← Book details Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 90 OF 211

Sashe 90

Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Wai Fauziyya ko Zarah ta zo....." Kaman daga sama suka ji muryar Aunty Mareeya tana fad'in hakan, had'a idon da sukai da Fatuu data juyo tana kallon ta yasa bata k'arasa Maganar ba ta d'an waro ido alamar mamaki, k'arasa shigowa tay ta nufi bakin gado ta zauna idon ta akan Fatuu dake ta mata murmushi tace "yar gidana yaushe kika zo ban sani ba sai yanzu da Abban su Hanif ya dawo daga Masallaci yake man Maganar Motar da aka parker a waje saitin gidan nan naje na lek'o ta ina gani nace wannan ai Motar Zarah ce?" Gaishe da ita ta fara yi kafin tace mata tun d'azu tazo Fauzy tace mata tana bacci, kallon Fauzy dake ta cin Alkubus tay ta d'an harareta "maimakon kije ki fad'i man tazo" yar dariya tay tace to tana tare da mijinta ya zata je mata d'aki, "to uban me ake a d'akin da bazaki je ba ko yau kika fara zuwa" dariya suka saki harda Fatuu Fauzyn tace "uhmm nidai ai ban ce wani abu ba ko nayi tunanin ko kuna bacci ne kuma da har zan kira ki ita tace tunda ba tafiya zata yi ba in k'yale ki gata nan ki tambaye ta" tsoki ta buga still dariya Fauzy ke yi tace mata ga Alkubus nan Zarah ta kawo masu ta jinjina kai, maido idon ta kan Fatuu tay tayi mata godiya ta tambayi mijin nata ya dawo lafiya dasu Hajiya da gwaggo duk ta amsa mata, mik'ewa tayi ta cire hijab d'in tana cikin ninketa Aunty dake kallonta tace "yar gidana abun Alheri dai sai k'ara girma yake ma sha Allah, amman ya fara motsi kuwa?" tana dariya tace mata a'a ai ba fa wani girma can yayi ba ta fad'i mata watannin shi Aunty tace to amman dai gaskiya in haka ne zata yi girman ciki yadda cikin farko bai cika wani girma ba k'ilan dai da gaske yan biyun ne, ita dai murmushi kawae take yi, bayan ta aje Hijab d'in ta nufi gadon ta haye idon ta akan Aunty Mareeya tace "kiyi hak'uri jiya kinata jira na naga dare yayi shine na yanke bari sai yau in zo in fad'i maki komai baki da baki" da sauri tace ai ba komai dama itama bata san ran a jiya zata kira ta fad'i mata yadda sukai ba ba kamar data ce bai gari,

"Na tambaye shi duk abunda kika ce harma da wanda baki ce ba wato aikin shi" a k'agauce Aunty tace aikuwa fa ba'a san aikin shi bama wllh to yanzu ya sukai da shi, tiryan tiryan ta shiga yi mata bayanin duk yadda sukai da Haisam gaba d'aya sun maida hankalin su akanta harda Fauzyn tayi cak tana kallon bakin Fatun, tun kafin ta rufe baki Aunty ta shiga washe baki ta fara fad'in "Alhamdulillah, Alhamdulillah dama ni wllh ban ji ina zargin shi da komai ba kawai a rai na ina jin sakayya ce ubangiji zai mata da shi" Murmushi Fauzy kawai ke saki bata ce komai ba Aunty ta kalle ta tace "to kin ji dai ai yanzu sai ki kwantar da hankalin ki tunda ga bayani nan daga bakin mai dil gashi nan kuma da kan shi yace abun kiyi Alfahari ne ma ita matsalar tashi da aka ce kada ki d'auketa a babbar matsala ke zaki zage damtse ki hana shi hakan sannan ki kore mayun kudajen matan da ke bibiyar shi wannan duk mai yuwuwa ne ba kamar in kika shige daga ciki in sha Allah za muyi k'ok'ari ya dawo bai sha'awar ta6a kowacce mace in ba ke ba" murmushi kawai Fauzy ke saki haka ma Aunty Mareeyar sai faman washe baki take gaba d'aya dad'i ya cikata farinciki ne bayyane akan fuskar ta can tace ma Fatuu to miye aikin shi data tambaya bata fad'i masu ba,
bayanin aikin nashi ta shiga yi tun kafin ta gama yanayin fuskar Aunty ya fara sauyawa lokacin data gama fad'i masu gaba d'ayan su zaro ido sukai da alamun razana Aunty tace wai bata gane su ke yin rocket ba wai wadda ta sani ko kuwa, Fatuu na dariya tace mata eh, aikuwa gaba d'aya ta k'arasa zaro idanun ta kai duka hannuwanta ta dafe k'irji tace "na shiga ukku ni Mariyatu, Zarah wannan abun fa ba shine ake ce ma makamin k'are dangi ba yanzu ace su suke yin shi" sosae ta rud'e don yanayin fuskar ta ya bayyana still dariya Fatuu ke yi tace mata itama wllh farko saida hankalinta ya tashi amman ai yace shi yafi k'arfi ta bangaren had'a jirgi kuma ba kowanne rocket ne missile ba, yarfa hannu Aunty tay ta d'an cize baki tace "ki gane Zarah irin abun nan ko wanda yasan inda ake saida su dole kaji tsoron shi balle kuma wanda ya san inda ake k'era su yake kuma aiki a wurin, haba, haba kice dole ma Sameer yak'i dariya suda ke k'era wannan mugun abun tashin hankalin ta ya zai rink'a ma sakin fuska, ai wllh Fauziyya ko baki son shi yanzu yazama dole ma ne ki amince mashi in dai ba so kike ya k'arar da kaf dangin mu ba koma ya tashi garin Funtua gaba d'aya",

