Sashe 166
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bayan sun dawo Abuja Washe gari Fatuu taje gidan Mino kai mata tsaraba Haisam ne ya kawota su twins a gida ta barsu, taji daɗin ganin yadda Mino ta saki jiki suna ta shan amarci da Nameer ta sha kananun kaya riga da wando, bayan data je ne Nameer ɗin ya fita, sosae Mino taji daɗin tsarabar data kai mata tace itama bada daɗewa ba zata je Yola Fatuu ta ɗan harareta tace ba yanzu ba sai ta shekara Minon ta noƙe kai tace "kai Adda Fatuu shekara yayi yawa ni dai gaskiya nan bada daɗewa ba zanje nasan dana nuna ma My Love ina son zuwa zai bar ni ƙilan ma tare zamu je" ɗan buɗa ido Fatuu tay ta ruƙe haba ta maimaita My Love ɗin da ta faɗa Mino ta saka dariya tare da rufe fuska alamar kunya, hira suka cigaba da yi anan Fatuu ke mata zancen Karatunta tace kar ta bari soyayya tasa ta shashantar dashi koda SSCE ne tayi ta samu result ɗin gama Secondary Minon tace eh rannan sunyi magana yace zata zana jarabawar sannan in zai tafi yin Master's Degree ɗin shi US zasu tafi tare sai taci gaba da Karatu a can, sosae Fatuu taji dadin jin hakan anan take sanar mata zancen komawarsu Us Mino ta marairaice fuska kamar zatayi kuka tace yanzu shikenan tafiya zatayi ta zama bata da kowa a nan Fatun tace mata kada ta damu tasan bazata yi maraicin rashinta ba tunda ga yan gidan su Nameer nan tasan zasu zame mata tamkar yan'uwa, tare suka shiga Kitchen yin abinci suna cikin yin aikin ne Mino ke faɗi mata wai Nameer yace in tana so a samo mata mai aiki da sauri Fatuu tace to ya tace mashi Minon tace cewa tayi ba sai an samo ba tunda ba wani aiki sosae sai yace wai ko gyaran gida ne a rinƙa yi mata, girgiza kai Fatuu tay tace kada a samo mata wata mai aiki ai gyaran gidan ma zata iya tunda ba wani datti yake yi ba inda take amfani dashi kullum kamar Bedroom, toilet da Kitchen su ta rinƙa gyara su kullum shi kuma falon tunda yana da girma in kamar taga bai 6aci ba tana iya bari sai bayan kwana biyu ta rinƙa sharewa amman zata iya kullum tasa towel ta goge kayan kallo da kujeru sai ta rinƙa saka turaren wuta akai akai koda zata yi mai aiki a bari ba yanzu ba sai kamar in ta samu ciki tayi nauyi kuma mai aikin ma kada ta bari a samo mata yarinya ko budurwa in ba haka ba a kwace mata My Love tana gani, dariya Mino tayi tace ita so take ma Aysha ta dawo wurinta shikenan ma ba sai tayi wata mai aiki ba Fatun tayi ɗan jimm alamar nazari kafin tace mata hakan ma yayi amman ta bari ba yanzu zata ɗaukkota ba tace to, bayan sun gama girkin saida suka gyara ko ina sannan suka zauna suka ci tare, Sai bayan Magrib Haisam yazo ɗaukarta lokacin Nameer ya dawo ya shigo cikin parlon suka gaisa Mino ta kawo mashi abun ta6awa da lemu daga baya sukai sallama. A ranar da daddare Haisam ke faɗi mata nan da sati guda zasu tafi Us, ana saura kwana ukku su tafi taje Katsina yin bankwana, har gidan Aunty mareeya da Feenah taje sannan taje gidansu Aminiyarta Haulat harda abun arziƙin data saba tayi mata taba Kawu Amadu makullin Motarta tace yaci gaba da yin amfani da ita, kwananta biyu ta dawo Abuja Washe gari wurin ƙarfe sha ɗaya suka tafi harda Mino amarya akai masu rakiya Airport daga nan Lagos zasu je wurin Fanan sai da daddare zasu tashi zuwa Us.
