Sashe 47
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Hannu Haisam ya bud'e ya rungume su aikuwa gaba d'aya aka hau tafi da sowa wasu suka fara yi masu Vedio daga inda suke, d'agowa yay ya kai hannu cikin aljihun shi ya fiddo farin hanky, d'ago da fuskar Fanan yay ya shiga share mata hawayen fuskarta itama tasa gefen gyalenta tana goge ma Fatuu, bayan sun gama goge gogen hawayen a tare suka kama hannun Fatuu ta yadda suka saka ta a tsakiya suka nufi komawa saman nan Mc ya shiga kwarzan ta su yana fad'in "What an emotional occurrence, What a beautiful Family...." Bayan sun koma saman a tare suka zaunar da ita ta sadda kanta k'asa tana ta sheshsheka, Mc ne ya sanar za'a jira Amarya tayi shiru sai aci gaba duk akai murmushi, after some few minutes yace ma Haisam saura shi suna so ya bayyana farincikin da yake ciki, tun kafin ya rufe baki ya girgiza mashi kai alamar bazai ce komai ba Mc hada kwa6e fuska ya juyo yace to anyi ma Ango laifi an sa Amaryar shi kuka don haka bazai yi magana ba aikuwa su Laila suka mik'e suna basu yarda ba yadda itama tayi shima sai ya yi nan fa wasu ma suka sa baki harda su Aunty abun sosae ya bada nishad'i, ganin an fi k'arfin shi yasa shi yi ma Mc d'in alamar ya kai mashi lasifikan, da sauri ya nufi saman ya mik'a mashi, yana amsa abunda yace shine yana matuk'ar son matanshi kuma zai yi matuk'ar kokarin ganin ya zama mai Adalci a gare su, yana fad'in hakan ya mik'a ma Mc mike d'in gaba d'aya aka hau tafi da sowa harda Sameer sarkin kamewa saida ya d'an yi guntun murmushi, mik'ewa Laila tayi ta nufi bayan hall d'in, cikin wani d'aki ta shiga inda ma'aikatan da zasu serving mutane Abinci suke gaba d'aya jikinsu sanye da farar t-shirt mai d'auke da tambarin wurin da suke aiki na k'awar Mom, umarnin fara kai Abinci ta basu dama abunda suke jira kenan ba 6ata lokaci suka fara zuzzubawa suna d'aurawa a saman manyan trays, a wuri na musamman aka zuba ma su Her Excellency da sauran manyan matan, ko ban fad'a ba ansan abinciccika ne na musamman nan suka shiga kai ma mutane duk abunda mutum yake so zai d'auka in ma fin plate d'aya ne mutum ke so na wani Abincin zai iya dauka, masu raba lemuna ma suka shiga kawo ma mutane shima ko nawa mutum ke so zai d'auka, samun wuri Mc yay yana fad'in bari yay refilling cikin shi ya k'ara samun karsashi duk aka sa dariya don cike da barkwanci yayi Maganar, a nutse kowa ke cin Abincin kuma ba wanda ya damu da yadda wani ke cin nashi har lokacin Fanan na saman tare suke cin Abincin harda ba Fatuu a baki tana murmushi ta bud'e mata bakin daga baya itama ta bata, Mc na gamawa ya mik'e yana fad'in to basu da lokacin 6atawa bari aci gaba da abunda ya tara su duk aka sa dariya ana fad'in sai da ya gama yasan basu da lokacin 6atawa, abu na gaba Ango da Amarya aka buk'aci su sauko su taka Haisam nuna wa yay bazai je ba Fanan ta nuna mashi kar yayi hakan baza'a ji dad'i ba, tare suka mik'e ya kama hannun Fatuu ita tayi gaba suka biyo bayanta, tana saukkowa ta koma cikin hall din Mc ya nuna masu inda zasu tsaya, suna zuwa wurin kawai aka fara sakin fireworks da dry ice smoke, Ya Allah har tsuma nike Saboda kayatuwar yadda ake sakin hayakin da kuma tartsatsin wutar kowa ka gani murmushi ne akan fuskar shi wasu kuma washe baki sukai, ita Fatuu ma d'an tsoron abun ne ya kamata yadda hayakin ya turnuk'e su da kuma yadda tartsatsin ke fita da k'arfi,
