Sashe 76
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Katseta tay "ajiya ya baki su ne, ko rok'on shi kikai, koma rok'on shi kikai sun halatta a ci su tunda ya baki" Fauzy tace "a'a Aunty kar fa a tada lissafi daga baya" tsoki ta buga tace "aita tadawar da yake ance maki shi K'aramin mutum ne, su irin su da sun ba mutum abu suke mantawa, ke in ma yace a biya shin ai muna da hali sai mu saida gonar gado" ta k'arasa tana kyalkyatar dariya itama Fauzyn dariyar take don ta gane dalilin da yasa ta sako zancen gona Saboda labarin data bata ne na Maganar gonar data yi mashi, cikin dariya Fauzy tace "Aunty ta ina ta zama gonar gado ga mai ita a raye, tace "ai shima gada yayi a wurin kakan mu ko kinga ai ta gadon ce kenan" dariya suka saka gaba d'aya daga baya sukai sallama kafin ta kashe ta tambayi to tayi mashi godiya ma kuwa ta sanar da ita yak'i ya d'auka tace ta kyale shi to sai wani lokacin in sun k'ara yin magana sai tayi mashi.
A ranar da daddare misalin k'arfe goma da wasu mintuna Senator yazo kawo ma Hajiya da Fatuu Fura kamar ko yaushe, tana zaune a parlor ya shigo bayan ya zauna sun gaisa da fara'a ya tambayi yau ina yar taya ta hirar ya ganta ita kad'ai ko har tayi bacci, d'an ta6e baki Hajiya tay tace tana d'aki yau fushi take shiyasa ta k'unk'ume a cikin d'aki, cike da kulawa ya tambayi abunda yasa take fushin Hajiyar ta fad'i mashi zancen karatun ta ne so take su koma taci gaba da zuwa shine tace mata ba yanzu ba tunda ba yadda za'ai tayi tafiya mai tsawo a yanzu, d'an murmushi yay yace "ina ruwan Daughter lafiya ai tana gaba da komai, na fahimce ta tana da babbar hujja inaga abunda za'ai za'a tuntu6i Makarantar tasu in za'a iya yi man Alfarma sai taci gaba da yin karatun ta online zuwa a k'ara d'an lokaci ta k'ara samun lafiyar da zata iya yin tafiya ba tare da tunanin wata matsala ba" kai Hajiya ta jinjina mashi tace in zai yuwu to ayi hakan don ba K'aramin son karatun take ba in ba cigaba taga tayi ba ta dingi damuwa kenan kuma hakan ma na iya haddasa mata wata matsalar don ba'a son mai ciki da damuwa, kai ya jinjina mata tare da mik'ewa yace bari ya gan ta ya k'ara kwantar mata da hankali, a bakin Bedroom d'in ya tsaya yayi sallama, sau biyu yayi shiru ba'a amsa ba hakan yasa shi shiga, hango ta yay kwance ta lullube rabin jikinta da duvet nan ya gane tayi bacci, juyowa yay ya dawo cikin parlon bayan ya zauna ya sanar ma Hajiyar bacci take yace in ta tashi sai a k'ara kwantar mata da hankali in sha Allah yadda yace d'in yana tunanin zai yuwu tace to, yar hira suka ta6a kafin yay mata saida safe ya tafi.
