Sashe 55
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Wurin k'arfe sha biyu su Hajiya Zainab sun gama shirin tafiya, zasu biya Asibiti su gaishe da Fatuu daga can zasu wuce, bayan ta fito tare da Mom da su Aunty da wasu mutane Security detail d'inta na biye da ita, Jidderh na a part d'in da su Fauzy suke suna zaune a parlor harda su Aunty Mareeya suna firar Dinner d'in jiya da kuma tashin hankalin da suka shiga lokacin da suka ji Fatuu ta fad'i, Yasmeen ce ta shigo da gudu ta nufe su tana d'an haki idon ta akan Jidderh tace mata ga Momy d'in Nasarawa can zasu tafi, zumbur Jidderh ta Mik'e ta ce ma su Fauzy suzo suje duk suka mik'e harda su Aunty Mareeya tana fad'in bari suma suyi mata bankwana don mace ce mai mutunci wllh, suna akan hanyar zuwa Aunty Mareeya ke ce ma Feenah in ka ga Sameer sai kace ba itace ta haife shi ba ta 6angaren hali Feenah na murmushi tace shima k'ilan in aka zauna dashi aga Mutuncin shi Aunty Mareeya tace amman dai da gani ba sai an fad'a ba yana da girman kai ba kamar Mahaifiyar tashi ba, gaba d'aya an fito waje bakin Entry Hall inda Motocin su suke a fake, tun bayan da Fauzy ta fito take ta wurga ido wai ko zata ga Sameer amman bata gan shi ba sai dai K'annan shi, tunanin ko yana a cikin Mota tay tabi Motocin da kallo saidai bazata iya ganewa ko yana ciki ba, Sallama Her Excellency tay da kowa ta nufi Mota da sauri aka bud'e mata bayan duk sun shishshiga ta d'aga ma mutane hannu kafin aka rufe kopar, a jere Motocin suka tashi ana ta d'aga masu hannu suka tafi jiniya na tashi, juyawa sukai suka koma cikin gidan, hakanan Fauzy take jin ta wani iri sai ganin fuskar Sameer take, a ranta ta raya k'ilan Shikenan bazata k'ara ganin shi ba har saida taji jikinta yayi sanyi yin tunanin, can kuma wata zuciyar ta raya mata k'ilan kuma sai ko bikin Mino da Nameer in Allah ya k'addara zasu auri juna, sukuku da ita ta koma part d'in su, koda ta shiga d'akin su ta nufa ba kowa a ciki ta nufi gado ta kwanta ta shiga tunano abubuwan da suka faru a tsakanin su wani lokacin tay murmushi wani lokacin kuma ta yamutsa fuska can zuciyarta ta raya mata wai ko dai son shi take shiyasa take ta tunanin shi haka da sauri ta hau girgiza kai saima ta yunkura ta mik'e ta nufi Parlor.
Wuraren sallar Azahar aka fara zaryar zuwa Asibiti ganin Fatuu, Yadikko tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a k'asa ta sha, har su Baffan Fatun da Ard'o sai da suka zo gaba d'aya Asibitin saida aka shaida an kwantar da dangin masu Mota don Motoci ne iri iri ke ta sintiri cikin Asibitin, da la'asar Mom da Hajiya da Aunty da gwaggo suka zo, bayan sun shiga d'akin sun duba Fatun Hajiya tace ma Aunty ta duba ta in dai ba wata matsala gwara a sallameta su koma gida don anata faman zaryar zuwa in suka koma sai taci gaba da yin bed rest d'in a gida tace to, tambayoyi tayi ma Fatun daga baya ta fita ta nufi Office d'in Doctor, bayan sun gaisa tay mashi bayanin suna so ai discharging Fatuu tunda ba wata matsala a tattare da ita, bai da yadda zai yi dole yayi masu yadda suke so don ya gane Auntyn