Sashe 35
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Yanzu ace yace yana son ki zaki so shi?" tambayarta Fauzyn tay wa, Fatun tace "shi wanccan d'an uwan Ya Haisam d'in" zaro ido Fauzy tay ta kai hannu ta ruk'e ha6a tace "tabbb kema dai da wani bahagon tunani kike wllh, ke yanzu ko wani yace maki wanccan zai so ni zaki yarda mutumin da daga gani zai yi izza ba kad'an ba, ai irin wanccan mutumin wllh matar shi ta bani don kuwa ba k'aramar wahalar shi zata sha ba don daga gani baza'a iya mashi cikin sauki ba, irin su komai akai masu ba'ai masu gwaninta" Fatuu dake dariya tace kawae ta bata amsa in ya ce yana son ta misali da aure zata iya auren shi, shiru Fauzy tay kaman mai nazari can tace "kinga don Allah mu bar Maganar nan abunda baka samu aka ce had'a shi da baka so don haka bai man ba" dariya sosae Fatuu ke yi tana fad'in Allah don bai ce yana son ta bane amman tasan tabbas zata so shi don ta fahimci ya yi mata, murmushi kawae Fauzyn tay zuciyarta na suffanto mata shi a ranta ta raya wannan ta ina ma zai iya wani son ta mima zai yi da ita, daidai lokacin suka iso part d'in da suke suka shiga.
Bayan sun shiga d'akin Toilet Fatuu ta wuce tayo Alwalar sallar isha, bayan ta gama hira suka dasa wadda yawanci duk akan Walimar gobe ce saida suka kai tsakar dare sannan Fatuu ta tashi don tafiya Fauzy tace ta kwana anan kawae mana tace ai gadon bazai ishe su ba tunda akwae wuri can bari taje kawae suka yi sallama dasu Haulat Fauzy ta rakota har waje kafin suka yi sallama ta koma. Washe gari Juma'a ana tashi aka fara shirye shiryen Walima ba kama hannun yaro masu aikin girki tuni sun fara dama tun jiya aka fara aikin nama banda shanun da Baffan Fatuu ya bada harda raguna da kaji aka yayyanka, Misalin k'arfe sha d'aya lokacin duk an gama breakfast Laila tasa Fatuu taje tayi wanka, da kanta taje d'akin Hajiya da yake nan aka kai akwatunan lefenta ta d'aukko mata kayan da zata saka wanda babbar Super ce ta had'u ba k'arya anyi mata straight skirt da riga half gown tare da sark'a da yankunan gold harda yan hannu da su jaka da takalmi da mayafi mahad'in kayan, bayan ta saka kayan Laila ta yi mata yar light make up kafin anjima wadda zata yi mata Bridal makeup d'in ta zo, da kanta ta d'aura mata kallabi abun sai dae ace Tubarkallah, nan fa aka hau yi mata hotuna bayan sun gama Laila ta kamata ta nufi d'akin Mom d'in su da ita, a parlor suka isketa da wasu mutane cikin yan uwan su da suka zo bikin Mom d'in na ganinta ta hau yi mata murmushi tace a kawota gefenta, bayan ta zauna ta gaishe da ita da sauran mutanen ana ta fad'in Ma sha Allah Amarya, mik'ewa Mom tayi ta kamo hannun Fatuu itama ta mik'e suka shiga cikin Bedroom harda Laila, wurin Hajiya Zainab ta kai ta, itama da murmushi ta tarbeta Mom ta sata ta zauna a bakin gado itama ta zauna a d'ayan gefen, gaida Hajiya Zainab d'in tayi da fara'a ta amsa ta yaba gayun nata tare da Addu'ar fatan Alkhairi Laila na amsawa daga baya ta kama hannun Fatun tace suje wurin Hajiya ta mik'e suka nufi hanyar fita idanun su Mom akan su, bayan sun fita Hajiya Zainab tace yarinyar nada kyau Mom dake murmushi tace sosae, part d'in Hajiya suka wuce bayan sun fito, duk suna zaune a parlor suna ta hira harda gwaggo suka shigo Laila tayi sallama duk suka maido idon su kan su suna amsa sallamar, gaishe da Mutanen parlon tay duk suka amsa, gefen Hajiya ta kai Fatun ta zaunar da ita tana murmushi tace "ga kishiyar ki na kawo kiga adon ta" d'an murmushi Hajiya tay ta ta6e baki tana kallon Fatuu da itama kallon ta take tana murmushi sai cewa tay ina ta wani yi kyau haka kamar an bad'a mata k'asa a fuskar, gaba d'aya yan d'akin sukai dariya suna fad'in duk kyaun nan da tayi wannan dai kishi ne ba wani abu ba Gwaggo dae sai murmushi take farinciki fal ranta ganin yadda Autarta ta fito sai kace d'iyar manyan mutane, gaishe da Hajiyar tayi bayan ta amsa ta juya kan sauran mutane ta gaishe da su da fara'a duk suka amsa suka hau