*Bayan Wata Biyu*
A kwana a tashi ba wuya a wurin ubangiji gashi cikin Fatuu har yayi wata ukku lokacin watan Haisam d'aya da rabi da tafiya, Sosae take samun kulawa a wurin dukkan Mutanen gidan ko tari tayi sai an tambaye ta lafiya, haka ta bangaren Abinci kullum ne da safe zuwa dare sai an tambayi abunda take so ta ci wani lokacin ta fad'i wani lokacin kuma tace zata ci abunda aka yi, sosae take hutawa don ko tsinke wannan bata kaudawa hakan yasa ta kara yin k'iba kumatunta sun k'aru ga wani irin fari data k'ara kamar Madara dama ita ba ja bace fara ce ta yi wani fayau ga fatarta tayi wani irin lukui lukui, ta bangaren jikinta ma hips d'inta sun k'ara saidai boobs d'inta sunfi k'aruwa sunyi fam dasu ga cikin nata har ya fito ana ganin shi ba kamar in tasa kaya da suka kamata sosae ake ganin shi, suna yin waya da Vedio call da Haisam akai akai don kullum ne sai sun yi wani lokacin wuni suke suna wayar in suna Vedio call har cikin take bud'e mashi ya gani haka Fanan ma sosae tayi murna ganin cikin ya fara fitowa tai ta kafa mata sharudd'a kan cikin ita kuma taita dariya, bangaren su gwaggo ma kullum sai tayi waya ko Vedio call da su gaba d'aya Mino ta k'osa ta dawo kullum sukai waya sai ta tambayi yaushe zata dawo, haka bangaren karatunta kamar yadda Senator yace ta Online d'in yanzu take yi har su Assignment da test duk ana mata hakan yasa ta kwantar da hankalinta, bangaren Fauzy itama tana kiran Sameer ta gaishe da shi saidai ba akai akai ba gudun kar ta zaqe saidai suna yawan yin magana ta chat wani lokacin shike fara mata magana ya tambayi yadda take da karatunta wani lokacin kuma ita ke mashi magana ta gaishe da shi sai dae tun Vedio call d'in da sukai rannan basu k'ara yi ba, Aunty Mareeya duk sukai waya ko ta koma weekend sai ta tambayi ko yace yana son ta tace mata a'a ita basu wannan Maganar da shi ba sai tay dariya tace ai sannu bata hana zuwa.
Ranar lahadi lokacin cikin Fatuu ya k'ara sati guda suna zaune da daddare a parlor suna shan furar su da Dad yasa aka kawo masu don shi yayi tafiya tare da Mr. President basu K'asar dama shi na hannun daman shi ne ana hasashen ma shi ne d'an takarar shi da zai tsaida a Za6e mai zuwa, suna cikin shan furar Hajiya tace "Fateema ina ga fa barin ki zan yi anan don hankali na yayi gida na gaji da zaman Abujar nan dama Saboda ke ne in ba don haka ba ni ina zan zauna haka" idanu waje Fatuu data dakata da shan furar take kallonta har ta gama, a marairaice ta fara rok'onta kan to su tafi tare mana Hajiyar tace mata a'a tunda dai tana karatun ta lafiya lou ta zauna ta k'ara lokaci, kwa6e fuska tay nan da nan idanun ta sukai rau rau sun ciko da k'walla, tsam ta mik'e ta matsa gaban Hajiyar ta duk'a a gabanta ta fara mata magiyar su tafi tare don Allah wllh ita lafiya lau take jin ta ba abunda ke damunta in sha Allah lafiya lau zasu je, Hajiya dake kallonta tace ta tashi bata ga halin da take ciki bane zata duk'a haka, k'wallan ne suka fara zubo mata tace to don Allah zasu tafi taren, ce mata tay ta tashi ta zauna ta yunk'ura ta mik'e, bayan ta zauna cigaba da yin k'wallan tayi, ajiyar zuciya Hajiya tayi tace ita ba k'in tafiya da ita take ba kawai matsala take gudu da sauri Fatun tace "in sha Allahu Hajiya ba abunda zai faru tunda ban jin wani ciwo kuma zaki iya sawa ma Aunty ta duba ni" shiru tay tana kallonta ta cikin glasses d'inta fuskarta da d'an murmushi, tasan in ta tafi ta barta bazata kwantar da hankalin ta ba zatai ta damuwa ne dama hada k'arin hakan yasa ta zauna, ajiyar zuciya ta sauke tace Shikenan zata yi ma Dad magana kan hakan in ya amince cikin satin da za'a shiga sai su tafi dama shima jibi zai dawo, rok'onta ta shiga yi kan ai ita zata sa shi ya amincen don Allah Hajiyar nata dariya tana fad'in wai ba nan da Katsinar duk d'aya bane Fatun tace mata eh amman tayi missing d'in su gwaggo ne.