likita ce. Bayan sallar Magrib aka sallame ta suka dawo gida, d'akin Mom aka kaita nan fa akai ta zuwa gaishe ta ita dai sai faman murmushi take bayan an tsagaita da shigowa Mom ta tambayeta abunda take son ci tana murmushi tace mata komai aka bata zata ci itama da murmushi akan fuskar ta tace in akwae wani abu da take jin tana so ta fad'i tace mata ba komae, mik'ewa tay ta fita bada jimawa ba sai gata ta dawo ruk'e da plate mai d'an girma Fruit ne aka yayyanko wanda suke da amfani ga mai ciki ta kai mata tace ta fara shan su tay mata godiya, ganin tana k'ok'arin saukkowa daga saman gadon yasa ta tambayi zatai wani abu ne tace eh hannu zata wanko cike da kulawa tace Ok amman tabi a hankali tace to, tsaye tay har saida ta shiga ta wanko hannun ta fito bayan ta koma ta zauna sannan ta tafi, bada jimawa sosae ba sai gata ta k'ara dawowa hannunta ruk'e da babban tray, a saman Carpet ta aje tace ma Fatun ta zo ta zauna nan yadda zata ji dad'i sai ta ci tace to, bayan ta zauna da kanta ta bud'e mata plates d'in da aka rufo da wasu, d'aya tuwon semovita ne mulmule ukku sai miyar Alaiyahu data ji yan ciki a cikin bowl sai d'ayan plate d'in mai d'an zurfi farfesun kaza ne sai zabga uban k'amshi yake a ido kawai sai ya burge mutum daga gefe lemu da ruwa ne harda cup, tana murmushi tace mata ta ci ta k'oshi ta d'aga mata kai ta juya ta nufi hanyar fita daga d'akin,
tun bata saki jiki ba har dai ta saki ta shiga kwasar Abincin wasa wasa sai gashi ta cinye mulmule biyu sannan ta koma kan farfesun, Ita kanta har mamakin kanta take yanzu lokacin da ba'a san da cikin ba kwata kwata bata cin Abinci sosae yadda ta saba take ci amman yanzu sosae cin Abincin ya k'aru, shima farfesun sosae ta ci shi don ba K'aramin dad'i yayi mata ba amman ta rage, bayan ta gama ta rufe komai ta d'auki tray d'in don ta fitar, a daidai bakin k'opa suka had'e da Haisam da dawowar shi kenan daga Masallaci, hannu ya kai ya amshi tray d'in yace mata wa yasa ta d'aukko ta langa6ar mashi da kai, ruk'e tray d'in yayi da hannu guda yasa d'ayan ya bubbud'e ganin bata cinye ba yasa shi kallon ta tana ganin haka ta tura mashi baki a shagwabe tace wllh ta k'oshi sosae ta ci, d'an d'aure fuska yay yace su koma ta ida cinyewa ta yamutsa fuska kamar zatai kuka tana fad'in Allah cikinta fashewa zai yi, suna Haka Mom ta sawo kai cikin d'akin har saida Fatuu ta ji kunya da sauri ta juyar da kai, tsayawa tay gefe da murmushi ta tambayi ya akai yace mata bata cinye ba, kallon Fatuu tay tace "Daughter ya akai baki cinye ba?" Juyowa tay a kunyace tace mata Allah ta k'oshi taci sosae, hannu Mom ta mik'a ta amshi tray d'in ta duba, jinjina kai tay tace ba laifi ta ci sosae ta juya ta fita da shi, had'a ido sukai tayi mashi wani kallo ya kai hannu ya jawo ta jikinshi ta saka dariya, ganin abun na neman yin yawa ta fara k'ok'arin k'wacewa tana fad'in kada Mom ta shigo don Allah, kawai sai gani tay ya d'auketa gaba d'aya ya nufi gado da ita gaban ta sai fad'uwa yake, a saman gadon ya d'aurata shi kuma ya zauna a baki yana murmushi yace hira yazo taya ta.