yin Addu'oi Laila dasu Hajiya na amsawa daga baya suka bar part d'in, baya suka wuce inda su Haulat suke, lokacin da suka shiga cikin parlon su Yadikko dasu Yaya duk suna zaune suna yin kallo, wurin su Laila ta nufa duk suka maido idon su kanta suna washe baki, zama tayi akan kujera Fatuu ma ta zauna a gefen ta suka hau gaishe da ita, da fara'a ta amsa Yadikko ce tace "wannan kaman Amarya" sai lokacin Laila ta gane ashe basu gane Fatun ba tana yar dariya tace itace ta kawo masu suga gayun ta gaba d'aya suka k'ara washe baki suna fad'in ai su basu ganeta ba Fatuu dai sai murmushi take ta gaida su,Yadikko ce ta daddage ta rangad'a gwad'a sai ga su Mino sun fito da gudu ta nufo ta ai koda taga Fatuu da gudu ta koma cikin d'akin tana fad'in azo aga Adda Fatuu Amarya tayi kaman sarauniya, nan duk suka firfito harda su Aunty Mareeya Fanan ma na a d'akin su tafi zama a wurin su duk da a d'akin Laila ta sauka, nan fa aka shiga yabon gayun aka hau yin hotuna da ita Fanan tace ai yakamata a kawo photographer Saboda ayi hard copy na tarihi Laila tace zai zo sai anjima sunyi Magana yace na iPhone d'in ma lafiya lou zai wanke su tace Ok, bayan sun gama hotunan Laila ta k'ara kamo hannunta ta fito da ita, part d'in Haisam ta wuce da ita suka shiga ta baya, knocking k'opar tayi aka bata izinin shigowa ta tura, su biyar ne a zaune, Haisam, Sameer, Salim, Abbas sai wani abokin su d'an nan Abujar Na'eem, da murmushi Laila ta nufi cikin parlon idanun su gaba d'aya akanta banda Sameer da yake sanye da headphones da alama ma bai san ta shigo ba, tunda suka shigo idon Haisam na akan Fatuu suna ta sakar ma juna murmushi, gaishe su Laila tayi tace ga Amaryar su nan ta kawo masu su ga gayunta na farko duk suka maido idon su akan Fatuu, kunya ce ta kamata da sauri ta sunnar da kanta k'asa ta gaishe dasu Abbas ya shiga tsokanar ta, mik'ewa Haisam yay jikin shi sanye da k'ananun kaya basu dad'e da gama yin Breakfast ba, inda suke tsaye ya nufo yana zuwa ya kai hannu ya kamo Fatun kawai sai ya rungumeta gaba d'aya Abbas da Na'eem suka sa sowa shi dai Saleem murmushi yake, abunda su Abbas ke yi ne ya jawo hankalin Sameer ya d'ago ya kalle su Abbas ya fara masu Video, gaba d'aya wata irin kunya ce ta kama Fatuu ji take kaman ta nutse k'asa, kokarin d'ago da kanta ya fara yi ta kafe kan tak'i yarda ya d'ago ta, d'ukar da kan shi yay can k'asan mak'oshi ya furta tayi kyau sosae murya can k'asa tace don Allah kunya take ji ya fita da ita ya furta Ok, d'agota yay tak'i yarda ta kalli side d'in da su Abbas suke yace ma Laila suje yana ruk'e da Fatun yayi mata side hug suka nufi hanyar fita ta cikin parlon Sameer dake kallon su ya d'an ta6e baki da yanayin d'an murmushi akan fuskar shi, suna fitowa wayar Laila ta fara yin ringing tace masu tana zuwa pls ta d'an yi gaba tana amsa wayar, maido Fatun yay jikinshi ya rungumeta ta yadda suna kallon fuskar juna sai yamutsa mashi fuska take tana fad'in ita kunya take ji don Allah, yana murmushi idanun shi a d'an lumshe yace to mi yay mata da zai zama abun kunya da ido tay mashi nuni da rungume tan da yayi, ce mata yay wannan ba wani abu bane yake ma yan'uwan shi ma balle ita matar shi, sai faman tura mashi baki da ya sha jambaki take gaba d'aya hakan da take ya fara turning d'in shi on, kallon ta kawae yake tana mashi shagwabar kar wani ya gan su don Allah, slowly ya duk'ar da kan shi saitin nata ya kai bakin shi kunnanta ya rad'a mata magana, d'agowa yay ya d'age mata gira tace "Yaushe?" a hankali ya furta "after isha" shiru ta d'an yi kaman mai nazarin wani abu taji yace ko bata so da sauri ta girgiza mashi kai, Laila ce ta dawo wurin su tana murmushi da sauri Fatuu ta juyar da fuskar ta, ce ma Haisam d'in tayi ko ta barta a nan ne ba tare daya ce komai ba ya saki Fatun Laila ta kamo hannunta suka nufi sauka daga benen tana yi tana d'an waiwayen shi yana tsaye bai koma ba fuskar shi da d'an murmushi har suka sauka sannan ya koma ciki.
