi Angon jegon fa banga an bashi komai ba" Aunty ta fad'a Dad na dariya yace "k'yale wannan mai kud'i ne shi" tace duk da haka dai shima a bashi gaskiya Arzik'in su twins Dad d'in ya kalle shi yace yana son wani abu ne a hankali ya girgiza kai yana murmushi yace a'a an gode da wanda aka bada Allah ya k'ara lafiya da Arziki suka amsa da Amin, Dad ya kalli Aunty yace to taji dai bai son komai tana yar dariya tace to ai ba haka yakamata a yi mashi ba shima sai a bashi kawai ba ai mashi tayin rowa ba duk akayi dariya Hajiya tace to ai shima ba za'a je dashi Umra d'in ba Aunty Laila tace wannan to na Dad ne saura ita ta bashi kyautar tace Shikenan shi ta bashi kaza da zakaran da suka guda duk aka kwashe da dariya harda Haisam d'in abun gwanin nishad'i haka suka cigaba da yin firar su lokacin Dad ya tambayi Hajiya nan da 2 weeks lafiya lou za'a iya yin tafiya da yaran Saboda suje su dawo Daughter ta koma School tace mashi eh yace to sai su shirya duk aka k'ara yi mashi godiya.

Bayan sati guda da yin suna yan Ethiopia suka koma lokacin saura sati d'aya su Fatuu su tafi Umra, sosae take samun kulawa gaba d'aya ita da yaran sunyi 6ul6ul dasu gwanin sha'awa, ana saura kwana ukku su tafi Hajiya tace mata in akwae kayan da za'a tafin mata dasu Katsina ta bada tunda da sun dawo zasu wuce can tace to. Lokacin da suka je Umra Fatuu harda kukanta na farinciki ganin gata ga ka'aba, sosae tayi Addu'oi daga cikin wanda tafi yi ma Addu'a akwae Mahaifiyarta da Mahaifinta sai mijinta da gwaggo, Hajiyar Sanata da kuma iyalin Sanata d'in sai sauran yan'uwanta da Abokan Arzuki harda Haulat bata manta da ita ba tayi mata Addu'ar Allah ya bata miji wanda zai kula da rayuwar ta da yarinyar ta, Satin su guda suka wuce Qatar sosae aka karramasu ba kamar Fatuu da su twins sai faman nan nan ake dasu gidan Yaya Othman d'in da suka sauka shi kan shi abun kallo ne don duniya ce mai zaman kanta ko ina walwali ke tashi kai kace da zallar gold aka yi gidan Fatuu ta girgiza da ganin gidan don bata ta6a zaton a rayuwarta zata ganta a cikin gida ba irin wannan, sun zaga garin sun sha hotuna sosae garin da suka je ya had'u Over don shine babban birnin su wato Doha, Birni ne na zamani kuma na duniya mai kyawun sararin samaniya, akwae gidajen tarihi da abubuwan jan hankali na al'adu kuma babbar cibiya ce ta kasuwanci da yawon bude ido na duniya, nan ma sati guda sukai suka juyo Abuja Haisam da Fanan kuma suka wuce US, kwanan su biyu da dawowa suka dawo Katsina, Ranar da suka dawo da daddare Fatuu ta nufi gidan su Haulat tare da Mino ta goya mata yaro guda don tana nan ta dawo anan take takaba don tun bayan rasuwar mijin nata bata jin dad'i hakan yasa aka dawo da ita nan yanzu ma har ta kusa gama takabar, lokacin da suka ga juna ita da Fatuu kuka sukai ta yi innar su na basu hakuri tana ruk'e da yaran tayi ma Fatuu barka tace taso tazo Abuja suna to Saboda yanayin da haulat take ciki yasa bata zo ba Fatun tace mata ba komai itama tana ruk'e da d'iyar Haulat, sosae tausayin Haulat ya kamata ganin yadda ta rame tana kwalla ta shiga rarrashinta kan ta rage damuwa tayi hak'uri tay d'an murmushi tace wllh ta bari ta rungumi kaddararta kawai abun ne wani lokacin in ya taso mata sai taji damuwa, k'arfafa mata gwuiwa ta shiga yi tace in sha Allahu zata samu miji wanda zai kula da ita ya ruk'e Umma Salma tamkar d'iyar shi a sanyaye Haulat d'in tace Allah yasa amman ita yanzu ma gaba d'aya auren ya fitar mata a rai Fatuu tace ta daina cewa hakan don zai zama tamkar bata yarda da kaddarar ta ba ta mik'a komai ga Allah in sha Allahu zai ji6anci lamuranta tace Allah yasa, anan ta kira Haisam ta bashi Haulat d'in ya k'ara mata gaisuwa, sosae Haulat ta yaba da su twins haka ma innar su sai faman fad'in Tubarkallah take daga baya sukai masu sallama suka tafi, Bayan komawar su gida Fatuu ta kira Aunty Mareeya ta sanar mata jini ya d'auke mata tun kafin su tafi Umra Saboda tafiyar yasa bata sanar mata ba amman ta fara amfani da wasu magungunan da Yadikko ta kawo mata tace to zata ba Fauzy sak'o ta kawo mata, washe garin da suka dawo ne Hajiya tayi ma Saude Magana akan ko za'a samo ma Fateema mai raino da zata rink'a taimaka mata Saboda zuwa Makaranta tace to za'a samu zata yi magana can gidan su, a Ranar da yamma Fatuu ta had'a uban kaya su atamfofi da lace harda dogayen riguna wasu daga cikin nata da tasan zasu yi ma Haulat da kayan shafa harda naman suna da kuma kud'i dubu hamsin taba Mino tace ta kai mata tace mata ta fara amfani dasu, lokacin da takai kayan Haulat kuka ta saka a haka cikin kukan ta kira Fatun a waya tace ya zatai mata wannan uwar dawainiyar tace mata ba komai tana dasu ne ita dai fatanta ta kwantar da hankalinta ta daina damuwa tace in sha Allahu ta daina, har gida washe gari innar su tazo tayi mata godiya harda rigunan jarirai ta kawo ma su twins taje tayi ma Hajiya barka anan take ce ma innar tasu ashe Haulat d'in gida ta dawo ta fad'i mata bata jin dad'i ne gashi ta saka damuwa a rai cike da tausayawa Hajiya tace ai dole ne don rashin miji ba K'aramin rashi bane tace ayi mata gaisuwa sai tazo innar tayi mata godiya kafin ta tafi.
Chapter 123 · 0% Book details