Sashe 63
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
mik'ewa tay tana d'an murmushi tace "ni zanje in taya murna don basu kad'ai abun Arzik'in ya shafa ba harda mu don haka ina mai baku shawara da ku kauda komai a ran ku kuyi farinciki hankali kwance ku dangwali Arziki, ke Yaya in kika kwantar da hankalin ki ma k'ilan Makka da kike ta mafarkin zuwa Masoyin ki Ardo da Ya'yan ki suka kasa kai ki duk da suna da halin hakan sai kiga ta sanadiyyar su kinje har ki k'ara ma sau ba adadi tunda kinfi kowa sanin halin iyalan Muhammadu basu da ruk'o in ba don haka ba da ko kallo a yanzu bazaki ishe su ba amman duk da tsangwama da tsanar da kike nuna masu hakan bai hana su jan ki a jiki ba wanda na tabbatar su wad'anda kike k'ok'arin ganin kin aikata shirka don ki jawo su a cikin Arzik'in ba lalle ko Habujar su bari ki rink'a zuwa wurin su ba balle har ta kai ga su biya maki Makka in ma ace burin naki ya cika kenan, in baki sani ba ki sani duk na kusa dake da kike ganin suna goya maki baya munafukan ki ne da sun samu dama zasu kaskantar da rayuwar ki kamar yadda kike masu" tana gama Maganar ta juya ta nufi k'opar fita, a razane Yaya ta bita da ido har ta fice haka Babar Altine ma, kallon juna sukai sun kasa cewa komai don abu ne da basu ta6a zato ba, sun d'an d'auki lokaci haka da k'yar innar Altine ta ja kafa ta matsa kusa da Yaya dake tsaye kamar an dasa ta, k'ok'arin k'arfafa mata gwuiwa ta shiga yi tana ce mata kada Maganganunta su dame ta ita tana tare da ita abunda za'ai kawae itama ai maganinta ta yadda bazata iya aikata abunda ta fad'an ba sai ayi yadda za'ai Auren ya koma kan d'aya daga cikin yaranta ita kuma ta mata alk'awarin duk abunda take so shi za'a rink'a yi in aka shigo cikin Arzik'in, bin ta da ido kawae Yayar tay daga yanayin fuskarta zaka fahimci ba k'aramar razana tay ba, ci gaba da k'arfafa mata gwuiwa tay can Yayar ta fara girgiza mata kai har saida gaban innar su Altinen ya fad'i,
matsawa Yaya tay ta zauna a bakin gado cikin mutuwar jiki tace mata akwae babbar matsala, dama bokan ta ya ta6a fad'a mata sai ta bi a hankali don a cikin gidan su akwae wadda zata kawo k'arshenta lokacin ta buk'aci sanin ko wacece yace bai samu gano kowacece ba amman tabbas sai tayi taka tsantsan don ba K'aramin tagayyara rayuwarta zata yi ba, a lokacin ta rok'e shi ya bata abunda zatai amfani dashi wurin yin maganin ta amman sai ya nuna bazai iya ba don a yadda ya gani ita bada asiri zata yak'e ta ba da ayar Allah ne, baki bud'e innar su Altine data durk'ushe a k'asa take sauraren ta, nannauyar ajiyar zuciya Yaya ta sauke ta hau jinjina kai tace "yanzu na gano k'arshe na da yace zata kawo wato shine in ta tona man Asiri aka kai ni gidan yari" sosae Yaya ta tsorata abun ka da mutumin kauye, nazarin Maganganun kishiyar tata ta shiga yi a cikin ranta tabbas tasan abunda ta fad'a kan iyalan Muhammadu gaskiya ne duk abubuwan da take masu basu nuna rashin d'a'a a gareta in akwae wadda zata ce tana mata rashin kunya to Fatuu ce ita kuma wannan ba ita kad'ai take mawa ba halinta ne haka kuma bayan ta girma yanzu duk ta bari, zuciyarta ce ta raya mata in tayi wasa to fa zata tashi a tutar babu ne, da sauri ta kalli innar su Altine tace mata su hak'ura kawai in ba haka ba zasu shiga matsala in dai suka aikata wani abu gara su goyi baya suma su ci Arzik'in ala bashshi in bikin yazo sai su tattaro sauran yaran da basu da Aure suzo dasu watak'il suma su dace, cike da amincewa innar su Altine ta jinjina mata kai don itama ta tsorata da Maganar da tace bokanta yayi don tasan muddin asirin Yaya ya tonu to itama kuwa bazata sha ba, da sauri Yaya ta yunk'ura ta mik'e tace mata ta taso suje su nuna suna farinciki kar ayi tunanin wani abu, da sauri ta mik'e buguzun buguzun suka nufi kopa,
