← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 126 OF 211

Sashe 126

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Cikin sa'a suka gama sai kuma ta k'arshen wato council, bayan sati guda suka fara yin ta duka kwana ukku sukai suka gama, a ranar gaba d'ayansu cikin tsananin farinciki suke sun sha ankon atamfofi sun d'aura jacket mai d'auke da sunayen su a baya ta Fatuu an rubuta RN Zarah ta Fauzy kuma RN Fauzy abun gwanin k'ayatarwa nan suka shiga d'aukar hotuna mutane sai so suke suyi hoto da su twins amman sun k'i yarda, Zainab Muhammadu ce tace wllh basu isa ba ayi bikin uwar su tare da ita gari ya gari har Abuja taje amman Suk'i yarda da ita, dole da tsiya ta d'auke su suna ta kuka suna ta6e baki irin dai yadda Fatuu ke yi da k'uruciyarta in zata yi kuka suma haka suke yi don lokacin da Haisam yazo har Magana yayi akan hakan yace ita suka biyo in zasu yi kuka yadda take.

Alhamdulillah shine abunda su Fatuu keta fad'a da suka kammala karatun nasu lafiya, tare da Fauzy suka dawo gida saida suka fara tsayawa a gidan gwaggo akai ta taya su murna da Addu'ar samun sakamako mai kyau daga baya suka koma gida nan ma su Hajiya da Saude kowa dai ya taya su murna Haisam ma tun bayan da suka fito daga jarabawar ya kirata ya taya ta murna da fatan sakamako mai kyau haka ma Sameer shima ya kira Fauzy ya taya ta murna.

Kwana ukku da gama jarabawar su Sameer yazo Katsina Ranar ya kama Alhamis dama ya sanar ma Fauzyn zai zo ya tafi da ita Abuja can za'ai masu pre wedding pics, da yamma jirgin su ya tashi zuwa Abuja, duk da hawanta ne na farko ba laifi ta dake saidai itama taji juwa kamar yadda Fatuu tayi, gabda kiran Magrib suka sauka Aunty Laila ce taje d'aukko su don itama ta gama karatunta ta dawo dama komawar da tayi Final Exams zasu yi, gidansu suka wuce su Mom suka tarbeta hannu bibbiyu sosae Jidderh ta nuna farinciki da zuwanta shi dama Sameer ya wuce part d'in Haisam, d'akinta Aunty Laila ta wuce da ita tana zuwa salla ta fara yi bayan ta gama anan ta kawo mata Abinci da abun sha cikin fara'a tace mata ta taso taci d'an anjima zasu fita ne tace to, ba laifi ta saki jiki taci Abincin Jidderh na gefenta tana mata hira, ana gama sallar isha suka fito zasu tafi harda Jidderh tana jaye da wani madaidaicin trolley bayan sunyi sallama dasu Mom suka fito, a parking space suka had'e da Sameer yayi wanka ya canza kaya suka hau wata dankareriyar Jeep Sameer d'in ne ya shiga driver seat Fauzy na niyyar shiga baya Aunty Laila tace ta hau gaba su kuma suka shiga bayan yaja suka tafi. Wani sananne kuma tsadadden wurin hoto suka je wurin mai girman gaske ne gashi ya matuk'ar Had'uwa don iya ginin wurin abun kallo ne fitilu masu k'ayatarwa ne ta ko ina kai kace da rana ne, akwai manyan Studios d'in d'aukar hoto sai kuma na kwalliya haka akwae restaurant a wurin sannan akwai had'addan parlon hutawa ko jira, suna zuwa ba 6ata lokaci don ansan da zuwan su sunyi booking aka fara yi ma Fauzy Makeup abunka da kwararru ba'a d'au lokaci ba aka gama sosae Fauzy tayi kyau abun ba'a magana harda gashinta aka gyara, shima Sameer d'in saida aka gyara mashi fuska ya k'ara fitowa sosae, bayan sun gama ne suka nufi wurin canza kaya aka bud'e trolley d'in da suka zo da su wanda gaba d'aya sababbin kaya ne aciki wanda aka d'inka ma Fauzy tsadaddu kuma had'add'un gaske kala daban daban, hotuna daban daban aka shiga yi masu saida sukai kala goma kuma kowanne da kaya kala daban kama daga atamfa, lace, shadda, material, Abaya, English wears harda wanda aka yi masu da kayan aikin Sameer d'in irin kayan da injiniyoyi suke sakawa itama Fauzyn ta saka na mata ta saka irin hular da suke sakawa daga baya wurin wuyanta gashinta ya fito sosae tayi kyau kai kace ba bahaushiya ba, bayan sun gama ne aka yi masu wasu tare da su Aunty Laila. Aunty Mareeya bata yi niyyar fad'i ma iyayensu game da tafiyar Fauzyn Abuja tare dashi ba don tasan baban su bazai so hakan ba dole ya kalubalanci hakan saidai kuma tasan in aka yi hotunan dole suyi trending a social media kuma tabbas sai yan gidansu sun gani k'arshe Baban nasu zai iya gani shima, tunanin mafita ta shiga yi k'arshe ta yanke zata ce mashi kawai Katsina yazo akai masu. Washe gari ya sako Fauzyn jirgi ta dawo, a ranar da daddare saiga hotunan ya turo mata lokacin da ta gansu har saida tayi d'an ihun farinciki don sosae suka d'akku sunyi kyau har sun gaji gashi sun saka sutturu masu tsada haka d'inkunan da akai ma Fauzyn sun hau da jikinta sosae abundai saidai ace ma sha Allah, lokacin da Aunty ta gansu kasa rufe baki tayi tana ta faman yabawa tana fad'in Fauzyn kamar ba ita ba ta wanku iya wankuwa, kan kace mi hotunan har sun baza social media a daren Fatuu ma tun kafin Fauzy ta tura mata sai gashi ta kirata tana fad'in yayi kyau matar injiniya wannan zafafan hotuna haka, tambayar ta tayi a ina ta gansu tace gasu nan Aunty Laila ta d'aura a status harda su Jidderh har su Mom ma duk sun d'aura, sosae Fauzy tay mamakin yadda ake ta kiranta ana yaba hotunan tare da fatan Alkhairi abun har ta kasa rufe bakinta ma, gaba d'aya yan'matan Sameer sai yanzu suka san da zai yi aure ganin hotunan sosae mutane da dama sukai mamakin wadda zai aura sakamakon Comments d'in da aketa yi ana fad'in yar talakawa ce a Funtua local Government d'in Katsina take, haka aketa faman yin Comments mafi yawanci yabo ne ake tayi ana jinjina yadda d'an Governor ya auri d'iyar talakawa wasu na fad'in da ana yin haka a K'asar nan da an rage talauci sosae, wad'anda suka san Sameer d'in nata jinjina Al'amarin suna basu ta6a tunanin zai auri yarinya k'arama kuma yar talakawa ba, haka dai aketa maganganu gaba d'aya hotunansu sai trending suke ko ina ka shiga Maganar ake, ta 6angaren Sameer d'in yan matan shi sai kiran shi suke suna fad'in ya zai masu haka tare da jaddada mashi irin son da suke mashi wanda ya sani amman zai auri k'aramar yarinya kuma yar talakawa, to gaba d'aya dai amsa d'aya yake basu itace ita Allah ya k'addara mashi zata zama Matar shi kuma yana sonta, abokanan shi ma suna ta kira suna mashi Allah ya sanya Alkhairi.

MUJAHEED
Chapter 126 · 0% Book details