Bayan sun shiga d'akin Toilet Fatuu ta wuce tayo Alwalar sallar isha, bayan ta gama hira suka dasa wadda yawanci duk akan Walimar gobe ce saida suka kai tsakar dare sannan Fatuu ta tashi don tafiya Fauzy tace ta kwana anan kawae mana tace ai gadon bazai ishe su ba tunda akwae wuri can bari taje kawae suka yi sallama dasu Haulat Fauzy ta rakota har waje kafin suka yi sallama ta koma. Washe gari Juma'a ana tashi aka fara shirye shiryen Walima ba kama hannun yaro masu aikin girki tuni sun fara dama tun jiya aka fara aikin nama banda shanun da Baffan Fatuu ya bada harda raguna da kaji aka yayyanka, Misalin k'arfe sha d'aya lokacin duk an gama breakfast Laila tasa Fatuu taje tayi wanka, da kanta taje d'akin Hajiya da yake nan aka kai akwatunan lefenta ta d'aukko mata kayan da zata saka wanda babbar Super ce ta had'u ba k'arya anyi mata straight skirt da riga half gown tare da sark'a da yankunan gold harda yan hannu da su jaka da takalmi da mayafi mahad'in kayan, bayan ta saka kayan Laila ta yi mata yar light make up kafin anjima wadda zata yi mata Bridal makeup d'in ta zo, da kanta ta d'aura mata kallabi abun sai dae ace Tubarkallah, nan fa aka hau yi mata hotuna bayan sun gama Laila ta kamata ta nufi d'akin Mom d'in su da ita, a parlor suka isketa da wasu mutane cikin yan uwan su da suka zo bikin Mom d'in na ganinta ta hau yi mata murmushi tace a kawota gefenta, bayan ta zauna ta gaishe da ita da sauran mutanen ana ta fad'in Ma sha Allah Amarya, mik'ewa Mom tayi ta kamo hannun Fatuu itama ta mik'e suka shiga cikin Bedroom harda Laila, wurin Hajiya Zainab ta kai ta, itama da murmushi ta tarbeta Mom ta sata ta zauna a bakin gado itama ta zauna a d'ayan gefen, gaida Hajiya Zainab d'in tayi da fara'a ta amsa ta yaba gayun nata tare da Addu'ar fatan Alkhairi Laila na amsawa daga baya ta kama hannun Fatun tace suje wurin Hajiya ta mik'e suka nufi hanyar fita idanun su Mom akan su, bayan sun fita Hajiya Zainab tace yarinyar nada kyau Mom dake murmushi tace sosae, part d'in Hajiya suka wuce bayan sun fito, duk suna zaune a parlor suna ta hira harda gwaggo suka shigo Laila tayi sallama duk suka maido idon su kan su suna amsa sallamar, gaishe da Mutanen parlon tay duk suka amsa, gefen Hajiya ta kai Fatun ta zaunar da ita tana murmushi tace "ga kishiyar ki na kawo kiga adon ta" d'an murmushi Hajiya tay ta ta6e baki tana kallon Fatuu da itama kallon ta take tana murmushi sai cewa tay ina ta wani yi kyau haka kamar an bad'a mata k'asa a fuskar, gaba d'aya yan d'akin sukai dariya suna fad'in duk kyaun nan da tayi wannan dai kishi ne ba wani abu ba Gwaggo dae sai murmushi take farinciki fal ranta ganin yadda Autarta ta fito sai kace d'iyar manyan mutane, gaishe da Hajiyar tayi bayan ta amsa ta juya kan sauran mutane ta gaishe da su da fara'a duk suka amsa suka hau yin Addu'oi Laila dasu Hajiya na amsawa daga baya suka bar part d'in, baya suka wuce inda su Haulat suke, lokacin da suka shiga cikin parlon su Yadikko dasu Yaya duk suna zaune suna yin kallo, wurin su Laila ta nufa duk suka maido idon su kanta suna washe baki, zama tayi akan kujera Fatuu ma ta zauna a gefen ta suka hau gaishe da ita, da fara'a ta amsa Yadikko ce tace "wannan kaman Amarya" sai lokacin Laila ta gane ashe basu gane Fatun ba tana yar dariya tace itace ta kawo masu suga gayun ta gaba d'aya suka k'ara washe baki suna fad'in ai su basu ganeta