Lokacin da Kishiyar Yaya ta shiga d'akin su Yadikkon bata isketa ba sai su Aysha kawai, da fara'a ta k'arasa wurin su ta tambaye su innar su suka ce mata ta fita taje ta dawo ta jinjina masu kai, a bakin gado ta zauna don ta jirata, bata jima sosae ba Yadikko ta dawo dama wurin gwaggo taje, a k'asa saman Carpet ta fara k'ok'arin zama ganin tana zaune a bakin gadon da sauri tace mata ya zata zauna a k'asa tazo ta zauna a bakin gadon mana Yadikkon na murmushi tace mata ai ba komai, gaisawa suka k'ara yi don sun gaisa da suka tashi, cikin nuna tsananin farinciki tace mata taji abun Alkhairin daya k'ara samun su a bakin innar su Altine taji dad'i sosae wllh, Addu'oi ta shiga yi Yadikkon sai murmushi take a cikin ran ta take amsawa Saboda nuna kunya ba kamar da Mino take y'a ta farko a wurinta, suna haka sai ga su Yaya sun turo k'opar kamar an jefo su gaba d'aya suka sauke idanun su cikin na kishiyar tata tana ganin su ta kauda fuskar ta, k'arasa shigowa ciki sukai ganin yadikkon zaune a k'asa yasa suma suka fara k'ok'arin zama a kan Carpet d'in, cikin girmamawa Yadikko tace masu don Allah su zauna a kan gado mana duk suka ce a'a bari dai suma su zauna a k'asan, gaisawa suka shiga yi sai faman washe baki suke kaman wad'anda akai ma Albishir da Aljanna su duk k'ok'arin da suke shine asan suna murna, bayan sun gama gaisawar ne suka shiga taya ta murna suna fad'in wllh sunyi farinciki jin abun Alkhairi da ya k'ara samun su, innar su Altine harda cewa ai ita d'azun tsabar farinciki ne ma yasa ta kasa cewa komai ta tashi da sauri ta nufi d'akin su don ta sanar ma dasu Yaya suma,
Yaya ma cikin washe baki take fad'in ita shiyasa bata ta6a k'alubalantar komawar su binni ba wllh Saboda tana ji a jikinta hakan zai zame masu Alkhairi ashe kuwa hakan ne aikuwa su Aysha ma sai a maida su can binnin suma kawai, jin hakan har saida kishiyar tata ta d'an yi guntun murmushi ta ta6e baki ita kanta Yaya da tayi maganar duk ta bi ta kama kanta har d'an d'aga kai tay ta kalli kishiyar tata ita dai Yadikko murmushi kawae take don gaba d'aya farinciki ya gama cikata, Mero ce ta fara tashi tana k'ara taya yadikko murna ta nufi k'opa ta bud'e ta fita, kallon juna Yaya da innar su Altine sukai duk sun yi kalar rashin gaskiya, mik'ewa Yaya tay tana washe baki tace ma Yadikko bari taje ta idasa kimtsa kaya jin haka yasa innar su Altine itama ta mik'e tace haka, bin su da ido yadikko tay har suka fita, lokacin da suka koma d'akin nasu Mero na zaune a bakin gado jakar kayanta a gabanta ko kallon su bata yi ba, wurin ta Yaya ta nufa ta tsaya daga gaban ta sai lokacin ta d'ago ta kalleta, cikin kwantar da murya Yaya tace "ina son ki sani Wallahi tallahi kwarankwasa gajimare ni bani na kashe Fatima Mahaifiyar Muhammadu ba, koda kika ji nace na muzguna mata har Allah ya amshi abun shi bawai nice na kasheta ba, nasan da zalunce ta tun bayan da Ard'o ya auro ta na fahimci ba K'aramin son ta yake ba na fara muzguna mata k'arshe na had'a mata da asirin daya sa Ard'on ya rink'a gudun ta duk aka tsaneta to bak'in cikin hakan ne ya haifar mata da ciwo har yay tsanani Saboda ba'a kulawa da ita k'arshe ta rasu, ita kuma Aisha Mahaifiyar inna wuro sau d'aya nayi yunkurin yi mata Asiri don in raba su Saboda tana yar binni tafi sauran matan Y'ayana komai amman sai boka yace man bazai iya ba Saboda tana da iskokai masu zafi bazasu bari Asiri yayi tasiri ba a kanta gara in rabu da ita don zasu iya maido shi kaina, to daga nan itama na rink'a nuna mata tsana har tazo ta kwanta ciwo akai tunanin na iskar ta ne ashe cuta ce a cikin cikinta amman ni wllh bani da sa hannu a cutar" idon Mero a kanta har ta gama sannan ta sauke ajiyar zuciya tace ai Mahaifiyar Muhammadu itace tay silar mutuwarta don haka alhakinta na akanta gashi ta rasu balle ta rok'e ta yafiyar abunda tayi mata, a k'arshe tace mata tana bata shawara ta tuba ta daina shirka don malamin su dake koya masu karatun Addini yace itace laifin da Allah bai yafewa in aka mutu ba'a tuba ba sannan kuma duk wanda ta zalinta tun wuri ta nemi yafiyar shi don Allah bai yafe hakkin wani a kan wani, cike da nadama Yaya tace to yanzu ya zatay da hakkin Fatima data mutu, shiru Mero tay can ta nisa tace to ita gaskiya bata sani ba amman zata tambayi malamin su kuma suma yakamata su rink'a zuwa karatun hakan zai sa su daina aikata wasu abubuwan, atare suka had'a baki wurin cewa to zasu rink'a zuwa da sun koma, a marairaice Yaya tace mata to don Allah zata rufa mata Asiri Meron tay d'an murmushi tace ai ita bata isa ta tona mata Asiri ba in Allah bai yarda ba in kuna yaso ko ba ta silar ta ba to sai asirin nata ya tonu, sosae jikin Yaya yay sanyi lakwas kamar an watsa ma kaza gishiri.