Ranar talata da daddare Senator ya dawo sai washe gari da safe wurin k'arfe tara ya samu shigowa gaisawa da Hajiya ya shirya cikin galleliyar shadda light blue babbar riga da yan ciki sai hula da Agogo da takalma mahad'in kayan sai baza uban k'amshi yake, lokacin tana cikin Bedroom ya shigo bayan yayi sallama an bashi izinin shigowa, tana zaune a bakin gado jikinta sanye da cotton d'in doguwar rigar bacci Fatuu kuma na kwance itama jikinta sanye da kayan bacci riga da wando sai hula bata dad'e da gama yin Breakfast ba ta dawo ta kwanta, yana niyyar zama a kan Carpet Hajiya tace ya zauna a bakin gadon mana, tun bayan da ya shigo Fatuu ta tashi zaune idonta a kanshi tana d'an murmushi bayan ya zauna ta gaishe dashi ya amsa mata da fara'a tay mashi an dawo lpy ya amsa shima ya tambayi jikinta tace mashi Alhamdulillah, k'ok'arin sauka ta fara yi daga gadon yace mata tayi kwanciyarta ba dad'ewa zai yi ba, duk da haka saida ta sauka ta koma kan Carpet ta zauna, gaisawa sukai da Hajiya tayi mashi an dawo lafiya, bayan sun gama gaisawar ne ya fara yi mata maganar tafiyarta da suka fara ta waya tun yana can, tambayarta yay game da Fatuu yace in tana ganin ba matsala sai su tafi taren cike da zolaya tace "ai ina ganin ta zauna kawai in ta samu kaman wata biyar sai ta koma" ta k'arasa Maganar had'i da satar kallon Fatuu, tana jin haka ta yamutsa fuska idanunta sukai rau rau, ganin Hajiya na kallon Fatun tana yar dariya yasa Dad d'in shima kai idon shi kanta kawai sai ganin k'walla sukai sun zubo mata sharr da sauri ta sunkuyar da kanta k'asa, d'an murmushi Dad yay calmly yace "Daughter ko baki jin dad'in zama da mu ne" da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a ba tare data d'ago ba,
"To kukan na miye?" Ya tambaya da fara'a, shiru tay bata ce komai ba ya sake cewa "Ko kina kewar yan uwanki ne?" Da sauri ta jinjina mashi kai,
"Ok, ki daina kuka kin ji za'a duba in dai hakan bazai ja wata matsala ba sai ku tafi tare" kai ta d'aga mashi yace to ta d'ago yaga in ta daina yin kukan, saida ta goggoge fuskar da hannu sannan ta d'ago yana murmushi yace to yaga itama tayi ta d'an yi murmushin Hajiya dake kallonta ma ta yi murmushi, daga baya yayi sallama da Hajiyar tayi mashi Allah ya huta gajiya.
A ranar da daddare misalin k'arfe goma da wasu mintuna Senator yazo kawo ma Hajiya da Fatuu Fura kamar ko yaushe, tana zaune a parlor ya shigo bayan ya zauna sun gaisa da fara'a ya tambayi yau ina yar taya ta hirar ya ganta ita kad'ai ko har tayi bacci, d'an ta6e baki Hajiya tay tace tana d'aki yau fushi take shiyasa ta k'unk'ume a cikin d'aki, cike da kulawa ya tambayi abunda yasa take fushin Hajiyar ta fad'i mashi zancen karatun ta ne so take su koma taci gaba da zuwa shine tace mata ba yanzu ba tunda ba yadda za'ai tayi tafiya mai tsawo a yanzu, d'an murmushi yay yace "ina ruwan Daughter lafiya ai tana gaba da komai, na fahimce ta tana da babbar hujja inaga abunda za'ai za'a tuntu6i Makarantar tasu in za'a iya yi man Alfarma sai taci gaba da yin karatun ta online zuwa a k'ara d'an lokaci ta k'ara samun lafiyar da zata iya yin tafiya ba tare da tunanin wata matsala ba" kai Hajiya ta jinjina mashi tace in zai yuwu to ayi hakan don ba K'aramin son karatun take ba in ba cigaba taga tayi ba ta dingi damuwa kenan kuma hakan ma na iya haddasa mata wata matsalar don ba'a son mai ciki da damuwa, kai ya jinjina mata tare da mik'ewa yace bari ya gan ta ya k'ara kwantar mata da hankali, a bakin Bedroom d'in ya tsaya yayi sallama, sau biyu yayi shiru ba'a amsa ba hakan yasa shi shiga, hango ta yay kwance ta lullube rabin jikinta da duvet nan ya gane tayi bacci, juyowa yay ya dawo cikin parlon bayan ya zauna ya sanar ma Hajiyar bacci take yace in ta tashi sai a k'ara kwantar mata da hankali in sha Allah yadda yace d'in yana tunanin zai yuwu tace to, yar hira suka ta6a kafin yay mata saida safe ya tafi.
