Sashe 175
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ka bar ni a tsaye haka ake welcoming baƙo" ta faɗa ta ɗan tura baki da sauri ya bata haƙuri yace ko zata shigo cikin shagon ga kujera ta girgiza mashi kai tace ciki zai shigar da ita zata gaisa da Grandma ɗin shi yace to, fitowa yay ya kulle ƙopar shago ta zagayo wurin shi yanata mata murmushi ganinta da kaya yace ta kawo ya ruƙe ta sakar mashi hannu guda suka kama tare suka nufi cikin gidan, faran faran Gwaggo ta tarbeta cikin sakin fuska a falo suka zauna ta gaishe da Gwaggon tana murmushi ta amsa mata tare da yi mata anzo lafiya da tambayar yan gidansu tace mata duk suna nan lafiya Kamalu yace ma Gwaggo tazo yin bautar ƙasa ne nan cikin fara'a tayi mata fatan alkhairi da fatan Allah ya bada sa'a yasa a gama lafiya ta amsa da Amin, miƙewa Gwaggo tayi ta fita daga cikin falon lokacin Farhar tace mashi kayan shi ne a cikin ledar akwae ma saura a gida bata iya ɗaukkowa sai dai in zata koma sai su je tare ya daukko, da mamaki ya buɗe ledar ya shiga duba kayan kafin da tsananin mamaki ya ɗago ya kalleta yace ya zata yi wannan hidiman haka sosae ta yamutsa mashi fuska tare da yi mashi wani kallo tace What are Friends for abunta nashi ne so bata son yana yi mata irin haka kawai inta bashi abu ya amsa shikenan, yana murmushi yace to tayi haƙuri yayi mata godiya tare da faɗin Allah shima ya bashi ikon kyautata mata haka tace bata buƙata iya haka da ya saki jiki da ita ya wadatar, ruƙe da tray mai ɗauke da kayan abinci Gwaggo ta dawo ta daura akan table ta matsar dashi gaban Farhar tana niyyar buɗe Warmer ɗin Farhar tace wllh ta ƙoshi yanzu taci abinci Gwaggon tace ai abun marmari ne taci ko ba yawa tunda ita baƙuwar su ce, Waina ce da miya taji alaiyahu da nama sai ƙamshi take Gwaggo ta kalleta tana murmushi tace ta dai iya cin waina ko tay yar dariya tace eh ana masu shi, bada yawa tasa ta zuba mata ba ta nufi Fridge ta ɗaukko mata ruwa da lemu ta kawo mata, bayan ta koma ta zauna Kamalu ya taso da kayan ya dawo wurin Gwaggo ya nuna mata yace ita ta kawo mashi tace ma akwae saura zasu je ya ɗaukko, duba kayan gwaggo ta shiga yi kafin ta ɗago da mamaki ta kalli Farha dake cin waina a nutse tace harda hidima haka banda wadda akai ai da ta bassu kada ɗawainiyar tayi yawa idonta a ƙasa tana ɗan murmushi tace mata a'a ba komai, godiya Gwaggon tayi mata da Addu'ar Allah ya saka da alkhairi, bayan ta gama ci harda ɗaukar tray ɗin zata fitar da sauri Kamalu ya miƙe ya kar6a yaje ya kai Kitchen bayan ya dawo tashi Gwaggo tayi ta fita, tambayoyi ta shiga yi mashi kan karatun shi yana bata amsa suna haka aka shigo siyan abu sai lokacin ya tuna da ya baro shago a buɗe yace mata zai koma shago zata zauna anan tace a'a bari su fita tare, bayan sun fito Kamalun yayi ma Gwaggo magana ta leƙo sukai sallama sannan suka fito shi ya shiga cikin shagon ita kuma ta tsaya daga gaba tana kallon yadda yake sallamar yaron da yazo siyayyar tana ta murmushi, bayan ya sallami yaron ya tafi tace mashi gaskiya irin wannan business ɗin bai dace dashi ba kamata yay ace a Haɗaɗɗan Office yake A.c na hura shi har saida yayi dariyar da haƙoran shi suka fito yace shi ina zai samu irin wannan aikin abunda ma duka yanzu ya fara karatun yace ai gara ma wannan sana'ar a cikin shago yake kuma akwae fanka a garinsu kafin yazo nan rake yake saidawa akan table wani lokacin cikin rana ma ta ɗan buɗa ido alamar mamaki, ganin tana ta tsayuwa yace mata ko zata shigo tace a'a bari ta wuce yaushe zai zo amsar sauran kayan yace ko in anyi Magrib daga masallaci sai ya shigo tace ok tare da ce mashi Bye, tana niyyar tafiya ya tsaidata ya miƙo mata ledar Sweet ɗin ta ɗan girgiza mashi kai alamar a'a ya ɗan mariraice mata fuska yace please wannan ce kyauta ta farko daya ta6a mata duk da ba wata mai yawa bace ta amsa zai ji daɗi in kuma bata son