Fatuu mi zatayi in ba dariya ba harda dafe ciki da 6ungulawa saman gadon don gaba d'aya Aunty fa ta rud'e, ita kanta Fauzy duk da ta d'an razana amman sosae Aunty ta bata dariya, bayan Fatuu ta tsagaita da yin dariyar ta taso zaune nan ta shiga kwantar ma Aunty da hankali tana nuna mata shifa ba'a ce dashi ake k'era wannan ba kuma koda dashi d'in shidai ai sana'a ce yake kuma misali don suna k'erawa hakan ba yana nufin sun iya amfani da shi ba tunda hakan ma wani ilimin ne, fuska a kwa6e Aunty ke kallonta hakan ya k'ara ba Fatuu dariya, da k'yar dai aka samu Aunty ta d'an kwantar da hankalinta Fauzy ta zuba mata alkubus ta fara ci duk in Fatuu ta kalleta sai ta saki dariya ita kuma saidai ta d'an girgiza kai ta tura Alkubus a baki, itama ta yaba alkubus d'in tana cikin ci tace ma Fauzy sai ta tsaya ta koya Abinci sosae in ba haka ba taje ta kwa6a mashi ya tarwatsa ta da rocket ita ta sani gaba d'aya suka kwashe da dariya Fauzy na fad'in ai fa sun bani da zancen rocket, bayan ta gama ci Fauzy tace yanzu sai ta kira Baban ta sanar mashi ko tana harararta tace ta sanar mashi da uban mi da ba tace bata son shi ba, Fauzy na murmushi tace to yanzu tana son shi Saboda kar a tashi Funtua suka saka dariya harda ita Auntyn,

Kiran Mahaifin nasu ta shiga yi tana fara ringing ya d'aga cikin girmamawa ta gaishe dashi tare da tambayar yadda suke duk ya amsa mata, a nutse ta shiga yi mashi bayanin sun yi magana da Fauziyya kuma ta nuna tana son shi har ma sun yi bincike akan shi, nan ta kwashe komai ta sanar mashi amman banda zancen ta6a mata da aka ce yana yi, nannauyar ajiyar zuciya mahaifin nasu ya saki yay d'an jimm har saida Aunty ta tambayi Lafiya da yanayin damuwa a muryar shi yace to ai abun ne ba K'aramin Al'amari bane d'an Governor fa, Aunty tace "Don Allah kar ka wani tashi hankalin ka Baba ai Allah baya daurawa bawa abunda bazai iya ba, kuma ai shi yaron yasan ita wacece tunda ta sanar dashi har ma aiki daka ajiye da noma da kake yi yanzu duk ta sanar mashi tunda yaji ya gani to kaga ai ba abun damuwa bane kuma dama ai ance wani hanin ga Allah baiwa ne k'ilan sakayyar abunda Mujaheed yayi mata ne" jinjina kai yay ya furta hakane kafin yace yanzu ita ya take ganin za'ayi don shi wllh gaba d'aya kan shi ya d'aure ganin abun yake ma kamar wani al'mara, dariya tayi tace ba al'mara bane da gaske ne ta kuma cewa "abunda nike gani Baba shine ka kira su kamar yadda kace masu sai kace cikin weekend mai zuwa in yayi masu sai su zo" shiru yay kafin yace mata hakan bai yi kusa ba kuwa tace a'a ai tunda neman Aure ne za'a zo ba wai bikin ba gara kawai a basu dama yanzu zata yi ma Yaya Mubarak magana duk abunda ya dace za'a yi in sha Allahu itama in dai zasu zo lokacin tana tunanin zata zo, a sanyaye yace Shikenan zai kira su d'in duk kuma yadda sukai zai kira ya sanar mata tace to, fatan Alkhairi yayi ya saka masu Albarka daga haka sukai sallama, suna gamawa ta k'ara ma wayar kud'i ta bank ta kira Mahaifiyar su, kamar yadda sukai da Baban nasu haka itama tayi mata bayani, sosae itama jikinta yay sanyi daga yanayin muryarta tace mata yanzu ita tana ganin hakan mai yuwuwa ne Aunty tace in sha Allahu su yi Addu'a kawai tace Shikenan zasu yi, bayan sun gama wayar kallon Fauzy tay da tay zuru ita kanta na Baban nasu ganin abun take kamar al'mara d'in tana murmushi tace mata to ta kira Baban nasu Fauzyn ta d'an ta6e baki tace umm Fatuu ta kai hannu ta dafata da murmushi tace wannan ba abun damuwa bane abun farinciki ne k'awata tay yar dariya,
Chapter 90 · 0% Book details