*Bayan Wata Biyu*
A kwana a tashi ba wuya a wurin ubangiji gashi cikin Fatuu har yayi wata ukku lokacin watan Haisam d'aya da rabi da tafiya, Sosae take samun kulawa a wurin dukkan Mutanen gidan ko tari tayi sai an tambaye ta lafiya, haka ta bangaren Abinci kullum ne da safe zuwa dare sai an tambayi abunda take so ta ci wani lokacin ta fad'i wani lokacin kuma tace zata ci abunda aka yi, sosae take hutawa don ko tsinke wannan bata kaudawa hakan yasa ta kara yin k'iba kumatunta sun k'aru ga wani irin fari data k'ara kamar Madara dama ita ba ja bace fara ce ta yi wani fayau ga fatarta tayi wani irin lukui lukui, ta bangaren jikinta ma hips d'inta sun k'ara saidai boobs d'inta sunfi k'aruwa sunyi fam dasu ga cikin nata har ya fito ana ganin shi ba kamar in tasa kaya da suka kamata sosae ake ganin shi, suna yin waya da Vedio call da Haisam akai akai don kullum ne sai sun yi wani lokacin wuni suke suna wayar in suna Vedio call har cikin take bud'e mashi ya gani haka Fanan ma sosae tayi murna ganin cikin ya fara fitowa tai ta kafa mata sharudd'a kan cikin ita kuma taita dariya, bangaren su gwaggo ma kullum sai tayi waya ko Vedio call da su gaba d'aya Mino ta k'osa ta dawo kullum sukai waya sai ta tambayi yaushe zata dawo, haka bangaren karatunta kamar yadda Senator yace ta Online d'in yanzu take yi har su Assignment da test duk ana mata hakan yasa ta kwantar da hankalinta, bangaren Fauzy itama tana kiran Sameer ta gaishe da shi saidai ba akai akai ba gudun kar ta zaqe saidai suna yawan yin magana ta chat wani lokacin shike fara mata magana ya tambayi yadda take da karatunta wani lokacin kuma ita ke mashi magana ta gaishe da shi sai dae tun Vedio call d'in da sukai rannan basu k'ara yi ba, Aunty Mareeya duk sukai waya ko ta koma weekend sai ta tambayi ko yace yana son ta tace mata a'a ita basu wannan Maganar da shi ba sai tay dariya tace ai sannu bata hana zuwa.