Fauzy taso zuwa Funtua bayan zuwan su amman Sameer yace tayi haƙuri ba yanzu ba don tana iya samun matsala in tayi wannan tafiyar a mota dole ta haƙura anan Nasarawa suka tsaya don zasu ɗan kwana biyu kafin su koma London, Bayan bikin Mino da kamar wata ɗaya lokacin satin su Fatuu biyu da komawa da daddare bayan sallar isha Gwaggo na zaune kan abun salla tun bayan data gama sallar take zaune a wurin kamar mai tunanin wani abu can ta kai hannu ta ɗaukko wayarta dake ajiye gefen abun salla ta shiga kiran Amadu, bayan ya ɗaga ta tambayi sun dawo daga masallaci ne yace mata eh ta ƙara tambayar ina Kamalu yace gasu nan tare a shago tace to shi ya shigo tana son ganin shi yace to, bada daɗewa ba ya shigo ɗakin da sallama ta ɗaga kai ta kalleshi tana amsawa ya nufi kan kujera ya zauna, gaishe da ita yayi ta amsa yace gashi ta ɗaga kai, shiru ta ɗan yi yanata kallonta can tace "Dama so nike in tambayeka wai kai baka son yin Aure ne?" ɗan waro ido yay sai kuma yayi yar dariya yace yana so mana amman miyasa tace haka ta ɗan ta6e baki tace taga baida niyya ne gashi yanata girma yanzu har ya fita daga shekara talatin amman bata ta6a jin yayi zancen yana da budurwa ba, yana dariya yace kawai shi soyayyarce ya ɗauketa 6ata lokaci don da yawa sai yaga an daɗe ana soyayya amman sai kaga anzo ba'a yi aure ba shiyasa Amman daya samu wadda suka fahimci juna zai yi auren, kai Gwaggo ta jinjina ta ɗan yi shiru tana kallon ƙasa ya fahimci kamar akwae wani abu a ranta hakan yasa shi tambayarta koda wani abu ta ɗago tana murmushi tace "Dama wata shawara ce nike son baka nace mi zai hana ka auri Haulatu duk da ba budurwa bace amman bata da wani aibu ina son yarinyar don tanada halin kirki kuma abunda aka fi buƙata kenan a wurin macen aure na tabbatar duk wanda ya aureta sai yaji daɗin zama da ita saboda tana da haƙuri sosae, ka duba yadda aka kasa yin ƙawance da Fatuu saboda halinta lokacin kuruciyarta amman haka Haulat ta jure duk da halinta na cika mutum haka taita haƙuri sa ita sukayi ƙawance har suka zama tamkar yan'uwa",
Shiru Kawu Amadu yay idonshi a ƙasa ganin haka yasa Gwaggon tace ita shawara ce ta bashi ba dole take mashi ba in bata yi mashi ba shikenan tana mashi Addu'ar Allah ya bashi wadda zasu daidaita mai halin kirki, ɗagowa yay yana murmushi yace a'a bawai bata yi mashi bane kawai yana mamakin yadda tunaninsu yazo daya ne don tun bayan dawowarta yaji yana son aurenta saida ya bari ta gama takaba sannan kwanaki yaje mata da Maganar amman sai bata yi na'am ba tace wai tursasa mashi akai kan ya aureta kuma tasan bai wuce Fatuu ce tasa saboda tausayinta da take amman in akace ya aureta ai an ƙware shi tunda ita yanzu ba budurwa bace, lokacin ya nuna mata shi ba wanda yasa shi shiya kawo kanshi to sai tace wai ya bata lokaci zata yi shawara to har yanzu zaman jiran amsarta yake ko bayan bikin su Mino saida yayi mata maganar amman sai ta ƙara cewa ya dai ƙara mata lokaci, Murmushi Gwaggo tayi tace ina ruwan Haulatu, duba agogon wayarta tayi taga lokaci kafin ta fara ƙoƙarin miƙewa tana faɗin bari taje gidan su, miƙewa yay shima yace suje ya rakata, bayan sun fito Amadu ya kwala ma Kamalu kira ya leƙo yace mashi zasu je su dawo yace to ya gaishe da gwaggo ta amsa tana murmushi, suna tafe suna hira gwanin sha'awa har kama Gwaggon yake lokacin da suka iso gidan a waje ya tsaya ita ta shiga, lokacin da tayi sallama innarsu Haulatun na a tsakar gida ta tarbeta da fara'a tana mata sannu da zuwa suka nufi ɗaki, bakin gado ta nuna mata Gwaggon tace bari ta zauna a kan tabarma dake shimfiɗe innar tace ya zata zauna a ƙasa don Allah, Gwaggo tana murmushi tace to ai ita ba baƙuwa bace ko kuma ai ba'a ƙasa bane tunda kan tabarma ne, itama innar zama tayi gefen gwaggon suka shiga gaisawa ta tambayi wurin su Fatuu da Amarya Mino duk tace mata suna nan lafiya, bayan sun gama gaisawa Gwaggo tace mata ina Haulat ne ta bata amsa da tana ɗakin ta ko ta kirata Gwaggon tace a'a tukunna, tambayar innar tayi ko sunyi magana data danganci Amadu da itane da alamun rashin fahimta ta bata amsa da a'a gaskiya, Gwaggo na murmushi a nutse ta shiga yi ma innar bayanin abunda ke faruwa tsakaninsu da Amadu sosae tayi mamaki har fuskarta ta bayyana tana murmushi tace wllh sam bata san da Maganar ba,