Wuraren sallar Azahar aka fara zaryar zuwa Asibiti ganin Fatuu, Yadikko tsabar farin ciki kamar ta zuba ruwa a k'asa ta sha, har su Baffan Fatun da Ard'o sai da suka zo gaba d'aya Asibitin saida aka shaida an kwantar da dangin masu Mota don Motoci ne iri iri ke ta sintiri cikin Asibitin, da la'asar Mom da Hajiya da Aunty da gwaggo suka zo, bayan sun shiga d'akin sun duba Fatun Hajiya tace ma Aunty ta duba ta in dai ba wata matsala gwara a sallameta su koma gida don anata faman zaryar zuwa in suka koma sai taci gaba da yin bed rest d'in a gida tace to, tambayoyi tayi ma Fatun daga baya ta fita ta nufi Office d'in Doctor, bayan sun gaisa tay mashi bayanin suna so ai discharging Fatuu tunda ba wata matsala a tattare da ita, bai da yadda zai yi dole yayi masu yadda suke so don ya gane Auntyn likita ce. Bayan sallar Magrib aka sallame ta suka dawo gida, d'akin Mom aka kaita nan fa akai ta zuwa gaishe ta ita dai sai faman murmushi take bayan an tsagaita da shigowa Mom ta tambayeta abunda take son ci tana murmushi tace mata komai aka bata zata ci itama da murmushi akan fuskar ta tace in akwae wani abu da take jin tana so ta fad'i tace mata ba komae, mik'ewa tay ta fita bada jimawa ba sai gata ta dawo ruk'e da plate mai d'an girma Fruit ne aka yayyanko wanda suke da amfani ga mai ciki ta kai mata tace ta fara shan su tay mata godiya, ganin tana k'ok'arin saukkowa daga saman gadon yasa ta tambayi zatai wani abu ne tace eh hannu zata wanko cike da kulawa tace Ok amman tabi a hankali tace to, tsaye tay har saida ta shiga ta wanko hannun ta fito bayan ta koma ta zauna sannan ta tafi, bada jimawa sosae ba sai gata ta k'ara dawowa hannunta ruk'e da babban tray, a saman Carpet ta aje tace ma Fatun ta zo ta zauna nan yadda zata ji dad'i sai ta ci tace to, bayan ta zauna da kanta ta bud'e mata plates d'in da aka rufo da wasu, d'aya tuwon semovita ne mulmule ukku sai miyar Alaiyahu data ji yan ciki a cikin bowl sai d'ayan plate d'in mai d'an zurfi farfesun kaza ne sai zabga uban k'amshi yake a ido kawai sai ya burge mutum daga gefe lemu da ruwa ne harda cup, tana murmushi tace mata ta ci ta k'oshi ta d'aga mata kai ta juya ta nufi hanyar fita daga d'akin,
tun bata saki jiki ba har dai ta saki ta shiga kwasar Abincin wasa wasa sai gashi ta cinye mulmule biyu sannan ta koma kan farfesun, Ita kanta har mamakin kanta take yanzu lokacin da ba'a san da cikin ba kwata kwata bata cin Abinci sosae yadda ta saba take ci amman yanzu sosae cin Abincin ya k'aru, shima farfesun sosae ta ci shi don ba K'aramin dad'i yayi mata ba amman ta rage, bayan ta gama ta rufe komai ta d'auki tray d'in don ta fitar, a daidai bakin k'opa suka had'e da Haisam da dawowar shi kenan daga Masallaci, hannu ya kai ya amshi tray d'in yace mata wa yasa ta d'aukko ta langa6ar mashi da kai, ruk'e tray d'in yayi da hannu guda yasa d'ayan ya bubbud'e ganin bata cinye ba yasa shi kallon ta tana ganin haka ta tura mashi baki a shagwabe tace wllh ta k'oshi sosae ta ci, d'an d'aure fuska yay yace su koma ta ida cinyewa ta yamutsa fuska kamar zatai kuka tana fad'in Allah cikinta fashewa zai yi, suna Haka Mom ta sawo kai cikin d'akin har saida Fatuu ta ji kunya da sauri ta juyar da kai, tsayawa tay gefe da murmushi ta tambayi ya akai yace mata bata cinye ba, kallon Fatuu tay tace "Daughter ya akai baki cinye ba?" Juyowa tay a kunyace tace mata Allah ta k'oshi taci sosae, hannu Mom ta mik'a ta amshi tray d'in ta duba, jinjina kai tay tace ba laifi ta ci sosae ta juya ta fita da shi, had'a ido sukai tayi mashi wani kallo ya kai hannu ya jawo ta jikinshi ta saka dariya, ganin abun na neman yin yawa ta fara k'ok'arin k'wacewa tana fad'in kada Mom ta shigo don Allah, kawai sai gani tay ya d'auketa gaba d'aya ya nufi gado da ita gaban ta sai fad'uwa yake, a saman gadon ya d'aurata shi kuma ya zauna a baki yana murmushi yace hira yazo taya ta.