Sashe 37
Asanadin Makwabtaka Part 3 Complete Hausa Novel · about 5 min read
"Yana nan yanzu a koma Yola acan yake aiki tare ma akayi bikin mu don bayan an fasa naku yayi nadama sosae, don har gwuiwa k'asa ya rok'i Dad kan ya bashi dama ta k'arshe kada a fasa Auren anan yake sanar mashi ai an ma d'aura maki Aure don haka ya hak'ura dake ba matar shi bace, aikuwa anan ya sume mashi abun ya kai shi ga kwanciya har gadon Asibiti, sosae yayi nadama wllh don akwae lokacin da muka zauna dashi yana k'walla yake fad'i man Allah ya jarabe shi da son ki sosae dama tunda ya gan ki matsayin wadda zai Aura yaji kin mashi gajan hak'uri yaja mashi amman yasan Allah ne ya kama shi, lokacin da aka zo neman Aure na shine Dad yayi mashi Maganar ya fito da wadda yake so tunda yasan bai rasa yan mata sai a had'a shine yace ma Dad d'in ya bar mashi komai ya nemo mashi kowacece zai Aura, farko Dad cewa yay ya fidda hannun shi akan shi saida Mom tay ta rok'on shi tana nuna mashi da gaske ya canza ba zai bashi kunya ba anan har take mashi Maganar wata k'anwar ki wai da akayi magana da suka je Dad d'in yace ai kuma shi ba K'aramin mutum bane ya riga yace a kyaleta tayi karatun ta yanzu bazai Koma ba yace a bashi ko ba don haka ba ma don abunda Ya Khalid d'in yay maki bazai nema mashi k'anwar ki ba, k'arshe dai wata d'iyar Abokin shi ya samo mashi Hafsat itama Secondary ta gama ba laifi tana da kyau itama bafullatana ce a cikin Yola suke shine akayi bikin mu tare, Yanzu suna acan Yola d'in yasa taci gaba da karatu tana nan ma da tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe, gaba d'aya Ya Khalid ya canza ta sanadiyyar abunda ya faru, sosae yay sanyi duk wani hali mara kyau da kika sani ya bari wllh don ni bai 6oye man komai tun lokacin da yana cikin ciwon son ki ya maida ni kamar k'awar shi yay ta fad'i man damuwar shi in ta lallashin shi ina k'arfafa mashi gwuiwa yanzu haka shima yasan da zamu zo nan" idanun ta cike da k'walla ta k'arasa Maganar itama Fatuu sosae jikinta yayi sanyi zuciyar ta sai tunano mata abubuwan da suka faru tsakanin su take, Allah mai juya Al'amari a yadda yaso a kuma lokacin daya so da rabon ta silar hakan zata auri Haisam yanzu data k'i yarda kota yanke ta gudu da tayi ma kan ta, k'arshe rayuwarta ta wulakance ta kuma jefa iyayen ta a matsala, shiyasa ake son bawa ya rink'a yarda da k'addara mai kyau da mara kyau, duk abunda Allah yayi ma bawan shi mai kyau ne don yafi mu son kan mu, sau da yawa abubuwa marasa dad'i da suke faruwa damu wasu kan haifar da abubuwa masu dad'i agare mu matuk'ar zamu dogara da Allah muyi rik'o da yin Hak'uri, suna zaunen Laila ta zo tace mata Dad d'in su na nemanta tace to ta nuna mata Sadeeya tace bak'uwarta ce yar uwarsu ce a Adamawa tana aure anan, a mutunce suka gaisa harda tambayar ta Unguwar da take anan Abuja ta d'auki Baby d'inta, daga baya ta kira Jidderh ta had'a su tace a kaita d'akinta a bata Abinci kafin su dawo, part d'in Dad d'in suka wuce gaba d'aya parlon shi cike yake da Manyan Mutane masu tumbin Naira kama daga shahararrun