ba Fatuu dai sai murmushi take ta gaida su,Yadikko ce ta daddage ta rangad'a gwad'a sai ga su Mino sun fito da gudu ta nufo ta ai koda taga Fatuu da gudu ta koma cikin d'akin tana fad'in azo aga Adda Fatuu Amarya tayi kaman sarauniya, nan duk suka firfito harda su Aunty Mareeya Fanan ma na a d'akin su tafi zama a wurin su duk da a d'akin Laila ta sauka, nan fa aka shiga yabon gayun aka hau yin hotuna da ita Fanan tace ai yakamata a kawo photographer Saboda ayi hard copy na tarihi Laila tace zai zo sai anjima sunyi Magana yace na iPhone d'in ma lafiya lou zai wanke su tace Ok, bayan sun gama hotunan Laila ta k'ara kamo hannunta ta fito da ita, part d'in Haisam ta wuce da ita suka shiga ta baya, knocking k'opar tayi aka bata izinin shigowa ta tura, su biyar ne a zaune, Haisam, Sameer, Salim, Abbas sai wani abokin su d'an nan Abujar Na'eem, da murmushi Laila ta nufi cikin parlon idanun su gaba d'aya akanta banda Sameer da yake sanye da headphones da alama ma bai san ta shigo ba, tunda suka shigo idon Haisam na akan Fatuu suna ta sakar ma juna murmushi, gaishe su Laila tayi tace ga Amaryar su nan ta kawo masu su ga gayunta na farko duk suka maido idon su akan Fatuu, kunya ce ta kamata da sauri ta sunnar da kanta k'asa ta gaishe dasu Abbas ya shiga tsokanar ta, mik'ewa Haisam yay jikin shi sanye da k'ananun kaya basu dad'e da gama yin Breakfast ba, inda suke tsaye ya nufo yana zuwa ya kai hannu ya kamo Fatun kawai sai ya rungumeta gaba d'aya Abbas da Na'eem suka sa sowa shi dai Saleem murmushi yake, abunda su Abbas ke yi ne ya jawo hankalin Sameer ya d'ago ya kalle su Abbas ya fara masu Video, gaba d'aya wata irin kunya ce ta kama Fatuu ji take kaman ta nutse k'asa, kokarin d'ago da kanta ya fara yi ta kafe kan tak'i yarda ya d'ago ta, d'ukar da kan shi yay can k'asan mak'oshi ya furta tayi kyau sosae murya can k'asa tace don Allah kunya take ji ya fita da ita ya furta Ok, d'agota yay tak'i yarda ta kalli side d'in da su Abbas suke yace ma Laila suje yana ruk'e da Fatun yayi mata side hug suka nufi hanyar fita ta cikin parlon Sameer dake kallon su ya d'an ta6e baki da yanayin d'an murmushi akan fuskar shi, suna fitowa wayar Laila ta fara yin ringing tace masu tana zuwa pls ta d'an yi gaba tana amsa wayar, maido Fatun yay jikinshi ya rungumeta ta yadda suna kallon fuskar juna sai yamutsa mashi fuska take tana fad'in ita kunya take ji don Allah, yana murmushi idanun shi a d'an lumshe yace to mi yay mata da zai zama abun kunya da ido tay mashi nuni da rungume tan da yayi, ce mata yay wannan ba wani abu bane yake ma yan'uwan shi ma balle ita matar shi, sai faman tura mashi baki da ya sha jambaki take gaba d'aya hakan da take ya fara turning d'in shi on, kallon ta kawae yake tana mashi shagwabar kar wani ya gan su don Allah, slowly ya duk'ar da kan shi saitin nata ya kai bakin shi kunnanta ya rad'a mata magana, d'agowa yay ya d'age mata gira tace "Yaushe?" a hankali ya furta "after isha" shiru ta d'an yi kaman mai nazarin wani abu taji yace ko bata so da sauri ta girgiza mashi kai, Laila ce ta dawo wurin su tana murmushi da sauri Fatuu ta juyar da fuskar ta, ce ma Haisam d'in tayi ko ta barta a nan ne ba tare daya ce komai ba ya saki Fatun Laila ta kamo hannunta suka nufi sauka daga benen tana yi tana d'an waiwayen shi yana tsaye bai koma ba fuskar shi da d'an murmushi har suka sauka sannan ya koma ciki.