Sashe 65
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"In sirri kuke son yi ai sai kuce in baku wuri ba ku canza harshe ba in d'auka gulmata kuke" Hajiya ta fad'a ta d'an kwa6e fuska duk sukai dariya, gwaggo ce tay mata bayanin cewa wai tana son ba k'awar ta atampa ne shine itama take ganin ya dace a ba su Yaya da yadikkonta amman bata san ko zasu iya hakan ba, hannu Hajiya ta kai ta ruk'e ha6a tace "Oni yasu, to Dije mi zai hana, ai kaya yanzu sun zama naku waya isa ya hana kuyi yadda kuke so da su in banda abun ki" gwaggo na murmushi tace dama wai taga kayan manya ne Hajiyar tace to ko manyan ne fa ai dai nata ne ko, kuma ai akwae atampopi suna nan da ba'a d'in ka ba tasan k'ilan bai wuce ma don hakan yasa ba'a d'inka su ba tunda yawancin kayan duk an d'inka, duk abunda zaku bada ku bada ba ruwan kowa da wannan" godiya gwaggo tayi mata tana yar dariya sai kawai ma Hajiyar ta mike ta nufi hanyar fita, Fauzy gwaggo tay ma magana ta mik'e taje suka sauke akwatunan, na kayan suka fiddo bayan an bud'e gwaggo tace ma Fatuu ta zo ta d'aukar ma Haulat d'in, wata atamfa mai golden tayi kyau sosae ta d'aukar mata, Su Yaya da Kishiyar ta da Yadikko suma duk atampopin aka d'aukar masu, ta Yadikko ma glitter ce mai kyau, wani lace tasa aka d'aukar ma k'annanta su Aysha sai k'awarta Zainab ma ta d'aukar mata wata sarka da yan kunne masu kyau dama ankon lace d'inta ta bar mata, su Aunty Mareeya ma da Feenah da Saude yan kunne fashion aka d'aukar masu kai da gani kasan zasu yi kud'i don ba k'ananu bane, akwatin cosmetics tasa Fauzy ta bud'e mata ta k'ara ma su Aysha da kayan shafa, gudun abun kar yay yawa yasa gwaggo da fullanci tace mata a bar su haka Fatun tace da su Baffan ta take son d'aukar ma shadda tace mata a'a an basu ta k'yale su in ma tana son basu ta bari a basu daga baya, Fatun tace to bari a basu ko turare ta d'aukar masu guda ukku daga haka gwaggo tace to a bashshi,
kallon Fauzy Fatuu tayi tace mata ta d'auki duk abunda take so da sauri ta girgiza mata kai tace wllh ba abunda zata d'auka duk uwar hidimar da akai dasu ga anko mai tsada har kala biyu gwaggo dai murmushi kawae take, madaidaicin akwati aka d'auko bayan an kwashe kayan cikin shi an maida cikin wani suka zuba kayan da suka d'aukar a cikin shi har Fauzy zata rufe Fatuu ta dakatar da ita, wani akwati ta nuna mata tace don Allah ta d'aukko mata, bayan ta jawo mata shi tasa ta bud'e, had'add'un dogayen riguna ne a ciki duk a Dubai aka siyo su Fatuu ta kai hannu ta ciro wata army green mai shegen kyau tasha adon stones, bayan ta saka cikin kayan tace ma Fauzy ta rufe, maida akwatunan sukai yadda suke da, tambayar gwaggo Fatuu tay jakarta da ta zuba kud'in da ta samu ranar Walima dama ita taba ajiya, bayan ta d'aukko mata ta bud'eta cikinta dankam take da kud'i, envelope d'in da Alhaji Lawal ya bata ta fiddo ta bud'e, kud'i ne a ciki bandir din yan dubu na dubu d'ari, maida su tay cikin envelope d'in ta d'auketa bayan ta rufe jakar ta mik'a ma gwaggo tace to ita da zasu tafi, ce mata tay ta tafin mata da ita kawae ba abunda zata yi da su don tana da kud'i sosae a account d'in ta.