Fauzy taso zuwa Funtua bayan zuwan su amman Sameer yace tayi haƙuri ba yanzu ba don tana iya samun matsala in tayi wannan tafiyar a mota dole ta haƙura anan Nasarawa suka tsaya don zasu ɗan kwana biyu kafin su koma London, Bayan bikin Mino da kamar wata ɗaya lokacin satin su Fatuu biyu da komawa da daddare bayan sallar isha Gwaggo na zaune kan abun salla tun bayan data gama sallar take zaune a wurin kamar mai tunanin wani abu can ta kai hannu ta ɗaukko wayarta dake ajiye gefen abun salla ta shiga kiran Amadu, bayan ya ɗaga ta tambayi sun dawo daga masallaci ne yace mata eh ta ƙara tambayar ina Kamalu yace gasu nan tare a shago tace to shi ya shigo tana son ganin shi yace to, bada daɗewa ba ya shigo ɗakin da sallama ta ɗaga kai ta kalleshi tana amsawa ya nufi kan kujera ya zauna, gaishe da ita yayi ta amsa yace gashi ta ɗaga kai, shiru ta ɗan yi yanata kallonta can tace "Dama so nike in tambayeka wai kai baka son yin Aure ne?" ɗan waro ido yay sai kuma yayi yar dariya yace yana so mana amman miyasa tace haka ta ɗan ta6e baki tace taga baida niyya ne gashi yanata girma yanzu har ya fita daga shekara talatin amman bata ta6a jin yayi zancen yana da budurwa ba, yana dariya yace kawai shi soyayyarce ya ɗauketa 6ata lokaci don da yawa sai yaga an daɗe ana soyayya amman sai kaga anzo ba'a yi aure ba shiyasa Amman daya samu wadda suka fahimci juna zai yi auren, kai Gwaggo ta jinjina ta ɗan yi shiru tana kallon ƙasa ya fahimci kamar akwae wani abu a ranta hakan yasa shi tambayarta koda wani abu ta ɗago tana murmushi tace "Dama wata shawara ce nike son baka nace mi zai hana ka auri Haulatu duk da ba budurwa bace amman bata da wani aibu ina son yarinyar don tanada halin kirki kuma abunda aka fi buƙata kenan a wurin macen aure na tabbatar duk wanda ya aureta sai yaji daɗin zama da ita saboda tana da haƙuri sosae, ka duba yadda aka kasa yin ƙawance da Fatuu saboda halinta lokacin kuruciyarta amman haka Haulat ta jure duk da halinta na cika mutum haka taita haƙuri sa ita sukayi ƙawance har suka zama tamkar yan'uwa",
Shiru Kawu Amadu yay idonshi a ƙasa ganin haka yasa Gwaggon tace ita shawara ce ta bashi ba dole take mashi ba in bata yi mashi ba shikenan tana mashi Addu'ar Allah ya bashi wadda zasu daidaita mai halin kirki, ɗagowa yay yana murmushi yace a'a bawai bata yi mashi bane kawai yana mamakin yadda tunaninsu yazo daya ne don tun bayan dawowarta yaji yana son aurenta saida ya bari ta gama takaba sannan kwanaki yaje mata da Maganar amman sai bata yi na'am ba tace wai tursasa mashi akai kan ya aureta kuma tasan bai wuce Fatuu ce tasa saboda tausayinta da take amman in akace ya aureta ai an ƙware shi tunda ita yanzu ba budurwa bace, lokacin ya nuna mata shi ba wanda yasa shi shiya kawo kanshi to sai tace wai ya bata lokaci zata yi shawara to har yanzu zaman jiran amsarta yake ko bayan bikin su Mino saida yayi mata maganar amman sai ta ƙara cewa ya dai ƙara mata lokaci, Murmushi Gwaggo tayi tace ina ruwan Haulatu, duba agogon wayarta tayi taga lokaci kafin ta fara ƙoƙarin miƙewa tana faɗin bari taje gidan su, miƙewa yay shima yace suje ya rakata, bayan sun fito Amadu ya kwala ma Kamalu kira ya leƙo yace mashi zasu je su dawo yace to ya gaishe da gwaggo ta amsa tana murmushi, suna tafe suna hira gwanin sha'awa har kama Gwaggon yake lokacin da suka iso gidan a waje ya tsaya ita ta shiga, lokacin da tayi sallama innarsu Haulatun na a tsakar gida ta tarbeta da fara'a tana mata sannu da zuwa suka nufi ɗaki, bakin gado ta nuna mata Gwaggon tace bari ta zauna a kan tabarma dake shimfiɗe innar tace ya zata zauna a ƙasa don Allah, Gwaggo tana murmushi tace to ai ita ba baƙuwa bace ko kuma ai ba'a ƙasa bane tunda kan tabarma ne, itama innar zama tayi gefen gwaggon suka shiga gaisawa ta tambayi wurin su Fatuu da Amarya Mino duk tace mata suna nan lafiya, bayan sun gama gaisawa Gwaggo tace mata ina Haulat ne ta bata amsa da tana ɗakin ta ko ta kirata Gwaggon tace a'a tukunna, tambayar innar tayi ko sunyi magana data danganci Amadu da itane da alamun rashin fahimta ta bata amsa da a'a gaskiya, Gwaggo na murmushi a nutse ta shiga yi ma innar bayanin abunda ke faruwa tsakaninsu da Amadu sosae tayi mamaki har fuskarta ta bayyana tana murmushi tace wllh sam bata san da Maganar ba,