masu kud'i zuwa masu Mulki, Laila ta shiga bin su da ita suna gaishe su suma dae har da kyautar kud'in suka mata daga baya Dad yace akawo ta wurin Alhaji Lawal dake a kusa dashi, a k'asa ta tsugunna ya kai hannu ya dafa Shoulder dinta da fara'a yace "Ma sha Allah Daughter, nayi matuk'ar farincikin yadda abu ya kasance, wannan aikin Albarkar da muke sa maki ne, matuk'ar zaka yi biyayya ga iyayen ka to kuwa rayuwar ka zata yi Albarka, Allah yasa Alkhairi ya baku zaman lafiya da zuria dayyiba yasa gidan zaman ki ne na har abada" Mutanen dake a kusa dashi sai amsawa da Amin suke harda wani abokin shi d'an Majalisa da suka zo tare, kasa jurewa Fatuu tay ta shiga yin hawaye komai daya faru a baya yana dawo mata, Envelope ya fiddo daga cikin Aljihun shi ya mik'a mata kawae sai ta fashe da kuka ya hau rarrashinta yana fad'in ai ba abun kuka bane, Senator dake ta murmushi yace "Kukan dad'i ne kasan shima yana sa ayi kuka" ya kalli Fatuu yace "Hakane ko Daughter?" A hankali ta d'aga mashi kai duk aka yi dariya daga baya Dad d'in yace ma Laila taje da ita.
Bayan sallar la'asar Nameer ya d'auki Mino suka fita Tk ma ya d'auki su Kawu Amadu da Kamalu suka shiga gari, Lokacin Laila tasa Fatuu ta canza shiga zuwa rantsatstsiyar shadda gray data sha ubansun aiki harda alkyabba aka d'aura mata lokacin Malamar da aka d'aukko zata yi Wa'azi wadda sananna ce ta zo, tuni an gyara main parlor d'in tsaf anan aka zazzauna Malamar itama a kan kujera ta zauna ta fara Wa'azin hannunta ruk'e da lasifika da ta karad'e ko ina, Wa'azi mai tsuma zuciya kan rayuwar Aure tayi, sai gab da sallar Magrib aka gama nan aka shiga rabon souvenirs abubuwa kala kala masu d'auke da sunan Haisam Ali Adamu Zakee da Fatima Muhammad Ardo, ba masu hotunansu cikin abubuwan da aka raba don Haisam d'in ya nuna bai so. Alhamdulillah Walima ta tashi lafiya abun dai sai san barka wllh, mun ci mun sha munyi hani'an yan Comment section an sha da ku da baku yi anko ba kun zo, kar ku manta gobe in Allah ya kai mu akwae Dinner itama kuma in ba anko ba shiga zaku yi ba ato😹.
Bayan sallar la'asar Nameer ya d'auki Mino suka fita Tk ma ya d'auki su Kawu Amadu da Kamalu suka shiga gari, Lokacin Laila tasa Fatuu ta canza shiga zuwa rantsatstsiyar shadda gray data sha ubansun aiki harda alkyabba aka d'aura mata lokacin Malamar da aka d'aukko zata yi Wa'azi wadda sananna ce ta zo, tuni an gyara main parlor d'in tsaf anan aka zazzauna Malamar itama a kan kujera ta zauna ta fara Wa'azin hannunta ruk'e da lasifika da ta karad'e ko ina, Wa'azi mai tsuma zuciya kan rayuwar Aure tayi, sai gab da sallar Magrib aka gama nan aka shiga rabon souvenirs abubuwa kala kala masu d'auke da sunan Haisam Ali Adamu Zakee da Fatima Muhammad Ardo, ba masu hotunansu cikin abubuwan da aka raba don Haisam d'in ya nuna bai so. Alhamdulillah Walima ta tashi lafiya abun dai sai san barka wllh, mun ci mun sha munyi hani'an yan Comment section an sha da ku da baku yi anko ba kun zo, kar ku manta gobe in Allah ya kai mu akwae Dinner itama kuma in ba anko ba shiga zaku yi ba ato😹.