A tare suka fito daga cikin d'akin Fauzy na janye da akwatin kayan, a parlor suka iske Hajiya zaune tace ma Fatuu ta k'yale su suje ita ta koma taje ta natsu wuri guda a marairaice tace mata tana son yin sallama dasu ne, lokacin da suka isa part d'in bayan gaba d'aya a parlor suka iske su don Abbas ya kira Feenah yace bada jimawa ba zasu tafi su zama cikin shiri, gaishe gaishe aka shiga yi ana k'ara yi ma Fatuu ya jiki bayan sun gama gwaggo tasa Fauzy ta bud'e akwatun, fiddo kayan su Yadikko tay harda turarurrukan su Ard'o ta nufi d'akin da suke don ta kai masu, suma na nan parlon Fauzy ta shiga fiddo na kowa tana bashi farko duk cewa sukai don Allah a bashshi banda duk uwar Hidimar da akai masu, saida gwaggo ta fito ta saka baki sannan suka amsa suna ta godiya da Addu'oi cike da Farinciki su Yadikko ma duk suka fito suna nuna masu nasu sai murna suke karma su Yaya da innar Altine su ji sam sun kasa rufe baki, fiddo kud'in da Fatuu tazo dasu tay ta shiga ba kowa dubu biyar biyar Haulat dae dubu talatin ta bata harda wanda zata yi kud'in Motar komawa Niger, nan fa parlor ya kacame anata farinciki Aunty Mareeya harda cewa in haka ake yin biki ai ba abunda zai hanata zuwa in dai ba ciwo ya kai ciwo ba duk aka sa dariya dama tun ran Asabar duk aka basu abubuwan da akayi na bikin, fakaitar idanun mutane Fatuu tay ta d'aukko trolley d'in Fauzy dake a cikin parlon, bud'e shi tay ta d'aukko jallabiyar da ta sako cikin kayan ta tura acikin akwatin kayan Fauzy data lura saboda a kusa da ita take tana niyyar yin Magana ta hau yi mata magiyar kar tace komai, wani kallo tay mata mai kamar harara Fatun ta saka dariya,
Gaba d'aya tare suka fito lokacin wuraren k'arfe goma yan Katsina da yan Adamawa harda wasu yan Daura, a gaban Entry Hall aka jere Motocin gaba d'aya duk an fito da yan tafiya da yan rakiya su Hajiya, Mom, Laila, Fanan, nan aka shiga yin bankwana Haisam da Abbas na daga can gefe sun jingina da Motar Abbas haka su Kawu Amadu da Tk da Kamalu ma duk suna gefe, Jidderh Saboda tafiyar tasu dama tak'i zuwa School Aunty dae ta tafi wurin aiki dama tayi sallama dasu kafin ta tafi Fatuu ji take kamar a tafi da ita, had'a ido sukai da Haisam ta yamutsa fuska ya saki murmushi don ya gane mi take nufi, Mino ma sai kallon love suke ita da Nameer suna sakar ma juna murmushi, Dad ne ya fito tare dasu Ard'o Fatuu ta nufe su ta gaishe su duk suka amsa Dad yay mata ya karfin jiki tace Alhamdulillah, kallon Baffan ta dake ta sakar mata murmushi tay itama murmushin take mashi sun kasa ce ma juna komai, kud'i Dad ya fiddo ya shiga raba ma duk masu tafiya aka hau godiya daga baya suka fara shiga cikin Motocin bayan an sassaka kayan su, d'aga ma juna hannu suka shiga yi kamar kar a rabu a Kusan tare duk suka tashi Motocin suna ta cigaba da d'aga ma juna hannu a haka suka tafi sai fatan Allah yasa a sauka lafiya, tsaye Fatuu tay idanun ta sun ciko da k'walla gaba d'aya har kewar su ta fara kamata, bayan barin Motocin aka tuk'o wadda Senator zai hau ta tsaya a gaban wurin dama a shirye yake, sallama yay da iyalin nashi duk sukai mashi sai ya dawo bayan an bud'e mashi k'opa ya shiga suka tafi, Haisam ne ya matso gaban Fatuu suka had'a ido a shagwabe ta tura mashi baki yay murmushi, Hajiya ce tace mata to suje ya kai hannu ya kamo hannunta duk kunya ta kamata suka nufi cikin gidan........
87
.......Alhamdulillah matafiya duk anyi waya da su sun isa lafiya gaba d'aya sai fatan Allah ya huta gajiya, bayan sallar isha Fatuu ta gama sallar tana zaune a saman gado jikinta sanye da voile material pink d'inkin riga da skirt tayi d'aurin kallabi mai kyau daga cikin kayan lefenta ne yayi mata kyau sosae, ruk'e take da wayarta tana bin chat d'in group d'in su na School da ake hirar komawa Makarantar bayan sun gama taya Fatuun murna data tura masu pics d'in bikin nata da akai,
kallon Fauzy Fatuu tayi tace mata ta d'auki duk abunda take so da sauri ta girgiza mata kai tace wllh ba abunda zata d'auka duk uwar hidimar da akai dasu ga anko mai tsada har kala biyu gwaggo dai murmushi kawae take, madaidaicin akwati aka d'auko bayan an kwashe kayan cikin shi an maida cikin wani suka zuba kayan da suka d'aukar a cikin shi har Fauzy zata rufe Fatuu ta dakatar da ita, wani akwati ta nuna mata tace don Allah ta d'aukko mata, bayan ta jawo mata shi tasa ta bud'e, had'add'un dogayen riguna ne a ciki duk a Dubai aka siyo su Fatuu ta kai hannu ta ciro wata army green mai shegen kyau tasha adon stones, bayan ta saka cikin kayan tace ma Fauzy ta rufe, maida akwatunan sukai yadda suke da, tambayar gwaggo Fatuu tay jakarta da ta zuba kud'in da ta samu ranar Walima dama ita taba ajiya, bayan ta d'aukko mata ta bud'eta cikinta dankam take da kud'i, envelope d'in da Alhaji Lawal ya bata ta fiddo ta bud'e, kud'i ne a ciki bandir din yan dubu na dubu d'ari, maida su tay cikin envelope d'in ta d'auketa bayan ta rufe jakar ta mik'a ma gwaggo tace to ita da zasu tafi, ce mata tay ta tafin mata da ita kawae ba abunda zata yi da su don tana da kud'i sosae a account d'in ta.