Ranar lahadi lokacin cikin Fatuu ya k'ara sati guda suna zaune da daddare a parlor suna shan furar su da Dad yasa aka kawo masu don shi yayi tafiya tare da Mr. President basu K'asar dama shi na hannun daman shi ne ana hasashen ma shi ne d'an takarar shi da zai tsaida a Za6e mai zuwa, suna cikin shan furar Hajiya tace "Fateema ina ga fa barin ki zan yi anan don hankali na yayi gida na gaji da zaman Abujar nan dama Saboda ke ne in ba don haka ba ni ina zan zauna haka" idanu waje Fatuu data dakata da shan furar take kallonta har ta gama, a marairaice ta fara rok'onta kan to su tafi tare mana Hajiyar tace mata a'a tunda dai tana karatun ta lafiya lou ta zauna ta k'ara lokaci, kwa6e fuska tay nan da nan idanun ta sukai rau rau sun ciko da k'walla, tsam ta mik'e ta matsa gaban Hajiyar ta duk'a a gabanta ta fara mata magiyar su tafi tare don Allah wllh ita lafiya lau take jin ta ba abunda ke damunta in sha Allah lafiya lau zasu je, Hajiya dake kallonta tace ta tashi bata ga halin da take ciki bane zata duk'a haka, k'wallan ne suka fara zubo mata tace to don Allah zasu tafi taren, ce mata tay ta tashi ta zauna ta yunk'ura ta mik'e, bayan ta zauna cigaba da yin k'wallan tayi, ajiyar zuciya Hajiya tayi tace ita ba k'in tafiya da ita take ba kawai matsala take gudu da sauri Fatun tace "in sha Allahu Hajiya ba abunda zai faru tunda ban jin wani ciwo kuma zaki iya sawa ma Aunty ta duba ni" shiru tay tana kallonta ta cikin glasses d'inta fuskarta da d'an murmushi, tasan in ta tafi ta barta bazata kwantar da hankalin ta ba zatai ta damuwa ne dama hada k'arin hakan yasa ta zauna, ajiyar zuciya ta sauke tace Shikenan zata yi ma Dad magana kan hakan in ya amince cikin satin da za'a shiga sai su tafi dama shima jibi zai dawo, rok'onta ta shiga yi kan ai ita zata sa shi ya amincen don Allah Hajiyar nata dariya tana fad'in wai ba nan da Katsinar duk d'aya bane Fatun tace mata eh amman tayi missing d'in su gwaggo ne.
Ranar talata da daddare Senator ya dawo sai washe gari da safe wurin k'arfe tara ya samu shigowa gaisawa da Hajiya ya shirya cikin galleliyar shadda light blue babbar riga da yan ciki sai hula da Agogo da takalma mahad'in kayan sai baza uban k'amshi yake, lokacin tana cikin Bedroom ya shigo bayan yayi sallama an bashi izinin shigowa, tana zaune a bakin gado jikinta sanye da cotton d'in doguwar rigar bacci Fatuu kuma na kwance itama jikinta sanye da kayan bacci riga da wando sai hula bata dad'e da gama yin Breakfast ba ta dawo ta kwanta, yana niyyar zama a kan Carpet Hajiya tace ya zauna a bakin gadon mana, tun bayan da ya shigo Fatuu ta tashi zaune idonta a kanshi tana d'an murmushi bayan ya zauna ta gaishe dashi ya amsa mata da fara'a tay mashi an dawo lpy ya amsa shima ya tambayi jikinta tace mashi Alhamdulillah, k'ok'arin sauka ta fara yi daga gadon yace mata tayi kwanciyarta ba dad'ewa zai yi ba, duk da haka saida ta sauka ta koma kan Carpet ta zauna, gaisawa sukai da Hajiya tayi mashi an dawo lafiya, bayan sun gama gaisawar ne ya fara yi mata maganar tafiyarta da suka fara ta waya tun yana can, tambayarta yay game da Fatuu yace in tana ganin ba matsala sai su tafi taren cike da zolaya tace "ai ina ganin ta zauna kawai in ta samu kaman wata biyar sai ta koma" ta k'arasa Maganar had'i da satar kallon Fatuu, tana jin haka ta yamutsa fuska idanunta sukai rau rau, ganin Hajiya na kallon Fatun tana yar dariya yasa Dad d'in shima kai idon shi kanta kawai sai ganin k'walla sukai sun zubo mata sharr da sauri ta sunkuyar da kanta k'asa, d'an murmushi Dad yay calmly yace "Daughter ko baki jin dad'in zama da mu ne" da sauri ta girgiza mashi kai alamar a'a ba tare data d'ago ba,
"To kukan na miye?" Ya tambaya da fara'a, shiru tay bata ce komai ba ya sake cewa "Ko kina kewar yan uwanki ne?" Da sauri ta jinjina mashi kai,
"Ok, ki daina kuka kin ji za'a duba in dai hakan bazai ja wata matsala ba sai ku tafi tare" kai ta d'aga mashi yace to ta d'ago yaga in ta daina yin kukan, saida ta goggoge fuskar da hannu sannan ta d'ago yana murmushi yace to yaga itama tayi ta d'an yi murmushin Hajiya dake kallonta ma ta yi murmushi, daga baya yayi sallama da Hajiyar tayi mashi Allah ya huta gajiya.