matsawa Yaya tay ta zauna a bakin gado cikin mutuwar jiki tace mata akwae babbar matsala, dama bokan ta ya ta6a fad'a mata sai ta bi a hankali don a cikin gidan su akwae wadda zata kawo k'arshenta lokacin ta buk'aci sanin ko wacece yace bai samu gano kowacece ba amman tabbas sai tayi taka tsantsan don ba K'aramin tagayyara rayuwarta zata yi ba, a lokacin ta rok'e shi ya bata abunda zatai amfani dashi wurin yin maganin ta amman sai ya nuna bazai iya ba don a yadda ya gani ita bada asiri zata yak'e ta ba da ayar Allah ne, baki bud'e innar su Altine data durk'ushe a k'asa take sauraren ta, nannauyar ajiyar zuciya Yaya ta sauke ta hau jinjina kai tace "yanzu na gano k'arshe na da yace zata kawo wato shine in ta tona man Asiri aka kai ni gidan yari" sosae Yaya ta tsorata abun ka da mutumin kauye, nazarin Maganganun kishiyar tata ta shiga yi a cikin ranta tabbas tasan abunda ta fad'a kan iyalan Muhammadu gaskiya ne duk abubuwan da take masu basu nuna rashin d'a'a a gareta in akwae wadda zata ce tana mata rashin kunya to Fatuu ce ita kuma wannan ba ita kad'ai take mawa ba halinta ne haka kuma bayan ta girma yanzu duk ta bari, zuciyarta ce ta raya mata in tayi wasa to fa zata tashi a tutar babu ne, da sauri ta kalli innar su Altine tace mata su hak'ura kawai in ba haka ba zasu shiga matsala in dai suka aikata wani abu gara su goyi baya suma su ci Arzik'in ala bashshi in bikin yazo sai su tattaro sauran yaran da basu da Aure suzo dasu watak'il suma su dace, cike da amincewa innar su Altine ta jinjina mata kai don itama ta tsorata da Maganar da tace bokanta yayi don tasan muddin asirin Yaya ya tonu to itama kuwa bazata sha ba, da sauri Yaya ta yunk'ura ta mik'e tace mata ta taso suje su nuna suna farinciki kar ayi tunanin wani abu, da sauri ta mik'e buguzun buguzun suka nufi kopa,
Lokacin da Kishiyar Yaya ta shiga d'akin su Yadikkon bata isketa ba sai su Aysha kawai, da fara'a ta k'arasa wurin su ta tambaye su innar su suka ce mata ta fita taje ta dawo ta jinjina masu kai, a bakin gado ta zauna don ta jirata, bata jima sosae ba Yadikko ta dawo dama wurin gwaggo taje, a k'asa saman Carpet ta fara k'ok'arin zama ganin tana zaune a bakin gadon da sauri tace mata ya zata zauna a k'asa tazo ta zauna a bakin gadon mana Yadikkon na murmushi tace mata ai ba komai, gaisawa suka k'ara yi don sun gaisa da suka tashi, cikin nuna tsananin farinciki tace mata taji abun Alkhairin daya k'ara samun su a bakin innar su Altine taji dad'i sosae wllh, Addu'oi ta shiga yi Yadikkon sai murmushi take a cikin ran ta take amsawa Saboda nuna kunya ba kamar da Mino take y'a ta farko a wurinta, suna haka sai ga su Yaya sun turo k'opar kamar an jefo su gaba d'aya suka sauke idanun su cikin na kishiyar tata tana ganin su ta kauda fuskar ta, k'arasa shigowa ciki sukai ganin yadikkon zaune a k'asa yasa suma suka fara k'ok'arin zama a kan Carpet d'in, cikin girmamawa Yadikko tace masu don Allah su zauna a kan gado mana duk suka ce a'a bari dai suma su zauna a k'asan, gaisawa suka shiga yi sai faman washe baki suke kaman wad'anda akai ma Albishir da Aljanna su duk k'ok'arin da suke shine asan suna murna, bayan sun gama gaisawar ne suka shiga taya ta murna suna fad'in wllh sunyi farinciki jin abun Alkhairi da ya k'ara samun su, innar su Altine harda cewa ai ita d'azun tsabar farinciki ne ma yasa ta kasa cewa komai ta tashi da sauri ta nufi d'akin su don ta sanar ma dasu Yaya suma,