"Dama nasan da wuya H,Zee bai auri yarinyar can ba, tun da naga yak'i amince man in nemeta dama I ave suspected something ever since" Najeeb ne da yake zaune gefen Abbas yayi Maganar, yar dariya Abbas yayi yace mashi wllh ba wani abu a ranshi a lokacin daya wuce taimaka mata kawai Allah ne ya k'addaro zasu zama ma'aurata yace baya fad'i mashi yadda komai ya faru ba, hararar Abbas d'in yayi fuska d'aure yace "ai kaima ba sona kake da ita ba in ba haka ba why not ni ka kirani kai man Maganar Aurenta kaga in ban aureta ba" Sosae Abbas yake dariya bai dai ce komai ba acikin ran shi ya raya ai duk k'anwar ja ce, Salim dai d'an murmushi kawae yayi, kamata Haisam yay har hayakin ya washe, wak'ar Fall in love aka kunna masu yana rik'e da ita sai murmushi yake mata itama d'an murmushin take duk kunya ta lullube ta, a hankali yake d'an motsawa da ita har lokacin tartsatsin wutar na tashi a bangaren daman su da hagun su abun gwanin k'ayatarwa, masu hoto da Video nata yi harda wanda aka daukko, bayan d'an lokaci kafin wak'ar ta k'are Laila ta nufi wurin Dj ta fad'i mashi ya canza masu Wak'a tace yasa wak'ar breaker ta burina, a hankali taken wak'ar ya fara da kid'a mai sanyin dad'i kafin baitin wak'ar ya fara fita,
_Dubaaa kan ki ana kallonaa....babban buri na ki kasance dab dani, in zaakii k'irga masoya naki ki sanyo danii, dubaaa kan ki ana kallonaa majnunii ni kuma nace in dai kai na ki ne baan fad'i ba, sak'o ya bayyana ni tun daga zuciya, sannan k'aunar ki tana kaman zuciya......_
"Dama nasan da wuya H,Zee bai auri yarinyar can ba, tun da naga yak'i amince man in nemeta dama I ave suspected something ever since" Najeeb ne da yake zaune gefen Abbas yayi Maganar, yar dariya Abbas yayi yace mashi wllh ba wani abu a ranshi a lokacin daya wuce taimaka mata kawai Allah ne ya k'addaro zasu zama ma'aurata yace baya fad'i mashi yadda komai ya faru ba, hararar Abbas d'in yayi fuska d'aure yace "ai kaima ba sona kake da ita ba in ba haka ba why not ni ka kirani kai man Maganar Aurenta kaga in ban aureta ba" Sosae Abbas yake dariya bai dai ce komai ba acikin ran shi ya raya ai duk k'anwar ja ce, Salim dai d'an murmushi kawae yayi, kamata Haisam yay har hayakin ya washe, wak'ar Fall in love aka kunna masu yana rik'e da ita sai murmushi yake mata itama d'an murmushin take duk kunya ta lullube ta, a hankali yake d'an motsawa da ita har lokacin tartsatsin wutar na tashi a bangaren daman su da hagun su abun gwanin k'ayatarwa, masu hoto da Video nata yi harda wanda aka daukko, bayan d'an lokaci kafin wak'ar ta k'are Laila ta nufi wurin Dj ta fad'i mashi ya canza masu Wak'a tace yasa wak'ar breaker ta burina, a hankali taken wak'ar ya fara da kid'a mai sanyin dad'i kafin baitin wak'ar ya fara fita,
_Dubaaa kan ki ana kallonaa....babban buri na ki kasance dab dani, in zaakii k'irga masoya naki ki sanyo danii, dubaaa kan ki ana kallonaa majnunii ni kuma nace in dai kai na ki ne baan fad'i ba, sak'o ya bayyana ni tun daga zuciya, sannan k'aunar ki tana kaman zuciya......_