A tare suka fito daga cikin d'akin Fauzy na janye da akwatin kayan, a parlor suka iske Hajiya zaune tace ma Fatuu ta k'yale su suje ita ta koma taje ta natsu wuri guda a marairaice tace mata tana son yin sallama dasu ne, lokacin da suka isa part d'in bayan gaba d'aya a parlor suka iske su don Abbas ya kira Feenah yace bada jimawa ba zasu tafi su zama cikin shiri, gaishe gaishe aka shiga yi ana k'ara yi ma Fatuu ya jiki bayan sun gama gwaggo tasa Fauzy ta bud'e akwatun, fiddo kayan su Yadikko tay harda turarurrukan su Ard'o ta nufi d'akin da suke don ta kai masu, suma na nan parlon Fauzy ta shiga fiddo na kowa tana bashi farko duk cewa sukai don Allah a bashshi banda duk uwar Hidimar da akai masu, saida gwaggo ta fito ta saka baki sannan suka amsa suna ta godiya da Addu'oi cike da Farinciki su Yadikko ma duk suka fito suna nuna masu nasu sai murna suke karma su Yaya da innar Altine su ji sam sun kasa rufe baki, fiddo kud'in da Fatuu tazo dasu tay ta shiga ba kowa dubu biyar biyar Haulat dae dubu talatin ta bata harda wanda zata yi kud'in Motar komawa Niger, nan fa parlor ya kacame anata farinciki Aunty Mareeya harda cewa in haka ake yin biki ai ba abunda zai hanata zuwa in dai ba ciwo ya kai ciwo ba duk aka sa dariya dama tun ran Asabar duk aka basu abubuwan da akayi na bikin, fakaitar idanun mutane Fatuu tay ta d'aukko trolley d'in Fauzy dake a cikin parlon, bud'e shi tay ta d'aukko jallabiyar da ta sako cikin kayan ta tura acikin akwatin kayan Fauzy data lura saboda a kusa da ita take tana niyyar yin Magana ta hau yi mata magiyar kar tace komai, wani kallo tay mata mai kamar harara Fatun ta saka dariya,
Gaba d'aya tare suka fito lokacin wuraren k'arfe goma yan Katsina da yan Adamawa harda wasu yan Daura, a gaban Entry Hall aka jere Motocin gaba d'aya duk an fito da yan tafiya da yan rakiya su Hajiya, Mom, Laila, Fanan, nan aka shiga yin bankwana Haisam da Abbas na daga can gefe sun jingina da Motar Abbas haka su Kawu Amadu da Tk da Kamalu ma duk suna gefe, Jidderh Saboda tafiyar tasu dama tak'i zuwa School Aunty dae ta tafi wurin aiki dama tayi sallama dasu kafin ta tafi Fatuu ji take kamar a tafi da ita, had'a ido sukai da Haisam ta yamutsa fuska ya saki murmushi don ya gane mi take nufi, Mino ma sai kallon love suke ita da Nameer suna sakar ma juna murmushi, Dad ne ya fito tare dasu Ard'o Fatuu ta nufe su ta gaishe su duk suka amsa Dad yay mata ya karfin jiki tace Alhamdulillah, kallon Baffan ta dake ta sakar mata murmushi tay itama murmushin take mashi sun kasa ce ma juna komai, kud'i Dad ya fiddo ya shiga raba ma duk masu tafiya aka hau godiya daga baya suka fara shiga cikin Motocin bayan an sassaka kayan su, d'aga ma juna hannu suka shiga yi kamar kar a rabu a Kusan tare duk suka tashi Motocin suna ta cigaba da d'aga ma juna hannu a haka suka tafi sai fatan Allah yasa a sauka lafiya, tsaye Fatuu tay idanun ta sun ciko da k'walla gaba d'aya har kewar su ta fara kamata, bayan barin Motocin aka tuk'o wadda Senator zai hau ta tsaya a gaban wurin dama a shirye yake, sallama yay da iyalin nashi duk sukai mashi sai ya dawo bayan an bud'e mashi k'opa ya shiga suka tafi, Haisam ne ya matso gaban Fatuu suka had'a ido a shagwabe ta tura mashi baki yay murmushi, Hajiya ce tace mata to suje ya kai hannu ya kamo hannunta duk kunya ta kamata suka nufi cikin gidan........
87
.......Alhamdulillah matafiya duk anyi waya da su sun isa lafiya gaba d'aya sai fatan Allah ya huta gajiya, bayan sallar isha Fatuu ta gama sallar tana zaune a saman gado jikinta sanye da voile material pink d'inkin riga da skirt tayi d'aurin kallabi mai kyau daga cikin kayan lefenta ne yayi mata kyau sosae, ruk'e take da wayarta tana bin chat d'in group d'in su na School da ake hirar komawa Makarantar bayan sun gama taya Fatuun murna data tura masu pics d'in bikin nata da akai,