Yaya ma cikin washe baki take fad'in ita shiyasa bata ta6a k'alubalantar komawar su binni ba wllh Saboda tana ji a jikinta hakan zai zame masu Alkhairi ashe kuwa hakan ne aikuwa su Aysha ma sai a maida su can binnin suma kawai, jin hakan har saida kishiyar tata ta d'an yi guntun murmushi ta ta6e baki ita kanta Yaya da tayi maganar duk ta bi ta kama kanta har d'an d'aga kai tay ta kalli kishiyar tata ita dai Yadikko murmushi kawae take don gaba d'aya farinciki ya gama cikata, Mero ce ta fara tashi tana k'ara taya yadikko murna ta nufi k'opa ta bud'e ta fita, kallon juna Yaya da innar su Altine sukai duk sun yi kalar rashin gaskiya, mik'ewa Yaya tay tana washe baki tace ma Yadikko bari taje ta idasa kimtsa kaya jin haka yasa innar su Altine itama ta mik'e tace haka, bin su da ido yadikko tay har suka fita, lokacin da suka koma d'akin nasu Mero na zaune a bakin gado jakar kayanta a gabanta ko kallon su bata yi ba, wurin ta Yaya ta nufa ta tsaya daga gaban ta sai lokacin ta d'ago ta kalleta, cikin kwantar da murya Yaya tace "ina son ki sani Wallahi tallahi kwarankwasa gajimare ni bani na kashe Fatima Mahaifiyar Muhammadu ba, koda kika ji nace na muzguna mata har Allah ya amshi abun shi bawai nice na kasheta ba, nasan da zalunce ta tun bayan da Ard'o ya auro ta na fahimci ba K'aramin son ta yake ba na fara muzguna mata k'arshe na had'a mata da asirin daya sa Ard'on ya rink'a gudun ta duk aka tsaneta to bak'in cikin hakan ne ya haifar mata da ciwo har yay tsanani Saboda ba'a kulawa da ita k'arshe ta rasu, ita kuma Aisha Mahaifiyar inna wuro sau d'aya nayi yunkurin yi mata Asiri don in raba su Saboda tana yar binni tafi sauran matan Y'ayana komai amman sai boka yace man bazai iya ba Saboda tana da iskokai masu zafi bazasu bari Asiri yayi tasiri ba a kanta gara in rabu da ita don zasu iya maido shi kaina, to daga nan itama na rink'a nuna mata tsana har tazo ta kwanta ciwo akai tunanin na iskar ta ne ashe cuta ce a cikin cikinta amman ni wllh bani da sa hannu a cutar" idon Mero a kanta har ta gama sannan ta sauke ajiyar zuciya tace ai Mahaifiyar Muhammadu itace tay silar mutuwarta don haka alhakinta na akanta gashi ta rasu balle ta rok'e ta yafiyar abunda tayi mata, a k'arshe tace mata tana bata shawara ta tuba ta daina shirka don malamin su dake koya masu karatun Addini yace itace laifin da Allah bai yafewa in aka mutu ba'a tuba ba sannan kuma duk wanda ta zalinta tun wuri ta nemi yafiyar shi don Allah bai yafe hakkin wani a kan wani, cike da nadama Yaya tace to yanzu ya zatay da hakkin Fatima data mutu, shiru Mero tay can ta nisa tace to ita gaskiya bata sani ba amman zata tambayi malamin su kuma suma yakamata su rink'a zuwa karatun hakan zai sa su daina aikata wasu abubuwan, atare suka had'a baki wurin cewa to zasu rink'a zuwa da sun koma, a marairaice Yaya tace mata to don Allah zata rufa mata Asiri Meron tay d'an murmushi tace ai ita bata isa ta tona mata Asiri ba in Allah bai yarda ba in kuna yaso ko ba ta silar ta ba to sai asirin nata ya tonu, sosae jikin Yaya yay sanyi lakwas kamar an watsa ma kaza gishiri.