irin shi sai ya canza mata wani, murmushi tayi tace ba kowane Sweet take sha bane yace ok ta faɗi mashi wadda take sha sai ya kira Uncle ɗinshi tunda yana kasuwa ya taho mata da ita tace No ba sai yayi haka ba tunda wannan ya bata zata sha ta miƙa mashi hannu ya bata tayi mashi godiya kafin ta ɗaga farin hannunta fatt tana mashi bye bye shima yayi mata ta tafi ya leƙo kai yana kallonta itama tana yi tana waiwayen shi tana mashi murmushi har saida ta kusa gida sannan ya maida kan shi, sai gab da Magrib Amadu ya dawo lokacin daya ga kayan da Farha ta kawo ma Kamalun shima ya jinjina abun har yana faɗin Allah yasa dai kar yazama wata matsala Gwaggo tace Amin, bayan sun gama sallar Magrib Kamalu yace mashi zai je ya amso sauran kayan kamar yadda yace mata Amadun ya tafi shi kuma ya wuce part ɗin Hajiya, a parlor ya iske Farhar tana kallo da yake ba salla take yi ba Hajiya kuma na bedroom ɗinta, sosae ta nuna jin daɗin zuwan nashi ya zauna nan suka shiga yin hira, har aka kira sallar isha suna zaune tace mashi yaje yayi salla in ya dawo sai ta ɗaukko mashi yace to, koda aka gama yin sallar ya dawo hirar suka cigaba da yi har Hajiya ta fito ta iske su suka gaisa dashi cikin fara'a ta tambayi ya karatunshi yana dai maida hankali ko yace mata sosae, ita kanta Hajiya saida ta ɗan yi mamakin ganin yadda suka saba da juna ƙarshe saida Farhar ta matsa mashi suka ci abinci tare bayan sun gama yace mata zai tafi harda ce mashi ai gobe ba School ko yace ya baro Uncle ɗin shi yana jiranshi ne sannan taje ta ɗaukko mashi tace ma Hajiya zata rakashi ta dawo tace to, tare suka kama ledar kayan suna tafe suna hira har suka iso bakin shagon yayi mata godiya ta gaishe da Amadu ya amsa mata ya ɗan saki fuska kafin tayi ma Kamalun saida safe ta tafi yana shiga cikin shagon Amadu ya wurga mashi harara tun ma kafin yayi magana yana murmushi ya bashi haƙuri yace itace ta ruƙe shi da hira, a ɗan fusace Amadun yace shi kuma da yake tsoronta yake ji da bazai ce mata zai tafi ba Kamalun nata ɗan murmushi ya ƙara bashi haƙuri yace bazai sake ba, Bayan Farha ta koma saida Hajiya ta tambayeta yadda akai tasan Kamalu har suka saba haka tace mata a Abuja wurin bikin Yaya Nameer suka san juna itama Hajiyar bata kawo komai ba a ranta tayi tunanin jininsu ne ya haɗu don shima Kamal ɗin kamar Fatuu yake yana da farin jini dama kuma yawanci Mutum mai kyau haka yake da shiga rai, bayan sun tashi daga shagon sun shiga gidane Kamalu ya haɗa duka kayan yace ma Amadun ya ɗauki wanda yake so da sauri yace mashi a'a yayi amfani da kayanshi, marairaice mashi yayi yana mashi magiya da ƙyar ya ɗauki wasu jeans da t-shirt yace sun isa ya gode duk da haka saida ya ƙara mashi da agogo da takalma, Washe gari Gwaggo ta kira Fatuu anan take sanar mata game da abubuwan da Farha ta kawo ma Kamalu sosae tayi mamaki tace banda kuɗin da akace ta turo mashi ya canza waya Gwaggon tace mata wllh kuwa kaya sosae ta kawo mashi Fatun tace ita gaskiya abubuwan da take mashi basu kwanta mata a rai ba tunda ansan halinta duk da ta canza kada daga baya abu yazo ya zama wata matsala ko tace zata yi mashi gori, Gwaggo na murmushi tace to ai dai ba roƙonta akayi ba ita taji ta gani duk da dai tana kyautata mata zaton da zuciya ɗaya take mashi Fatun tace to Allah yasa amma dai duk da haka a daina amsar mata kaya zata kira Kamalun ma tayi mashi magana Gwaggon tace gashi can ɗaki bari ta bashi tace to, bayan sun gaisa ta tambayi ya karatu ya amsa mata tambayar shi tayi wai mike tsakaninshi da Farha ne yace mata shi wllh ba komai daga dai abotar data ce mashi tana son suyi shikenan Fatuu tace to ita bata son yana amsar mata abubuwa ko yace zai tambayeta wani abu don zai iya zama matsala duk abunda yake so ita ya kirata in sha Allahu indai baifi ƙarfinta ba zata mashi yace mata to tare da yi mata godiya daga baya sukai sallama.